Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya
Published: 11th, April 2025 GMT
Wani muhimmin abun lura ma shi ne ita kanta Amurka ba za ta tsira daga mummunan tasirin wannan yaki na cinikayya da take rura wutarsa ba. Ko shakka babu matakin zai haifarwa Amurka matukar koma bayan tattalin arziki, da hauhawar farashi a cikin gida, da dakile guraben ayyukan yi da sauransu. Tuni ma kasuwannin Amurkan suka fara dandana kudarsu, inda aka fara ganin koma bayan kasuwannin hannayen jari, da gurguncewar sana’o’i sakamakon rashin tabbas da kasar ke fuskanta, yayin da kasar ke tunkarar matsanancin yanayi na komadar tattalin arziki.
Wata manuniya da ka iya haskaka abun da ka iya wakana ga Amurka a wannan karo ita ce irin yadda Amurka ta sha fama da kalubalen hauhawar farashi, da koma baya ga sana’ar noma, da ta sarrafa hajoji, yayin da gwamnatin shugaba Trump ta farko ta dauki makamancin wannan mataki a baya. Don haka abu ne a fili, cewa gwamnatin Trump ta yanzu ma za ta dandana kudarta, bisa wannan mataki na karin haraji marar ma’ana da ta sake bullo da shi.
Tuni dai masana, da masu fashin baki suka bayyana illar wannan mataki na Amurka, suna masu cewa kasancewar tattalin arzikin duniya yana sarke da juna, rungumar kariyar cinikayya alama ce ta rashin hangen nesa da toshewar basira. Kuma tuni al’ummun kasa da kasa suka gano makircin da Amurka ta boye karkashin wannan manufa ta karin haraji, don haka dai ba abun da ya ragewa gwamnatin Amurka illa ta lashe amanta, ta gyara babban kuskuren da ta tafka, domin kaucewa yin mummunan da-na-sani.(Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
Zanga-zanga ta ɓarke a yankin Numan da ke Jihar Adamawa, kan zargin sojoji da kashe wasu mata a garin Lamurde.
Mata sun fito zanga-zangar ne sakamakon rikicin da ya ɓarke tsakanin kabilu Bachama da Chobo.
An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello TurjiA lokacin zanga-zangar an ruwaito cewar mata bakwai ne suka mutu sannan wasu 11 suka jikkata.
Shaidu sun ce sojoji sun buɗe musu wuta yayin da suke tare hanya, suna zargin rundunar da goyon bayan wata ƙabila.
Sai dai rundunar Sojin Najeriya ta musanta wannan zargi.
Ta ce dakarun sun yi artabu ne da wasu ‘yan bindiga a yankin, kuma ta ce mutuwar wasu mata biyu ya faru ne sakamakon buɗe wuta da ‘yan bindigar suka yi, ba wai sojoji suka harbe su ba.
Gwamnatin Jihar Adamawa, ta ayyana dokar hana fita na awa 24 a Lamurde domin daidaita al’amura da zaman lafiya.
A Numan, matan da suka sanya riga ɗauke da launin baƙi ne suka fara zanga-zangar a manyan tituna, inda suke neman yi wa waɗanda aka kashe adalci.
An riga an binne wasu daga cikin waɗanda suka rasu, lamarin da ya ƙara haifar da damuwa a tsakanin al’ummar yankin.
Ɗan Majalisa mai wakiltar yankin, Kwamoti Laori, ya yi Allah-wadai da kisan, inda ya ce ya kamata a gudanar da bincike mai zurfi.
Ya buƙaci hukumomin tsaro da su ɗauki matakin da ya dace, tare da tabbatar da zaman lafiya ba tare da tauye haƙƙin ɗan Adam ba.
Mazauna yankin sun ce rigimar ta jefa mutane cikin tsoro, wanda hakan ya sa da dama suka tsare daga gidajensu.
Shugabannin al’umma a yankin, sun yi kira da a yi sulhu domin kaucewa ƙarin tashin hankali.