“Wannan shi ne karo na biyu, a shekarar da ta gabata dukkanin ƙananan hukumomi a Nijeriya ta hannun jihohinsu sun samu tallafin buhun shinkafa miliyan ɗaya mai nauyin kilogiram 10. Don haka, a wannan shekarar ma muna sake yin makamancin na bara.”

 

Hashim ya yi tilawar cewa gidauniyar Dangote ta himmatu wajen samar da tallafin kayan abinci ga mabuƙata, tallafi a ɓangaren kiwon lafiya, gina ɗakunan kwanan ɗalibai a jami’o’i, da sauran tallafi ciki har da wanda gidauniyar ta yi a lokacin annobar Korona.

 

Ya ce tallafin dafawa ne kan ƙoƙarin da gwamnatocin jihohi ke yi wa al’ummarsu, ya yi fatan cewa shinkafar da suka kawo Bauchi ɗin za ta je kai tsaye ga waɗanda aka bayar domin su wato marasa ƙarfi da marasa galihu a cikin al’umma.

 

Da ta ke amsar tallafin haɗi da ƙaddamar da rabarwa, Kwamishiniyar ma’aikatar kula da harkokin jin ƙai ta jihar, Hon. Hajara Yakubu Wanka ta nuna matuƙar godiyarsu ga gidauniyar Dangote bisa ga wannan tallafin.

 

Ta ce, a daidai lokacin da suke ƙoƙarin kammala rabon tallafin azumin da gwamnan jihar Bala Muhammad ke yi ne suka samu wannan tallafin daga wajen Dangote, don haka ne ta ce hakan zai ƙara kyautata jin daɗin jama’a a irin wannan watan da jama’a ke fama da azumi.

 

A cewar ta, cikin adadin buhu 25,000 da gidauniyar ta kawo Bauchi, za a rabar da guda 500 ga kowace ƙaramar hukuma daga cikin su 20, sai kuma guda dubu 10 da aka ware domin rabarwa a masallatai da cocina, gami da sauran guda 5,000 da za a rabar ga sauran masu ruwa da tsaki.

 

Shi ma a jawabinsa a madadin ƙananan hukumomin jihar Bauchi kuma shugaban ALGON na jihar, Hon. Mahmood Baba Ma’aji ya fara ne da gode wa gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad a bisa tallafin da ya rabar ga ƙananan hukumomin jihar.

 

Hon. Ma’aji ya ce a satukan da suka wuce ne gwamnan ya ƙaddamar da rabon tallafin azumin wanda kowace ƙaramar hukuma sai da ta ci gajiyar hakan.

 

A gefe guda, ya gode wa gidauniyar Dangote bisa ƙara samar da tallafi a jihar ya bada tabbacin cewa za su sanya ido wajen rabon kayan tare da tabbatar da cewa a waɗanda suka dace su ci gajiyar tallafin ne suka amfana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gidauniyar Dangote

এছাড়াও পড়ুন:

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

A yau, 17 ga watan Satumba, Shugaba Tinubu ya ɗage dokar ta-ɓaci da ya ƙaƙaba wa al’ummar jihar Ribas biyo bayan rashin jituwa da yaƙi ci yaƙi cinyewa da ya dabaibaye ɓangaren zartarwa da na dokokin jihar. Cikakken bayani na nan tafe…

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar