Aminiya:
2025-12-05@21:43:49 GMT

Mai damfarar fursunoni ya gurfana a kotu a Kano

Published: 11th, April 2025 GMT

An gurfanar da wani mutum a gaban Kotun Majistare ta 17 a Kano bisa zargin shi da karɓar kuɗi a hannun wasu fursunoni da alƙawarin cewa zai fitar da su daga gidan yari.

Ana zargin wanda ake tuhumar, Kabiru Ahmed, da karɓar jimillar kuɗi naira dubu dari shida da goma daga Abdul Mukhtar, Bilkisu Shehu da kuma Muhammad Yahaya da sunan zai yi musu aiki a sako su daga gidan yari.

Lauyar masu gabatar da ƙara, Barista Sadiya Sabo, ta tuhumi mutumin da laifin damfara da kuma cin amanar da aka ba shi.

Wanda ake tuhuma ya amsa laifin, amma ya bayyana cewa ba shi kaɗai ya aikata wannan haramtaccen aiki ba.

’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya

Mai shari’a, Mai shari’a Hudu Haruna, ya bayar da umarnin mika wanda ake zargin ga ’yan sanda domin ci gaba da bincike, kuma ya ɗage shari’ar zuwa 20 ga watan Afrilu da muke ciki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Damfara Gidan Yari

এছাড়াও পড়ুন:

Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro

Majalisar Dattawan Najeriya za ta tantance wanda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa a matsayin Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa, a zamanta na yau Laraba.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa daga ofishin Shugaban Masu Rinjaye na majalisar, Opeyemi Bamidele.

Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi DAGA LARABA: Kalubalen Dake Gaban Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro

Sanarwar ta ce majalisar ta karɓi buƙatar Shugaban Ƙasa Tinubu na tabbatar da wanda aka naɗa Ministan Tsaro.

Sanarwar ta ƙara da cewa za a karanta wasikar a gaban majalisar a ranar Laraba, sannan kuma za a ci gaba da tantance wanda aka naɗa nan take.

Opeyemi ya bayyana cewa majalisar ba za ta iya jinkirta irin wannan buƙata ba a wannan lokaci mai muhimmanci, domin ta shafi muhimman abubuwan da suka shafi ƙasar.

A ranar Talat ace Tinubu ya aike da sunan Christopher gaban majalisar domin amincewa bayan murabus din tsohon Ministan, Muhammad Bdaru Abubakar.

Kafin nadin nasa dai, Christopher shi ne tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya da Tinubu ya sauke tare da ragowar manyan hafsoshi a kwanakin baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • An harbe manomi saboda rikici kan filin kiwo a Borno
  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
  • Tinubu ya san dalilin da ya sa na yi murabus daga muƙamin ministan — Badaru
  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
  • Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu
  • Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro