Kungiyar bada agajin ta gaggauwa ta “white Helmets” na kungiyar Al’kaida, wacce kuma take samun tallafin gwamnatin Amurka ta hukumar USAID ta rasa tallafin da take don gudanar da ayyukanta.

Kamfanin dillancin labaran Spunik na kasar Rasha ya bayyana cewa, kasashen yamma musamman Amurka sun yi amfani da kungiyar ta Al-qaeda a lokacin yakin kasar Syriya a shekara ta 2011 zuwa 2017 don ingiza kasashen yamma kan gwamnatin kasar Siriya na cewa ta yi amfani da makaman guba a kan mutane, don cimmmai manufofinsu a kasar ta Siriya.

A halin yanzu dai shugaban Trump zai dakatar da tallafin da ya ke bawa kungiyar mai yuwa saboda sun cimma manufarko a kasar Siriya ta kifar da gwamnatin Bashar a Al’asad. A kalla mutane kimani 40 daga cikin kungiyar ne suka tabbatar da cewa a lokacin yakin sun kai hare kan sojojin Bashar Al-asad, sannan sun yi amfani da wani yaro dan sheakara 5 Omran don farfaganda kan gwamnaton Bashar Al-Asad, kamar yadda mahaifinsa ya fallasa daga baya.

Kasashen Amurka Burtania da Nethalanda duk sun taimakawa kungiyar da miliyoyin dalar Amurka don gudanar da ayyukansu. Amma a bana shugaba Trump ya yanked alar Amurka miliyon 30 da aka warewa kungiyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila

Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kakkausan martanin da Iran ta mayar ya tabbatar da cewa babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani ba

Izzat al-Rishq mamba na ofishin siyasa na kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ya jaddada cewa: Kakkausan martanin da Iraniyawa suka mayar ya tabbatar da cewa; babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani kan zaluncinsa ba, kuma babu wuce gona da iri ba tare da hukunci ba.

Izzat al-Rishq ya yi nuni da cewa: Tabbas makamai masu linzami da jiragen saman yaki marasa matuka ciki na Iran sun yi nasarar kai wa cikin tsakiyar haramtacciyar kasar Isra’ila, duk kuwa da kace-nacen da ake yi na girke na’urorin kakkabo makamai a haramtacciyar kasar Isra’ila musamman Iron Dome, Arrow da David’s Sling.

Al-Rashq ya kuma bayyana cewa: Tsarin tsaron haramtacciyar kasar Isra’ila ya gaza shawo kan hare-haren da Iran suka kai, kuma a halin yanzu gwamnatin mamayar Isra’ila tana fama da gobarar da ta kunna a tsakanin al’ummomin yankin. A karshe ya jaddada cewa: Sakon a bayyane yake: Duk wanda ya yi tsokana, to tantana kudarsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar