Leadership News Hausa:
2025-12-08@01:22:33 GMT

Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

Published: 11th, April 2025 GMT

Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

Wani muhimmin abun lura ma shi ne ita kanta Amurka ba za ta tsira daga mummunan tasirin wannan yaki na cinikayya da take rura wutarsa ba. Ko shakka babu matakin zai haifarwa Amurka matukar koma bayan tattalin arziki, da hauhawar farashi a cikin gida, da dakile guraben ayyukan yi da sauransu. Tuni ma kasuwannin Amurkan suka fara dandana kudarsu, inda aka fara ganin koma bayan kasuwannin hannayen jari, da gurguncewar sana’o’i sakamakon rashin tabbas da kasar ke fuskanta, yayin da kasar ke tunkarar matsanancin yanayi na komadar tattalin arziki.

 

Wata manuniya da ka iya haskaka abun da ka iya wakana ga Amurka a wannan karo ita ce irin yadda Amurka ta sha fama da kalubalen hauhawar farashi, da koma baya ga sana’ar noma, da ta sarrafa hajoji, yayin da gwamnatin shugaba Trump ta farko ta dauki makamancin wannan mataki a baya. Don haka abu ne a fili, cewa gwamnatin Trump ta yanzu ma za ta dandana kudarta, bisa wannan mataki na karin haraji marar ma’ana da ta sake bullo da shi.

 

Tuni dai masana, da masu fashin baki suka bayyana illar wannan mataki na Amurka, suna masu cewa kasancewar tattalin arzikin duniya yana sarke da juna, rungumar kariyar cinikayya alama ce ta rashin hangen nesa da toshewar basira. Kuma tuni al’ummun kasa da kasa suka gano makircin da Amurka ta boye karkashin wannan manufa ta karin haraji, don haka dai ba abun da ya ragewa gwamnatin Amurka illa ta lashe amanta, ta gyara babban kuskuren da ta tafka, domin kaucewa yin mummunan da-na-sani.(Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini

Majalisar Dokokin Amurka ya iso Abuja yayin da ƙasashen biyu ke ƙara matsa ƙaimi wajen tattaunawar diflomasiyya kan haɗin gwiwar tsaro da kuma zargin tauye haƙƙin addini.

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro Nuhu Ribadu, ya ce ya gana da wakilan kuma zuwan tawagar na cikin abubuwan da suka amince da shi a tasu ziyarar da suka kai birnin Washington a watan Nuwamba.

“Tawagar ta ƙunshi ‘yanmajalisar wakilai Mario Díaz-Balart, Norma Torres, Scott Franklin, Juan Ciscomani, da Riley M. Moore,” in ji Ribadu cikin wata sanarwa a shafinsa na sada zumunta.

Kazalika, Jakadan Amurka a Najeriya Richard Mills na cikin tawagar.

A cewar Ribadu, tattaunawar ta mayar da hankali kan yaƙi da ta’addanci, tabbatar da zaman lafiyar yanki da kuma ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba
  • Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya
  • Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri
  • Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika
  • Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • Amurka Tana Sake Yin Bitar Alakar Da Ke Tsakaninta Da Tanzania