Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki a NUPRC — Buba Galadima
Published: 10th, April 2025 GMT
Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya bayyana yadda Shugaba Bola Tinubu, ya taimaki ’yarsa ta samu aiki a Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Ƙasa (NUPRC).
Galadima, ya bayyana haka ne yayin wani shiri a gidan talabijin na AIT.
Matatar Ɗangote ta rage farashin fetur zuwa N865 Yadda masu safarar ɗan Adam ke yaudarar mutane ta intanetYa ce duk da yana yawan sukar gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki, har yanzu shi da Shugaba Tinubu abokai ne.
Ya ce: “Abokai ne mu kuma za mu ci gaba da zama abokai. Idan ina buƙatar wani abu daga gare shi, zan iya tambayarsa.
“Bari na faɗi gaskiya a idon duniya. ’Yata ce ta yi amfani da wayata ta kira Shugaban Ƙasa, shi kuma ya yi zaton ni ne. Sai suka ce ’ya’yana ne, suka sanar da shi al’amura sun yi tsanani.”
Ya ƙara cewa: “Sun faɗa wa Tinubu cewa ‘mahaifinmu ba zai iya wannan ba, amma ya faɗa mana kai abokinsa ne.’
“Ɗaya daga cikinsu ta ce ta kammala NYSC amma ba ta samu aiki a NUPRC wacce Gbenga Komolafe ke jagoranta.
“Tinubu ya ‘kira Komolafe, ya ce ku bai wa ’yar abokina aiki.’ Shi ya sa ta ke son zuwa Makkah don yi wa Allah da Shugaban Ƙasa godiya.”
Galadima ya kuma bayyana cewa ’yarsa ta yi aiki a gwamnatin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari na tsawon shekara huɗu ba tare da an taɓa biyanta albashi ba.
Ya ce: “’Yata ta yi aiki da shi (Buhari) har na tsawon shekara huɗu, kuma ya bayar da umarnin kada a biya ta albashi.
“Sai dai duk wata a kawo takardar da ke nuna an biya ta. Ta yi aiki da Buhari shekara huɗu a ofishin Osinbajo ba tare da ta karɓi ko sisin kwabo ba,” in ji shi.
Galadima, ya kuma ce shi kansa ya yi aiki tare da Buhari na tsawon shekara goma sha uku.
Wannan kalamai sun bai wa mutane da dama mamaki, musamman ganin cewa Galadima ya shahara wajen sukar gwamnatin APC a fili.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
Dan majalisa mai suna muhammad Mirzai ya ce; Kasashen turai sun zaku, akan su sami bayanai akan girman asarar da aka yi wa cibiyoyin Nukiliyar Iran don haka ya zama wajibi Iran din ta yi amfani da siyasar barinsu a cikin duhu.
A yayin zaman da majalisar shawarar musulunci ta Iran ta yi a yau Talata, dan majalisar ya kuma yi bayani akan kallafaffen yakin kwanaki 12, ya yi ishara akan yadda HKI ta yi amfani da kirkirarriyar fasaha da kuma wasu hanyoyi na leken asiri,amma duk da haka ta ci kasa, saboda jagoranci mai cike da fasaha na jagora, da kuma yadda al’ummar kasar ta yi tsayin daka da goyon bayan tsarin musulunci.
Haka nan kuma ya ce; Daga cikin manufofin da HKI ta Shata cewa za ta cimmawa a yayin yakin, shi ne samar da sauyi a cikin wannan yankin, shi ya sa da dama daga cikin hukumomin kasashen larabawa su ka fahimci cewa raunana Iran yana nufin raunana kasashensu.