Mai damfarar fursunoni ya gurfana a kotu a Kano
Published: 11th, April 2025 GMT
An gurfanar da wani mutum a gaban Kotun Majistare ta 17 a Kano bisa zargin shi da karɓar kuɗi a hannun wasu fursunoni da alƙawarin cewa zai fitar da su daga gidan yari.
Ana zargin wanda ake tuhumar, Kabiru Ahmed, da karɓar jimillar kuɗi naira dubu dari shida da goma daga Abdul Mukhtar, Bilkisu Shehu da kuma Muhammad Yahaya da sunan zai yi musu aiki a sako su daga gidan yari.
Lauyar masu gabatar da ƙara, Barista Sadiya Sabo, ta tuhumi mutumin da laifin damfara da kuma cin amanar da aka ba shi.
Wanda ake tuhuma ya amsa laifin, amma ya bayyana cewa ba shi kaɗai ya aikata wannan haramtaccen aiki ba.
’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan NajeriyaMai shari’a, Mai shari’a Hudu Haruna, ya bayar da umarnin mika wanda ake zargin ga ’yan sanda domin ci gaba da bincike, kuma ya ɗage shari’ar zuwa 20 ga watan Afrilu da muke ciki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Damfara Gidan Yari
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya san dalilin da ya sa na yi murabus daga muƙamin ministan — Badaru
Tsohon Ministan Tsaro, Abubakar Badaru, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya san dalilin da ya sa ya yi murabus.
Badaru, ya ajiye aiki ne a ranar Litinin, inda ya ce matsar rashin lafiya ce ta sa ya yi murabus.
Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokintaShugaban ƙasa ya amince da murabus ɗinsa kuma ya naɗa Janar Chris Musa a matsayin sabon Ministan Tsaro.
Badaru, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa ya yi murabus ne saboda barazanar da Amurka ta yi na ɗaukar matakin soji kan Najeriya game da zargin kisan Kiristoci.
“Ina so na bayyana a fili cewa wannan labari ƙarya ne, an ƙirƙire shi don ɓata min suna, kuma ba shi da alaƙa da ni ko wani da ke magana a madadina,” in ji shi.
Ya ce an ƙirƙiro wannan ƙarya ne don a ɓata masa suna da kuma haddasa rikici tsakaninsa da shugaban ƙasa.
“Gaskiyar dalilin murabus ɗina na bayyana ta shugaban ƙasa. Duk wani ƙarin bayani na daban ƙarya ne da aka ƙirƙira,” in ji Badaru.
Ya tabbatar wa Tinubu da ’yan Najeriya cewa har yanzu yana biyayya, tare da jajircewa wajen ganin an samu zaman lafiya, tsaro da nasarar jam’iyyar APC kafin zaɓen 2027.