Mai damfarar fursunoni ya gurfana a kotu a Kano
Published: 11th, April 2025 GMT
An gurfanar da wani mutum a gaban Kotun Majistare ta 17 a Kano bisa zargin shi da karɓar kuɗi a hannun wasu fursunoni da alƙawarin cewa zai fitar da su daga gidan yari.
Ana zargin wanda ake tuhumar, Kabiru Ahmed, da karɓar jimillar kuɗi naira dubu dari shida da goma daga Abdul Mukhtar, Bilkisu Shehu da kuma Muhammad Yahaya da sunan zai yi musu aiki a sako su daga gidan yari.
Lauyar masu gabatar da ƙara, Barista Sadiya Sabo, ta tuhumi mutumin da laifin damfara da kuma cin amanar da aka ba shi.
Wanda ake tuhuma ya amsa laifin, amma ya bayyana cewa ba shi kaɗai ya aikata wannan haramtaccen aiki ba.
’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan NajeriyaMai shari’a, Mai shari’a Hudu Haruna, ya bayar da umarnin mika wanda ake zargin ga ’yan sanda domin ci gaba da bincike, kuma ya ɗage shari’ar zuwa 20 ga watan Afrilu da muke ciki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Damfara Gidan Yari
এছাড়াও পড়ুন:
DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankali
Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta gayyaci Yusuf Datti Baba-Ahmed, tsohon abokin takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar Labour a zaben 2023 tare da Peter Obi.
DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed ne a daren Juma’a bisa zargin ci gaba da bayyana ra’ayoyi da take ganin na iya tayar da hankali a Najeriya.
Wata majiyar tsaro ta ce DSS ta daɗe tana bibiyar kalaman Baba-Ahmed a kafafen yada labarai, musamman kan iƙirarin da ya yi na cewa akwai “rikicin kundin tsarin mulki” a Najeriya.
A cewar majiyar, “Kwanan nan Datti Baba-Ahmed ya bayyana a talabijin inda ya zargi kotuna da rundunar sojoji da rashin hana rantsar da Shugaba Bola Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shettima. Har ma ya yi nuni da cewa rantsar da Tinubu ta bai wa sojoji damar cin mutuncin mutane.
Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali CAF ta ƙara yawan ’yan wasan ƙasashe zuwa 28 a gasar nahiyar AfrikaTa ƙara da cewa irin waɗannan kalamai na iya haifar da tashin hankali a ƙasar, musamman a irin wannan yanayin siyasa da ake ciki.
Ta ce, “Abin damuwa ne ganin yadda irin wannan magana ta janyo rikice-rikice a wasu ƙasashe kamar Guinea-Bissau. Hukumar tsaro tana ɗaukar wannan da muhimmanci, ba don siyasa ba, sai don kare zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.”
A cewar majiyar, DSS ta yi wannan gayyata ne bisa ƙa’ida, saboda kalaman Datti Baba-Ahmed da suka yi kama da raina ƙoƙarin gwamnati wajen inganta tsaro a matsayin “wasa” na iya tayar da hankalin jama’a da kuma rage amincewa da hukumomin ƙasa.
Ta ce, “Wannan gayyatar ba hukunci ba ne, amma matakin kariya ne domin fayyace niyya, da manufar kalamansa a muhallinsu, da kuma hana fitowar labarai da za su iya haifar da rikici ba tare da an yi niyya ba.”
Har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto, DSS ba ta fitar da wata sanarwa ba, haka kuma Datti Baba-Ahmed bai ce komai a hukumance kan gayyatar ba.