Aminiya:
2025-11-24@17:43:32 GMT

’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara

Published: 13th, April 2025 GMT

’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje fiya da 10 a yankin Biyabiki da ke Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara.

’Yan ta’addan sun cinna kona wuraren ne bayan sallar Isha’i a ranar Asabar a wani da ake zargin na ramuwar gayya ne kan kashe Isuhu Yellow, kanin wani jagoran ’yan bindiga mai suna Adamu Aliero.

Shaida sun ce da  misalin karfe 8 na dare ne ’yan bindigar da ake zargin yaran kasurgumin dan bindiga Adamu Aliero ne suka kai harin a kan babura, inda suka banka wa wuraren wuraren wuta, sannan suka tsere ba tare da taba mazauna ba.

“Wuraren da suka cinna wa wuta sun hada da masallacin Juma’a da wani karamin asibiti da kuma gidaje kimanin 10 da suka lalata,” in ji wani mazaunin garin da ya nemi a boye sunansa.

A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa

Ana kyatuta zaton harin na da alaka da kashe Adamu Yelow a wani harin kwanton bauna da shi da tawagarsa suka kai wa jami’an tsaro, a yankin Keta, kimanin makonni uku da suka gabata, amma jami’an tsaron suka aika su lahira.

Tun da farko a ranar sai da ’yan ta’addan sun kuma kai wani hari a kauyen Tsageru a ranar, inda suka kona gidaje da dama.

Wani mazaunin yankin ya ce, “Ba mu san wace butaka suke neman cim ma da kona gidaje da kayan gwamnati da suke yi ba; Tun da aka kashe Isuhu Yellow yankunanmu ke ta fuskantar barazana, don haka muna kyatata zaton wanna harin ramuwar gayya ce.”

Wakilinmu ya yi kokarin tattaunawa da kakakin ’yan sanda na Jihar Zamfara, DSP Yazid Abubakar, domin samun karin bayani, amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba, bayan ya yi ta kiran wayar jami’in.

Wannan hari na kara nuna alamr ci gaban matsalar tsao a Jihar Zamfara inda ’yan bindiga ke kara cin karensu a yankunan karkara, duk kuwa da kokarin hukumomin tsaro na yi wa tufkar hanci a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan ta adda hari Zamfara yan bindiga Yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana 47 da ke faɗin Najeriya.

Gwamnatin ta ɗauki wannan mataki ne bayan hare-haren da ’yan bindiga suka kai makarantu a jihohin Kebbi da Neja, inda suka sace ɗalibai da ma’aikata, suka kashe mutum ɗaya.

Atiku ya nemi a ayyana dokar ta-ɓaci kan satar ɗalibai a Najeriya Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai a Neja

A wata takarda da aka aike wa shugabannin makarantu a ranar Juma’a, Daraktar Makarantun Sakandare, Hajiya Binta Abdulkadir, ta ce Ministan Ilimi, Dokta Tunji Alausa, ya amince da rufe makarantun na wucin gadi saboda barazanar matsalolin tsaro.

Takardar ta bayyana cewa an rufe makarantun ne domin kare ɗalibai da malamai daga hare-haren ’yan bindiga, da kuma kauce wa duk wata barazana.

Makarantun da abin ya shafa sun haɗa da waɗanda ke Zariya, Daura, Sakkwato, Potiskum, Ikare-Akoko, Abaji, da sauransu.

Wannan umarni na zuwa ne a daidai lokacin da hare-haren da ake kai wa makarantu ke ƙara tsananta.

A Jihar Kebbi, ’yan bindiga sun kai hari makarantar Government Girls Comprehensive Secondary School da ke Maga, inda suka sace ɗalibai 25, tare da kashe mataimakin shugaban makarantar, Malam Hassan Makaku, yayin da yake ƙoƙarin kare su.

Rahotanni sun nuna cewa daga 2014 zuwa 2022, an sace yara sama 1,680 a makarantun Najeriya.

Gwamnati ta ce rufe makarantun na wucin gadi ne, domin kare ɗalibai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
  • Harin Isra’ila ya kashe mutum 5 a Kudancin Beirut
  • Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar
  • ’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba
  • ’Yan sanda sun daƙile harin ’yan bindiga, sun ceto mutum 25 a Zamfara
  • Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja
  • Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno
  • Ɗalibai 215 da malamai 12 aka sace a Makaranta a Neja — CAN
  • Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA
  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya