Aminiya:
2025-12-12@07:31:19 GMT

Mai damfarar fursunoni ya gurfana a kotu a Kano

Published: 11th, April 2025 GMT

An gurfanar da wani mutum a gaban Kotun Majistare ta 17 a Kano bisa zargin shi da karɓar kuɗi a hannun wasu fursunoni da alƙawarin cewa zai fitar da su daga gidan yari.

Ana zargin wanda ake tuhumar, Kabiru Ahmed, da karɓar jimillar kuɗi naira dubu dari shida da goma daga Abdul Mukhtar, Bilkisu Shehu da kuma Muhammad Yahaya da sunan zai yi musu aiki a sako su daga gidan yari.

Lauyar masu gabatar da ƙara, Barista Sadiya Sabo, ta tuhumi mutumin da laifin damfara da kuma cin amanar da aka ba shi.

Wanda ake tuhuma ya amsa laifin, amma ya bayyana cewa ba shi kaɗai ya aikata wannan haramtaccen aiki ba.

’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya

Mai shari’a, Mai shari’a Hudu Haruna, ya bayar da umarnin mika wanda ake zargin ga ’yan sanda domin ci gaba da bincike, kuma ya ɗage shari’ar zuwa 20 ga watan Afrilu da muke ciki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Damfara Gidan Yari

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa

Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa

Muhsin Umar Chiroma wanda aka fi sani suna SKD Arewa, xaya ne daga cikin matasan mawaqan zamani da ludayinsu ke kan dawo wajen tashe, musamman a shafukan sada zaumunta. A hirarsa da Aminiya, saurayin mawaqin ya bayyana abin da ya xauki hankalinsa har ya yi wata waqa da ya yi wa laqabi da suna ‘Arewa’.

Muhsin wanda ya fi qwarewa a fagen waqoqin ‘Gambara’, da aka fi sani da Hip Hop, bayyana wa Aminiya cewa, halin da Arewacin Nijeriya ya shiga na rashin tsaro shi ne jigon waqarsa.

A cikin waqar haziqin mawaqin, ya yi tsokaci a kan yadda shugabanni a Arewa suka yi biris da halin da talakawa suka tsinci kansu a ciki na barazanar ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro. Inda yake qoqarin ganin ya jawo hankalin masu muli da ma talakawa don su farka daga barci.

Matashi mawaqin ya ce, “waqata mai taken ‘Arewa’, waqa ce da zan ce na yi ta ne saboda in tayar da shugabanni da kuma talakawan Arewacin Nijeriya daga barci. Domin kuwa ga gobara nan ta tunkaro mu daga kogi amma kuma da alamu babu wanda ya damu da ita.”

Da yake amsa tambayar ko me ya sa ya zavi yin amfani da waqa don wayar da kan jama’a kan muhimmancin haxin kai don tunkarar wannan matsala? Mawaqin zamanin sai ya ce, “ka san kowa da dutsen da ke hannunsa zai yi jifa. Don haka tunda yake ina da fasahar waqa, shi ya sa na ga wannan ita ce, kawai hanya xaya tilo da tafi sauqi wajena in isar da wannan muhimmin saqo.”

Matashin ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu akwai fitattun mawaqan da suka yi waqoqi kan abin da ya shafi tavarvarewar tsaro a qasa. Amma duk da haka, ya dace manya fitattun mawaqa na zamani da duniya ta san su, su qara qaimi wajen wayar da kan matasa don su guji shiga ayyukan laifi da ke jefa qasa cikin rashin tabbas.

SKD Arewa, ya kuma shawarci matasan mawaqa da su rungumi karatu, domin a cewarsa, ilimi ne zai taimaka musu wajen inganta sana’o’insu kuma ya basu damar amfani da shafukan sada zumunta wajen tallata fasahohinsu.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin da miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe ta Jigawa Ta Nemi Kotuna Su Daina Jan Kafa Wajen Aiwatar da Shari’a
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa