Aminiya:
2025-12-06@11:19:00 GMT

Mai damfarar fursunoni ya gurfana a kotu a Kano

Published: 11th, April 2025 GMT

An gurfanar da wani mutum a gaban Kotun Majistare ta 17 a Kano bisa zargin shi da karɓar kuɗi a hannun wasu fursunoni da alƙawarin cewa zai fitar da su daga gidan yari.

Ana zargin wanda ake tuhumar, Kabiru Ahmed, da karɓar jimillar kuɗi naira dubu dari shida da goma daga Abdul Mukhtar, Bilkisu Shehu da kuma Muhammad Yahaya da sunan zai yi musu aiki a sako su daga gidan yari.

Lauyar masu gabatar da ƙara, Barista Sadiya Sabo, ta tuhumi mutumin da laifin damfara da kuma cin amanar da aka ba shi.

Wanda ake tuhuma ya amsa laifin, amma ya bayyana cewa ba shi kaɗai ya aikata wannan haramtaccen aiki ba.

’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya

Mai shari’a, Mai shari’a Hudu Haruna, ya bayar da umarnin mika wanda ake zargin ga ’yan sanda domin ci gaba da bincike, kuma ya ɗage shari’ar zuwa 20 ga watan Afrilu da muke ciki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Damfara Gidan Yari

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatinsa na shirin sayen jirage marasa matuƙa da wasu kayan aiki domin kare yankunan da ke iyakar Kano da Katsina.

Kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.

Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000

Gwamna Abba, ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci sansanin rundunar haɗin gwiwa ta JTF, domin ganin yadda suke shirin kare al’umma daga hare-haren ’yan bindiga a yankunan Tsanyawa da Shanono.

Ya roƙi al’ummar yankunan da abin ya shafa da su riƙa bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani game da duk wani motsi na ’yan bindiga.

Gwamnan ya ce ya kai wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ziyara, domin neman taimako kan lamarin, inda shugaban ya amince da buƙatar da aka gabatar masa cikin gaggawa.

Ya umarci dakarun JTF da su yi duk mai yiwuwa wajen ceto mutanen da aka sace a Tsanyawa da Shanono.

“Mun san cewa waɗannan hare-hare sun jawo asarar rayuka, wasu kuma an yi garkuwa da su. Insha Allah za a ceto su,” in ji shi.

Gwamna Abba ya ce sun kai wannan ziyara ne domin fahimtar halin tsaron yankin da kuma ƙarfafa guiwar jami’an tsaro.

Ya ƙara da cewa irin wannan matsalar tsaro sabon abu ne a Kano, amma gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro domin magance ta.

A yayin ziyarar, ya jajanta wa iyalan mutanen da aka sace tare da tabbatar musu cewa gwamnati na ƙoƙarin ganin an dawo da su cikin gaggawa.

Rahotanni sun nuna cewa aƙalla mutum 10 aka sace a Tsanyawa da Shanono, ciki har da wata tsohuwa da ’yan bindiga suka hallaka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200
  • Yan Sanda Sun Kama Muhuyi Magaji, Tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci a Kano
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • An harbe manomi saboda rikici kan filin kiwo a Borno
  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina