Gwamnatin Jihar Jigawa, tare da hadin gwiwar Bankin Duniya, ta dauki nauyin dalibai sama da 500 a wani mataki na tsara makomar matasa a fannin fasahar zamani.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan yayin bikin kaddamar da shirin da kuma mika takardun shaidar karatu ga wadanda suka ci gajiyar shirin fasahar zamani na Innovation Development and Effectiveness in the Acquisition of Skills (IDEAS) a Jihar Jigawa.

Malam Umar Namadi ya jaddada kudirin gwamnatinsa na karfafawa matasa ta hanyar kirkire-kirkire a fannin fasahar zamani da kuma koyon sana’o’i don habaka tattalin arziki.

“A yau, mun kammala horar da dalibai 240 da suka koyi yadda za su bunkasa  harkokinsu na kasuwanci don tabbatar da ci gaba mai dorewa,” in ji gwamnan.

“Haka kuma, a yau muna mika takardun shaidar karatu ga dalibai 550 da suka sami guraben karatu ta hannun Hukumar Samar da Ayyuka da Taimakon Matasan Jihar Jigawa, tare da hadin gwiwar Bankin Duniya, Arms of Ideas, da gwamnati.”

A cewarsa, wadannan dalibai da suka sami guraben karatu a Jami’ar Baze za a horas da su a fannonin fasahar zamani da ke taka muhimmiyar rawa a kasuwannin duniya.

Gwamna Namadi ya bayyana cewa karkashin wannan shiri, Gwamnatin Jihar Jigawa da Bankin Duniya sun saka hannun jarin sama da Naira miliyan 100 domin tabbatar da samun ingantaccen ilimi da koyon sana’o’i.

“Wannan kudade hadin gwiwa ne tsakanin Bankin Duniya da Gwamnatin Jihar Jigawa. Bankin Duniya ya bayar da Naira miliyan 85, yayin da gwamnatin jihar ta bayar da Naira miliyan 50, kuma an riga an biya kudaden gaba daya.”

Ya kara da bayanin cewa shirin zai ba dalibai damar koyon akin binciken sirri, (Artificial Intelligence), da fasahar blockchain, binciken kasuwanci (Business Intelligence), da tsaron yanar gizo (Cybersecurity), da sauransu.

Baya ga horon fasahar zamani, gwamnan ya kuma sanar da kammala horas da matasa ‘yan kasuwa 240 da suka samu horo kan hanyoyin bunkasa kasuwancinsu. Ya kara da cewa kowannensu zai samu tallafin jari na Naira 50,000 domin fadada kasuwancinsu da kuma tabbatar da dorewarsa.

Saboda haka, Gwamna Namadi ya bukaci daliban da su yi amfani da wannan dama yadda ya kamata, tare da tabbatar musu da karin tallafi ga wadanda suka yi fice a karatunsu.

“Ina bukatar ku yi kokari don cimma wannan buri. Duk wani dalibi da ya kammala karatu da Upper Credit ko Distinction zai samu sabuwar kwamfutar tafi-da-gidanka (laptop) domin tallafa masa!”

Ya sake tabbatar da goyon bayan gwamnatinsa ga fannin fasahar zamani,  da karfafawa matasa tattalin arziki a Jihar Jigawa, tare da alkawarin gabatar da karin manufofi da shirye-shirye don inganta rayuwarsu da kuma bunkasa sana’o’insu.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Bankin Duniya Jigawa Gwamnatin Jihar fasahar zamani Bankin Duniya Jihar Jigawa tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Babban sakataren MDD António Guterres, ya bayyana a jiya Talata cewa, jerin shawarwarin da Sin ta gabatar wato shawarar raya duniya, shawarar tabbatar da tsaron duniya, shawarar raya wayewar kan al’ummun duniya, da kuma jagorantar harkokin duniya, sun dace da ka’idar kundin tsarin MDD.

Guterres ya bayyana hakan ne yayin da yake amsa tambayoyin ‘yan jarida a wani taron manema labarai da aka yi a ranar. Ya ce shawarwarin da Sin ta gabatar sun mutunta manufar kasancewar bangarori da dama, kuma sun goyi bayan MDD a matsayin cibiyar hadin gwiwar kasa da kasa, tare da dukufa kan inganta hadin gwiwa tsakanin kasashe daban daban da warware rikice-rikice cikin lumana.

Guterres ya kara da cewa, yanzu ana fuskantar rarrabuwar kawuna a fagen siyasa ta duniya da kuma karuwar yaduwar rikice-rikice, da ma rashin hukunta masu laifi. Bugu da kari, sabbin fasahohi suna ci gaba da bullowa “ba tare da bin wani tsari ba”, yayin da rashin daidaito ke kara tsananta. A wannan yanayi, babban taro karo na 80 na MDD mai tsawon mako guda da za a fara a mako mai zuwa, zai ba da duk wata dama ga tattaunawa da shiga tsakani.(Amina Xu)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar