’Yan bindiga sun harbi alkali da ɗansa, sun sace mutane 13 a Katsina
Published: 11th, April 2025 GMT
’Yan bindiga sun kai hari garin Mahuta da ke Ƙaramar Hukumar Kafur a Jihar Katsina, inda suka harbi wani alkali, Rabiu Mahuta, a hannu da kuma dansa.
A lokacin harin na daren Talata, maharan sun raunata mutane uku tare da yin garkuwa da wasu mutane 13, ciki har da matar alƙalin da kuma biyar daga cikin ’ya’ansa.
Wani mazaunin garin da ya zanta ya ce ’yan bindigar sun isa wurin ne da misalin karfe 11:30 na dare, kuma kai tsaye suka nufi gidan alkalin, inda suka kwashe kusan awa guda suna ƙoƙarin karya ƙofar gidan.
Cutar Kwastomomi: NERC ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar N628m ’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin NejaDuk da kiran da alƙalin ya yi wa DPO na yankin domin neman taimako, jami’an tsaro ba su iso a kan lokaci ba.
Ya ce, “Da suka samu nasarar shiga gidan, nan take sun harbe shi a hannu, sai ya faɗi a ƙasa. An kuma raunata ɗansa da raunin harbi a goshinsa.”
Wani makwabcinsa, wanda kuma mamba ne a hukumar tsaron al’umma ta jihar da ya yi ƙoƙarin kai ɗauki a lokacin harin, shi ma an harbe shi kuma yana karɓar magani a wani asibiti a Katsina a halin yanzu.
Maharan sun kuma yi garkuwa da wasu mutane biyar a gidan wani mai suna Shehu Maishayi, tare da Malam Sufi Nahi da kuma matar Malam Abdurrazak, wanda ke zaune a wajen garin Mahuta.
Majiyoyi sun ce sojoji sun iso ne kawai bayan da ’yan bindigar suka tsere daga wurin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga garkuwa da mutane
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
Rundunar Ƴanandan Jihar Bauchi ta kama wani matashi mai suna Umar Yau, wanda aka fi sani da “Snake,” bisa zargin damfara ta yanar gizo da satar bayanan wasu mutane. An kama Yau, mai shekaru 25 daga unguwar Yelwan Makaranta a Bauchi, bayan binciken da aka fara sakamakon ƙorafi daga wata mata da ya damfara.
Fatimah Faiz Ali Bawahab, wata ’yar kasuwa ta yanar gizo, ta kai ƙorafin cewa wani ya ƙirƙiri asusun bogi a Facebook da sunanta da hotunanta don damfarar mutane. CSP Ahmed Wakil, kakakin rundunar, ya ce wanda ake zargin ya ƙirƙiri asusun “Amizeebaby Muhd” inda ya ke tallata kasuwancin ƙarya, yana karɓar kuɗi daga mutane ta asusun banki.
Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin BirtaniyaAn gano cewa an taɓa damfarar wani Nafiu Muhd a watan Maris 2022, inda ya tura kudi zuwa asusun da ke dauke da suna Hansatu Yau, bayan haka aka toshe shi. Daga baya, bincike ya gano cewa ana amfani da sunayen Hansatu Yau da Umar Yau wajen karbar kuɗin jama’a a yanar gizo.
Bayan ƙorafin da aka samu, Kwamishinan ’Yansanda ya umurci gudanar da bincike na fasaha wanda ya kai ga kama Yau a ranar 5 ga Yuni, 2025. An kwato kati tara na ATM, katin zabe, na’urar MiFi, da sauran kayayyakin da suka tabbatar da laifin. Yau ya amsa cewa ya damfari mutane kusan 40 cikin shekaru biyar. An miƙa shi zuwa Rundunar ’Yansandan Kano don ci gaba da bincike da shari’a.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp