Kungiyar Ansarullah Ta Ce Keta Hurumin Kasar Da Amurka Ta Yi Zai Gamu Da Maida Martani
Published: 17th, March 2025 GMT
Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Abdulmalik Badruddeen Huthi ya bayyana cewa hare-haren ta’adanci wadanda sojojin Amurka da Burtaniya suka kai kan yankuna da dama a kasar ba zasu hana mutanen kasar ci gaba da kare Falasdinawa a Gaza ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Al-huthi yana fadar haka a wani jawabin da ya gabata a jiya Lahadi da yamma.
Kafin haka dai jiragen saman yakin wadanda suka taso daga kan kataparen jirgin ruwa mai daukar Jiragen yaki na kasar Amurka sun kai hare hare a yankuna da dama a kasar ta Yemen wadanda suka hada da birnin San’a babban birnin kasar. Hare-haren dai sun kashe yara da mata da dama sannan sun lalata injunan wutan lantarki da dama.
Kungiyar Ansarullah ta kasar yemen dai ta tallafawa Falasdinawa a yankin tufanul Aksa wanda aka fara a ranar 7 ga watan octoban shekara ta 2023. Har zuwa lokacin da aka tsagaita wuta a ranar tsakanin Falasdinawa a Gaza da HKI a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025.
Amma a cikin yan makonnin da suka gabata HKI ta hana abinci da magunguna da kuma sauran bukatun Falasdinawa shiga yankin na Gaza. Wanda ya sa kungiyar ta koma tana hana jiragen HKI wucewa ta Tekun maliya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato
Mataimakinsa kan harkokin majalisa Honarabul Attahiru Danmadi ne ya wakilci dan majalisar ya kuma tabbatarwa wadanda lamarin ya shafa kokarinsa kan daukar matakan da suka kamata domin tabbatar da tsaron rayukan su da dawowa da zaman lafiya a yankunan.
Garuruwan da ‘yan bindigar suka tarwatsa a gundumar Kuchi sun hada da Fakku, sha’alwashi, tulluwa da Rafin- gora a inda mutane bakwai suka rasa rai. A gundumar Jabo kuwa kauyukan da lamarin ya shafa su ne; Gesolodi, Hilya, Guraye, Guma, Chakai, Modo, Badariya, Tafki, Balera, Gudumawa da Rafin shinka.
“Mun girgiza kwarai da wannan halin da kuke ciki. A matsayina na wakilin ku, zan ci-gaba da kokarin da ya kamata a majalisa domin ganin jami’an tsaro sun kawo karshen wannan ta’addancin.”
Dan Majalisar ya ce ya gabatar da bukata ga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa domin tallafawa wadanda lamarin ya shafa kuma zai ci- gaba da bibiya domin ganin tallafin ya samu cikin lokaci.
Ya ce yana kokarin ganin rundunar sojoji ta kara tura wadatattun jami’ai tare da tallafa masu domin yakar ‘yan ta’addan da wanzar da zaman lafiya a yankunan.
Tallafin kayan abinci na gaggawa da dan majalisar ya bayar sun hada da buhuhuwan masara, gero, garin kwaki da kuma kuli- kuli.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp