Ministan ya ce maganar da ya faɗa da farko wadda ba a ruwaito ta a daidai ba ita ce:

“E, lallai an samu cigaba a harkar tsaro a sassa daban-daban na ƙasar nan, ko da yake ba a kawar da duk wani aikin tashin hankali gaba ɗaya ba.

“Hukumomin tsaro suna aiki ba dare ba rana don tabbatar da cewa an shawo kan matsalolin da ake da su a wasu sassan Jihar Borno da wasu wurare.

“Haɗin gwiwar da muke gani tsakanin hukumomin tsaro, musamman a shekaru biyu da suka wuce, da kuma gagarumin zuba jari a kayan aiki da na’urorin zamani da ake yi, yana nuna yadda Gwamnatin Tarayya take ɗaukar batun tsaro da matuƙar muhimmanci.

“Gwamnatin Tinubu tana da ƙwarin gwiwar kawar da ayyukan ‘yan bindiga da ta’addanci a faɗin ƙasar.

“Nasarorin da hukumomin tsaro suka samu a cikin watanni 18 da suka wuce suna nuna cewa lallai Nijeriya tana komawa daidai a hankali a hankali.

“Gwamnati tana kira ga kowa da kowa, musamman gwamnatocin jihohi, da su haɗa hannu wajen kawar da ragowar ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka a duk inda suke.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu

Ɗan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar Labour (LP) a zaben 2023, Peter Obi, ya buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya dawo gida nan take domin tunkarar matsalar rashin tsaro da ke ƙara ƙamari.

Ya bayyana hakan ne a shafinsa na X, a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar hare-haren ’yan bindiga a jihohin Filato, Zamfara, Borno da wasu sassan ƙasar.

Shugaba Tinubu ya tafi Faransa a ranar 2 ga Afrilu don “tafiyar aiki” na makonni biyu. Daniel Bwala, Mataimakin Shugaban Ƙasa na Musamman kan Yaɗa Manufofi, ya ce tafiyar na da nufin yin yin bitar tsare-tsaren gwamnatin Tinubu da kuma sauye-sauyen, gabanin cikar shekaru biyu na gwamnatin.

A cikin saƙonsa na ranar Laraba, Obi ya ce ya zama dole ya ja hankalin “shugabanmu mai janyewa, zuwa ga ƙalubalen tsaro a gida,” yana mai jaddada buƙatar “ya dakatar da kansa bayan da yake yi a ƙasar waje nan take, ya dawo gida domin magance matsalar tsaro da ta mamaye ƙasar.”

An kashe shanu 36, an ba 42 guba a Filato Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ’yan jarida su daina kawo rahoton ayyukan ’yan ta’adda

Ya bayyana cewa, wannan kira nasa na gaggawa ya zama dole saboda ƙaruwar ta’addanci da  miyagun laifuka a faɗin Najeriya, tare da rashin ganin matakan da gwamnati ke ɗauka a zahiri.

Ya bayyana wa Tinubu cewa, “A cikin makonni biyu da kuka yi a waje, sama da ’yan Najeriya 150 sun rasa rayukansu sakamakon rashin tsaro a faɗin ƙasar, musamman a jihohin Filato da Zamfara. Fashewar bututun mai da aka yi a yankin Neja Delta, ya ƙara nuna kasar cikin kunci.

“A Arewa Maso Gabas, shugabannin Jihar Borno na kuka game da dawowar ’yan ta’adda, inda ake kashe sojoji da fararen hula ba tare da dalili ba. A Kudu Maso Gabas, labarin haka yake: kashe-kashe da garkuwa da mutane.

“A cikin duk waɗannan, shugaban kamfanin da ke da cikin matsala, mai suna Najeriya, ya bar hedikwatar kamfanin ya je ya yi zamansa a ƙasar Faransa,” in ji Obi.

Ya jaddada cewa, babban aikin kowace gwamnati shi ne tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan kasarta, yana mai tambayar “dalilin zaman a wata ƙasa da shugabanninsu suka tabbatar da zaman lafiya yayin da jini ke ci gaba da zuba a tamu ƙasar.”

Obi ya ce, gwagwarmayar samun Najeriya ta gari ba batu ne na tabbatar da cewa kowane ɗan kasa ya ga, ya ji, kuma ya amfana da manufofi da shawarwarin waɗanda ke kan mulki.

“Don haka, ina kira ga shugaban ƙasa da ya dakatar da duk abin da yake yi a Faransa da sauri ya dawo gida ya ɗauki mataki ta hanyar magance waɗannan batutuwa masu tayar da hankali,” in ji Obi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yara Kimani 3,500 Ne Suka Rasa Rayukansu A Taken Medeteranin A Shekaru 10 Da Suka Gabata
  • Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu
  • An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato
  • Batawa Sin Suna Ba Zai Taimaka Kawar Da Tambarin Amurka A Matsayin Daular Kutsen Intanet Ba
  • Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ’yan jarida su daina kawo rahoton ayyukan ’yan ta’adda
  • An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato
  • Samarwa Matasa Abun Yi Shi Zai Kawo Ƙarshen Ta’addancin Boko Haram Da ‘Yan Bindiga – Zulum 
  • Gazawar Gwamnati Kan Kiyaye Rayuka Da Dukiyoyi: Gwamnan Filato Ya Nemi Yafiyar Al’ummar Jihar
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • HOTUNA: Zulum ya karɓi baƙuncin Majalisar Sarakunan Arewa a Borno