Leadership News Hausa:
2025-07-04@01:09:11 GMT

Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

Published: 11th, April 2025 GMT

Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

Wani muhimmin abun lura ma shi ne ita kanta Amurka ba za ta tsira daga mummunan tasirin wannan yaki na cinikayya da take rura wutarsa ba. Ko shakka babu matakin zai haifarwa Amurka matukar koma bayan tattalin arziki, da hauhawar farashi a cikin gida, da dakile guraben ayyukan yi da sauransu. Tuni ma kasuwannin Amurkan suka fara dandana kudarsu, inda aka fara ganin koma bayan kasuwannin hannayen jari, da gurguncewar sana’o’i sakamakon rashin tabbas da kasar ke fuskanta, yayin da kasar ke tunkarar matsanancin yanayi na komadar tattalin arziki.

 

Wata manuniya da ka iya haskaka abun da ka iya wakana ga Amurka a wannan karo ita ce irin yadda Amurka ta sha fama da kalubalen hauhawar farashi, da koma baya ga sana’ar noma, da ta sarrafa hajoji, yayin da gwamnatin shugaba Trump ta farko ta dauki makamancin wannan mataki a baya. Don haka abu ne a fili, cewa gwamnatin Trump ta yanzu ma za ta dandana kudarta, bisa wannan mataki na karin haraji marar ma’ana da ta sake bullo da shi.

 

Tuni dai masana, da masu fashin baki suka bayyana illar wannan mataki na Amurka, suna masu cewa kasancewar tattalin arzikin duniya yana sarke da juna, rungumar kariyar cinikayya alama ce ta rashin hangen nesa da toshewar basira. Kuma tuni al’ummun kasa da kasa suka gano makircin da Amurka ta boye karkashin wannan manufa ta karin haraji, don haka dai ba abun da ya ragewa gwamnatin Amurka illa ta lashe amanta, ta gyara babban kuskuren da ta tafka, domin kaucewa yin mummunan da-na-sani.(Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sanda Sun Hana Yunqurin Fasa Shago a Gombe, Tare da Kwato Babur

 

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta hana yunqurin fasa wani shago da wasu vata-gari suka yi qoqarin yi a Unguwar Buba Shongo da ke cikin birnin Gombe, inda ta qwato wani babur da kayan da ake zargin an yi niyyar amfani da su wajen fasa shagon.

A cewar sanarwar da mai Magana da Yawun Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, lamarin ya faru ne da misalin qarfe 3:00 na safiyar Litinin, 1 ga Watan Yuli, 2025, lokacin da jami’an Operation Hattara ke kan sintiri a daren.

Jami’an sun hango wasu mutane da ba a san ko su wane ne ba suna qoqarin fasa wani shago mallakin wani Muhammadu Adamu Musa, mai shekara 42 da haihuwa.

Da vatagarin suka hango motar sintirin ‘yan sanda na qaratowa, sai suka tsere suka bar shagon ba tare da cimma burinsu ba.

Kayan da aka samu a wurin sun haxa da baqin babur qirar Yamaha mai lamba GME 480 VN da wani qarfe na tanqwara qoafa da takalmin roba guda xaya.

“Dukkan kayan da aka qwato suna hannun ‘yan sanda, kuma bincike yana ci gaba a kan zargin haxa baki da yunqurin aikata laifi,” in ji sanarwar.

Rundunar ta bayyana cewa wannan lamari ya qara tabbatar da cewar dokar da ta takaita zirga-zirgar babura a cikin dare a faxin jihar na nan daram, domin yawan laifukan da ake aikatawa da su a wannan lokaci na dare.

Rundunar ta kuma tabbatar wa da jama’a cewa tana ci gaba da qoqari don kamo waxanda suka gudu tare da gurfanar da su a gaban shari’a.

Haka zalika, rundunar ta buqaci jama’a da su kasance masu lura da abin da ke faruwa a muhallansu tare da ci gaba da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan
  • ‘Yan Sanda Sun Hana Yunqurin Fasa Shago a Gombe, Tare da Kwato Babur
  • ’Yan Majalisar Wakilai bakwai na Akwa Ibom sun koma APC
  • Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro
  • NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta
  • Za mu ɗauki mataki kan mambobinmu da ke shirin shiga haɗakar ADC — PDP
  • Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Ba Za A Iya Kawar Da Fasahar Nukiliya Da Karfi Ba
  • Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci
  • Iran Ta Ce Babu Batun Tattaunawa Duk Tare Da Amurkawa Sun Ce Za’a Yi