Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Abdulmalik Badruddeen Huthi ya bayyana cewa hare-haren ta’adanci wadanda sojojin Amurka da Burtaniya suka kai kan yankuna da dama a kasar ba zasu hana mutanen kasar ci gaba da kare Falasdinawa a Gaza ba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Al-huthi yana fadar haka a wani jawabin da ya gabata a jiya Lahadi da yamma.

Ya kuma kara da cewa sojojin kasar zasu ci gaba da kai hare hare kan katafaren jirgin ruwan yaki mai daukar jiragen saman yaki na Amurka dake cikin Tekun maliya. Sannan zasu ci gaba da kai hare hare kan jiragen HKI da na Burtania da na Amurkan masu wucewa ta tekun malia kamar yadda ta bayyana tun farko.

Kafin haka dai jiragen saman yakin wadanda suka taso daga kan kataparen jirgin ruwa mai daukar Jiragen yaki na kasar Amurka sun kai hare hare a yankuna da dama a kasar ta Yemen wadanda suka hada da birnin San’a babban birnin kasar. Hare-haren dai sun kashe yara da mata da dama sannan sun lalata injunan wutan lantarki  da dama.

Kungiyar Ansarullah ta kasar yemen dai ta tallafawa Falasdinawa a yankin tufanul Aksa wanda aka fara a ranar 7 ga watan octoban shekara ta 2023. Har zuwa lokacin da aka tsagaita wuta a ranar tsakanin Falasdinawa a Gaza da HKI a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025.

Amma a cikin yan makonnin da suka gabata HKI ta hana abinci da magunguna da kuma sauran bukatun Falasdinawa shiga yankin na Gaza. Wanda ya sa kungiyar ta koma tana hana jiragen HKI wucewa ta Tekun maliya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza

Bayanai daga Falasdinu na cewa akalla Falasdinawa 35 dane  suka hada da kananan yara aka kashe a wanisabon kisan kiyashi na Isra’ila a zirin Gaza.

A cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza, wadannan hare-haren sun yi sanadin mutuwar mutane 35 tare da jikkata 109 a cikin sa’o’i 24 da suka gabata.

Adadin wadanda sukayi shahada sakamakon yakin kisan kare dangi da Isra’ila ke yi a yankin da aka yi wa kawanya ya zarce 52,400.

Adadin wadanda suka jikkata kuma ya kai kusan 118,014 tun daga watan Oktoban 2023.

Majalisar Dinkin Duniya dai ta yi gargadin barkewar ayyukan jin kai a Gaza.

Hukumar samar da abinci ta duniya (WFP) ta fitar da wani kakkausan gargadi game da matsalar jin kai da ke kara tabarbarewa a Gaza a dai dai lokacin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-haren bama-bamai da kuma killace fararen hula da ke fama da yunwa.

Tun cikin watan Maris ne Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya haramta kai kayan agaji zuwa Gaza, a wani mataki da ya ce na da nufin tursasa Hamas ta amince da tsawaita matakin farko na yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Da Alamu Amurka Ta Fara Dandana Kudarta
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut