Aminiya:
2025-11-21@16:31:46 GMT

’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara

Published: 13th, April 2025 GMT

’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje fiya da 10 a yankin Biyabiki da ke Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara.

’Yan ta’addan sun cinna kona wuraren ne bayan sallar Isha’i a ranar Asabar a wani da ake zargin na ramuwar gayya ne kan kashe Isuhu Yellow, kanin wani jagoran ’yan bindiga mai suna Adamu Aliero.

Shaida sun ce da  misalin karfe 8 na dare ne ’yan bindigar da ake zargin yaran kasurgumin dan bindiga Adamu Aliero ne suka kai harin a kan babura, inda suka banka wa wuraren wuraren wuta, sannan suka tsere ba tare da taba mazauna ba.

“Wuraren da suka cinna wa wuta sun hada da masallacin Juma’a da wani karamin asibiti da kuma gidaje kimanin 10 da suka lalata,” in ji wani mazaunin garin da ya nemi a boye sunansa.

A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa

Ana kyatuta zaton harin na da alaka da kashe Adamu Yelow a wani harin kwanton bauna da shi da tawagarsa suka kai wa jami’an tsaro, a yankin Keta, kimanin makonni uku da suka gabata, amma jami’an tsaron suka aika su lahira.

Tun da farko a ranar sai da ’yan ta’addan sun kuma kai wani hari a kauyen Tsageru a ranar, inda suka kona gidaje da dama.

Wani mazaunin yankin ya ce, “Ba mu san wace butaka suke neman cim ma da kona gidaje da kayan gwamnati da suke yi ba; Tun da aka kashe Isuhu Yellow yankunanmu ke ta fuskantar barazana, don haka muna kyatata zaton wanna harin ramuwar gayya ce.”

Wakilinmu ya yi kokarin tattaunawa da kakakin ’yan sanda na Jihar Zamfara, DSP Yazid Abubakar, domin samun karin bayani, amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba, bayan ya yi ta kiran wayar jami’in.

Wannan hari na kara nuna alamr ci gaban matsalar tsao a Jihar Zamfara inda ’yan bindiga ke kara cin karensu a yankunan karkara, duk kuwa da kokarin hukumomin tsaro na yi wa tufkar hanci a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan ta adda hari Zamfara yan bindiga Yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas

Mutum uku da wani yaron babbar motar kaya sun rasa ransu bayan wayar wutar lantarki kashe su a lokacin wani bikin nadin sarauta a unguwar Idimu da ke Ƙaramar Hukumar Alimosho ta jihar Legas,

bayanai sun nuna cewa lamarin ya faru ne ranar Talata, 11 ga watan Nuwamba, kuma an gano cewa yaron motar, wanda ba a tantance sunansa ba tukuna, ya mutu nan take a wurin.

Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka Babu addinin da ake yi wa kisan ƙare dangi a Binuwai — Gwamna Alia

Rahotanni sun ce wani mazaunin unguwar da aka karrama da sarauta ne ya shirya taron cashiyar a titin Anjorin domin murnar nadin.

Sai dai yayin da ake tsaka da bikin, wata babbar mota mai ɗaukar yashi ta yi ƙoƙarin shiga layin amma ta samu cikas saboda ɗaya daga cikin tantunan da aka kafa a kan hanya.

Wani ganau mai suna Femi Ajiboye, ya shaida wa wakilinmu a ranar Laraba cewa yayin da suke ƙoƙarin matsar da tantin gefe, ƙarfen tantin ya taɓa wayar lantarki, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar su nan take.

Femi ya ce, “Bikin nadin sarauta ya ɗauki mako guda ana yin sa, kuma a cikin wannan lokaci wani mazaunin unguwar ya sami sarauta. Yayin da yake gudanar da wani taro na musamman don murnar nadin, wata mota mai ɗaukar yashi ta yi ƙoƙarin shiga sabon rukunin gidajen da ke ƙarshen titin, amma tantin da aka kafa ya tare hanya.
“A lokacin ne wasu daga cikin mahalarta bikin tare da ɗaya daga cikin yaran motar suka ɗage tantin daga hanya.

“Ba tare da sun ankara ba, ashe akwai budaddiyar wayar lantarki a ƙasa. Da ƙarfen tantin ya taɓa wayar, sai wutar ta ja su. Mutane ba su fahimci abin da ke faruwa ba sai da suka ga sun faɗi a ƙasa. A lokacin ne aka gane cewa wutar lantarki ce ta kashe su,” in ji Femi.

Rahotanni sun ce lamarin ya jefa taron cikin alhini, inda aka dakatar da bukin nan take.

Wani mazaunin unguwar da ya bayyana sunansa da Olajide, ya ce an garzaya da waɗanda abin ya shafa zuwa asibiti, inda aka tabbatar da mutuwar yaron motar nan take.

“Dukkan yankin ya rikice lokacin da lamarin ya faru saboda mutane sun yi tunanin sun mutu gaba ɗaya. An kai su huɗun asibiti, amma yaron motar bai tsira ba. Sauran baƙi uku an karɓe su kuma suna samun kulawa a yanzu,” in ji shi.

Olajide ya ƙara da cewa iyalan mamacin sun ɗauki gawarsa daga baya suka yi masa jana’iza.

Wani mazaunin unguwar da ya nemi a ɓoye sunansa saboda dalilai na sirri ya ce ya ga mamacin kafin lamarin, lokacin da ya sayi dizal a gidan mai.

“Na ga mutumin lokacin da ya sayi dizal a tashar mai ba da jimawa ba. Na yi matuƙar mamaki da aka ce ya mutu. Wannan mutumin da na gani kimanin mintuna talatin kafin haka,” in ji shi.

Lokacin da aka tuntubi jami’an ‘yan sanda a ranar Lahadi don jin ta bakinsu, jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ’yan sandan jihar ta ce ba ta da masaniya.

Ta ce: “Na kira DPO na yankin, ta ce babu irin wannan rahoto da aka kawo ofishin ’yan sanda.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu wani addini da matsalar tsaron Nijeriya ta ƙyale — Fafaroma
  • Za a aurar da marayu 200 a Zamfara
  • Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas
  • Hamas Tayi Gargadi Game Da Kara Dagulewar Al’amura Bayan Harin Isra’ila A Gaza
  • Babu addinin da ake yi wa kisan ƙare dangi a Binuwai — Gwamna Alia
  • Isra’ila ta kashe akalla Falasdinawa 27 a wani sabon harin bam
  • Kimanin Falasdinawa 2 Ne Suka yi Shahada Sakamakon Harin Isra’ila  A  Ainul Hilwa
  • DAGA LARABA: Hanyoyin Da Suka Kamata A Bi Wajen Ceto Daliban Kebbi Da Aka Sace
  • Gwamnan Taraba ya dakatar da ficewa daga PDP saboda sace ɗalibai a Kebbi
  • Iran: An Bayyana Taron Gundumomin Dake Gabar Ruwan ” Caspian” Da Cewa Yana Bunaksa Alakar Kasashen Yankin