Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya
Published: 11th, April 2025 GMT
Wani muhimmin abun lura ma shi ne ita kanta Amurka ba za ta tsira daga mummunan tasirin wannan yaki na cinikayya da take rura wutarsa ba. Ko shakka babu matakin zai haifarwa Amurka matukar koma bayan tattalin arziki, da hauhawar farashi a cikin gida, da dakile guraben ayyukan yi da sauransu. Tuni ma kasuwannin Amurkan suka fara dandana kudarsu, inda aka fara ganin koma bayan kasuwannin hannayen jari, da gurguncewar sana’o’i sakamakon rashin tabbas da kasar ke fuskanta, yayin da kasar ke tunkarar matsanancin yanayi na komadar tattalin arziki.
Wata manuniya da ka iya haskaka abun da ka iya wakana ga Amurka a wannan karo ita ce irin yadda Amurka ta sha fama da kalubalen hauhawar farashi, da koma baya ga sana’ar noma, da ta sarrafa hajoji, yayin da gwamnatin shugaba Trump ta farko ta dauki makamancin wannan mataki a baya. Don haka abu ne a fili, cewa gwamnatin Trump ta yanzu ma za ta dandana kudarta, bisa wannan mataki na karin haraji marar ma’ana da ta sake bullo da shi.
Tuni dai masana, da masu fashin baki suka bayyana illar wannan mataki na Amurka, suna masu cewa kasancewar tattalin arzikin duniya yana sarke da juna, rungumar kariyar cinikayya alama ce ta rashin hangen nesa da toshewar basira. Kuma tuni al’ummun kasa da kasa suka gano makircin da Amurka ta boye karkashin wannan manufa ta karin haraji, don haka dai ba abun da ya ragewa gwamnatin Amurka illa ta lashe amanta, ta gyara babban kuskuren da ta tafka, domin kaucewa yin mummunan da-na-sani.(Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Amurka ta matsa lamba a kan kotun ICC don janye bincike kan yakin Gaza da Afghanistan: Reuters
Gwamnatin shugaban Amurka Donald Trump ta bukaci kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC) ta yi gyara ga yarjejeniyar da aka kafa domin kare Trump da manyan jami’an Amurka daga duk wani bincike na yanzu ko nan gaba, in ji wani jami’in gwamnatin Trump a ranar Laraba. Barazanar dai na kunshe ne da gargadin kara sanya takunkumi idan kotun ta ki bin umarnin.
Kamfanin dillancin labaran reuters ya bayar da rahoton cewa, wa’adin na Washington ya hada da karin wasu bukatu guda biyu: cewa kotun ta ICC ta janye bincikenta kan laifukan yaki da shugabannin Isra’ila suka aikata a lokacin yakin Gaza, da kuma cewa ta rufe binciken da ta yi tun farko kan halin sojan Amurka a Afghanistan. Idan kotu ta ki yin aiki, gwamnatin Amurka na iya sanya sabbin takunkumi kan daidaikun jami’an ICC.
Matsayin gwamnatin Trump na baya-bayan nan ya ginu ne kan takun saka a baya da hukumomin kasa da kasa. Kotun hukunta manyan laifuka ta ICC da ke birnin Hague, ta fuskanci matsin lamba daga Washington tun bayan da ta bude bincike kan ayyukan sojan Amurka a lokacin yakin Afghanistan da kuma a baya-bayan nan, kan matakin da “Isra’ila” ta dauka a zirin Gaza.
Jami’an Trump sun bayyana irin wannan binciken a matsayin na siyasa da kuma cin zarafi ga ikon kasa, kamar dai yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5 December 10, 2025 Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa December 10, 2025 Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD December 10, 2025 Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa. December 10, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi December 10, 2025 Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci