’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
Published: 13th, April 2025 GMT
’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje fiya da 10 a yankin Biyabiki da ke Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara.
’Yan ta’addan sun cinna kona wuraren ne bayan sallar Isha’i a ranar Asabar a wani da ake zargin na ramuwar gayya ne kan kashe Isuhu Yellow, kanin wani jagoran ’yan bindiga mai suna Adamu Aliero.
Shaida sun ce da misalin karfe 8 na dare ne ’yan bindigar da ake zargin yaran kasurgumin dan bindiga Adamu Aliero ne suka kai harin a kan babura, inda suka banka wa wuraren wuraren wuta, sannan suka tsere ba tare da taba mazauna ba.
“Wuraren da suka cinna wa wuta sun hada da masallacin Juma’a da wani karamin asibiti da kuma gidaje kimanin 10 da suka lalata,” in ji wani mazaunin garin da ya nemi a boye sunansa.
A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a MajalisaAna kyatuta zaton harin na da alaka da kashe Adamu Yelow a wani harin kwanton bauna da shi da tawagarsa suka kai wa jami’an tsaro, a yankin Keta, kimanin makonni uku da suka gabata, amma jami’an tsaron suka aika su lahira.
Tun da farko a ranar sai da ’yan ta’addan sun kuma kai wani hari a kauyen Tsageru a ranar, inda suka kona gidaje da dama.
Wani mazaunin yankin ya ce, “Ba mu san wace butaka suke neman cim ma da kona gidaje da kayan gwamnati da suke yi ba; Tun da aka kashe Isuhu Yellow yankunanmu ke ta fuskantar barazana, don haka muna kyatata zaton wanna harin ramuwar gayya ce.”
Wakilinmu ya yi kokarin tattaunawa da kakakin ’yan sanda na Jihar Zamfara, DSP Yazid Abubakar, domin samun karin bayani, amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba, bayan ya yi ta kiran wayar jami’in.
Wannan hari na kara nuna alamr ci gaban matsalar tsao a Jihar Zamfara inda ’yan bindiga ke kara cin karensu a yankunan karkara, duk kuwa da kokarin hukumomin tsaro na yi wa tufkar hanci a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan ta adda hari Zamfara yan bindiga Yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
GGCSS Maga: Halin da iyaye ke ciki bayan sace ’ya’yansu
Iyayen ɗalibai ’yan mata 25 ’yan bindiga sace ɗakunan kwanansu a Jihar Kebbi sun bayyana irin tashin hankali da suka shiga bayan abin da ya faru.
“Ita kaɗai gare ni,” in ji Malam Muhammad Maga, mahaifin Nafisa, wadda ita kadai ya haifa, kuma take cikin ɗaliban da ’yan bindiga suka sace a makarantar.
Malam Muhammad wanda idanunsa ke cike da ƙwalla ya ce, “Roƙona Allah Ya sa a dawo min da ita lafiya, ita kaɗai gare ni. Ina roƙon Gwamna Idris ya taimaka a dawo mana da su. Mun san ƙoƙarin da yake yi a fannin tsaro a tsawon shekara biyu da ya yi a kan mulki.”
Shi ma Malam Aliyu Yakubu, ɗaya daga cikin iyayen ɗaliban da aka sace, ya ce, “’Yata na cikin ɗaliban da aka sace daga ɗakin kwanansu a safiyar Litinin, gaskiya ni da sauran iyaye muna cikin tashin hankali.
Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi Sace Ɗalibai: Gwamnatin Tinubu ba ta shirya kawo ƙarshen ta’addancin ’yan bindiga ba — Amnesty Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan soji a Borno“Babban abin da nake tsoro shi ne kada abin ya zama irin na Makarantar ’Yan Mata ta Gwamantin Tarayya ta Birnin Yauri, inda yaran da aka sace suka shafe sama da shekara biyu a hannun ’yan bindiga
Muna rokon Gwamnatin Jihar Kebbi da Gwamnatin Tarayya su yi duk mai yiwuwa su ceto mana ’ya’yan mu”
Aminiya ta ruwaito cewar da asubahin ranar Litinin ne ’yan bindiga suka yi ta harbe-harbe a iska sa’annan suka kutsa cikin Makarantar sakandaren ’Yan Matan Gwamnati ta Musamman (GGCSS) da ke garin Maga a Ƙaramar Hukumar Danko Wasagu a Jihar Kebbi, suka yi abin gaba da ɗalibai 25.
’Yan bindigar sun ci karensu babu babbaka, ba tare da wani ƙalubale ba, in banda Mataimakin Shugaban Makarantar, Malam Hassan Yakubu Makuku, wanda ya yi ƙoƙarin hana su tafiya da ɗaliban, amma suka harba shi har lahira, suka yi abin gaba da yaran.
Makarantar GGCSS Maga ta kasance a rufe na kimanin shekaru biyar saboda tsaron irin garin GGSS Birnin Tauri a zamanin gwamnatin da ta gabata ta Abubakar Atiku Bagusu, sai ’yan shekarun baya aka buɗe ta, inda aka girke jami’an tsaro.
Wani mahaifi da ’yarsa A’isha take cikin ɗaliban da aka sace, ya ce, wani mazaunin garin ne ya fara sanar da shi cewa A’isha tana cikin yaran da aka sace, “Amma ban gaskata ba, sai da na zo makarantar na iske iyaye na ta koke-koke. Roƙona ga gwamnati shi ne ta taimaka ta ceto maka ’ya’yanmu.”
Kawai Altine, wanda shi ma ’yan bindiga sun sace ’yarsam ya ce, “Na miƙa komai ga Allah, kuma na yi imanin cewa Allah Zai dawo mana da ita nan ba da jimawa ba. Roƙona kawo shi ne gwamnati da jami’an tsaro kada su yi ƙasa a gwiwa, wajen bi sawu domin gano yaran namu.”
Wani shugaban al’umma a yankin, Malam Rabi’u Abubakar, ya ce harin ya girgiz al’ummar yankin, musamman iyayen ɗalibai.
Ya ce, “Muna da dalilin yin baƙin ciki, saboda sun tafi mana da ’ya’ya, kuma suka kashe mana Malam Yakubu Makuku, saboda ya nemi kada su ɗauki yaran. Haƙiƙa wannan babban rashi ne.”
Kakakin Gwamnan Jihar Kebbi, Abdullahi Idris Zuru, ya shaida wa Aminiya cewa an turo ƙarin jami’an tsaro daga Abuja zuwa jihar domin su taimaka a aikin da ake yi na nema da kuma ceto ɗaliban.
Tun da farko Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi ta tabbatar da harin, tare da sanar da cewa tuni jami’an tsaro da mafarauta suka fara aikin ceto ɗaliban.
Aminiya ta ruwaito cewa Gwamna Jihar Kebbi, wanda labarin harin ya sa shi gaggawar yanke ziyarar aiki da ya kai Abuja, ya yi wata ganawa da iyayen ɗaliban, inda ya ba su tabbacin yin duk mai yiwuwa tare da jami’an tsaro domin kuɓutar da yaran.
Karo na biyu ke nan da ’yan bindiga suka kutsa cikin makarantar kwana ta ’yan a Jihar Kebbi suka yi garkuwa da gomman dalibai — na farko shi ne a Makarantar ’Yan Mata ta Gwamantin Tarayya da ke Birnin Yauri.