Asbitoci a Abuja babban birnin tarayyar Najeriya wadanda suka hada da Asbitin kasa da kuma na Asokoro duk a ciki suke da wadanda suka ji rauni, ko sun mutu bayan da wata motar daukar gas ta yi hatsari a kan gadar Karu a tsakiyar birnin Abuja a jiya Laraba da misalign karfe 7:14 na yamma.

Jaridar Daily Trust ta Najeriya ta bayyana cewa wasu majiyoyi sun tabbatar da mutuwar muta ne 6 sannan wasu da dama sun ji rauni sanadiyyar hatsarin.

Labarin ya nakalto Mr Mark Nyam mai kula da al-amuran gaggawa na hukumar NEMA ta kasa ya bayyana cewa hatsarin ya auku ne a lokacinda direban motar daukar gas ya burma cikin wasu ababen hawa a kan gadar Karu wanda ya kai ga feshewar tankar gas da yake dauke da shi. Sannan nan da nan wutan ta watsu zuwa wurare da dama kusa da wurin.

Mark ya kara da cewa a halin yanzu dai jami’an tsaro da na ceto daban daban suna aikin tallafawa wadanda abin yashafa da kuma duk wanda yake bukatar taimako a wurin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Miliyoyin Mutane Sun Yi Juyayin Imam Husain ( a.s) A Karbala
  • Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad
  • Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
  • Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutum 50 a Amurka
  • Akalla Mutane 52 Suka Rasa Rayukansu Saboda Ambaliyan Ruwan Sama A Jihar Texas Na Kasar Amurka
  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)
  • ’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
  • Kotu ta umarci a mayar da Sanata Natasha majalisa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
  • Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace