Aminiya:
2025-05-01@01:08:20 GMT

’Yan bindiga sun harbi alkali da ɗansa, sun sace mutane 13 a Katsina

Published: 11th, April 2025 GMT

’Yan bindiga sun kai hari garin Mahuta da ke Ƙaramar Hukumar Kafur a Jihar Katsina, inda suka harbi wani alkali, Rabiu Mahuta, a hannu da kuma dansa.

A lokacin harin na daren Talata, maharan sun raunata mutane uku tare da yin garkuwa da wasu mutane 13, ciki har da matar alƙalin da kuma biyar daga cikin ’ya’ansa.

Wani mazaunin garin da ya zanta ya ce ’yan bindigar sun isa wurin ne da misalin karfe 11:30 na dare, kuma kai tsaye suka nufi gidan alkalin, inda suka kwashe kusan awa guda suna ƙoƙarin karya ƙofar gidan.

Cutar Kwastomomi: NERC ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar N628m ’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja

Duk da kiran da alƙalin ya yi wa DPO na yankin domin neman taimako, jami’an tsaro ba su iso a kan lokaci ba.

Ya ce, “Da suka samu nasarar shiga gidan, nan take sun harbe shi a hannu, sai ya faɗi a ƙasa. An kuma raunata ɗansa da raunin harbi a goshinsa.”

Wani makwabcinsa, wanda kuma mamba ne a hukumar tsaron al’umma ta jihar da ya yi ƙoƙarin kai ɗauki a lokacin harin, shi ma an harbe shi kuma yana karɓar magani a wani asibiti a Katsina a halin yanzu.

Maharan sun kuma yi garkuwa da wasu mutane biyar a gidan wani mai suna Shehu Maishayi, tare da Malam Sufi Nahi da kuma matar Malam Abdurrazak, wanda ke zaune a wajen garin Mahuta.

Majiyoyi sun ce sojoji sun iso ne kawai bayan da ’yan bindigar suka tsere daga wurin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga garkuwa da mutane

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna

A Kaduna, an kama wasu mutane uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, ciki har da wani da ya ce ya koma jihar ne domin kafa sabuwar ƙungiya bayan an kama abokan aikinsa a Kwara.

Haka kuma, an kama wasu biyu da ke ɗauke da bindigogi.

‘Yansanda sun gano makamai da dama, ciki har da bindigogi ƙirar AK-47 da AK-49, da kuma wasu makamai da aka ƙera a gida.

Wannan aiki na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na yaƙar garkuwa da mutane da safarar makamai a faɗin ƙasar.

Kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya ce ana ci gaba da bincike, kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargi a kotu da zarar an kammala binciken.

Ya kuma yaba da goyon bayan da al’umma da jami’an tsaro suka bayar wajen nasarar kama su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai ziyarci Katsina
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Binciken Yawaitar Haɗurran Tankokin Man Fetur A Nijeriya 
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara