Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-18@17:24:14 GMT

Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Makarantu A Jihar Kwara

Published: 13th, March 2025 GMT

Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Makarantu A Jihar Kwara

Sama da mutane 100 ne mazauna garin Ijagbo da ke karamar hukumar Oyun ta jihar Kwara suka rasa matsugunansu sakamakon ruwan sama ya yi barna a cikin al’umma.

 

Gidan Rediyon Najeriya ya tattaro cewa an lalata cibiyoyin ilimi da gidajen zama da rumfunan kasuwa tare da lalata dukiyoyi.

 

Guguwar ruwan sama ta yi barna a kwalejin Ansar Deen da ke Ijagbo yayin da ajujuwa sama da 10 suka yi lalace, inda dalibai da malamai suka makale.

 

An gano cewa guguwar ta afku ne da misalin karfe 4 na yamma. a ranar Litinin, tare da yaga rufin ajujuwan tare da lalata muhimman kayan koyo da kuma kawo cikas ga ayyukan ilimi.

 

Da suke Magana game da wannan ibdi’in, shugabannin makarantar, Mista Olaniyi Musbaudeen da Misis Saheed, sun yi kira ga gwamna AbdulRahman AbdulRazaq da ya gaggauta kawo musu tallafi domin dawo da ababen more rayuwa da suka lalace.

 

“Mun yi matukar bakin ciki da wannan bala’in. Rugujewar wadannan ajujuwa na haifar da babbar barazana ga karatun dalibanmu,” in ji Mista Musbaudeen.

 

A halin yanzu kwamishinan ilimi na jihar Kwara Dr Lawal Olohungbebe ya ziyarci makarantar da lamarin ya shafa domin tantance irin barnar da aka yi .

 

Ya kuma baiwa mahukuntan makarantun da sauran al’ummar jihar tabbacin shirin gwamnatin jihar na maido da kayayyakin da abin ya shafa.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara Ruwan Sama

এছাড়াও পড়ুন:

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

A nan gaba za ayi bayani kan ilimin da muhimmancin da yake da shi ga mutane daidaikai,da kuma al’umma.Kai har ma dalilin da yasa aka samu nau’ukan ilimi daban-daban da kuma gamsassun daliliai na lamurran ilimi.

 

Minene Ilimi?

World Vision a shekarar (2021)ya bayyana ilimi a matsayin wata hanya ce da mutane suka karuwa da ilimi ko kuma ya san wani labara wanda yana zama ilimi sannu a hankali. Bugu da kari wurin koyon ilimi ya zama shi ma wuri ne da mutum/ mutane za su bunkasa dabarunsu na rayuwa da sua kasance dole,su gane dokoin da suka kasance dole ne a sansu,su gane yadda za su gabatar da hukuncin da ya dace mai kuma amfani, su kuma gane bambanci tsakanin maikyau da marakyau.Mi yasa ilimi yake da amfani ga al’umma?Ilimi yana da amfani ga al’umma saboda shine hanya mafita ta taimakawa al’umma su gane yadda rayuwa take, da kuma yadda suma za su bada tasu gudunmawar gare su. (Abulencia, 2021).

Kowace kasa tana da nata irin tsarin iliminta.Sai dai kuma da akwai bambanci ba dan kadan ba, alal misali abubuwan da za ayi amfani dasu da kuma kudi da ake amfani da su domin taimakawa irin tsarin ilimi da ake amfani da shi,wanda hakan yake.Kamar dai yadda wani zai yi tsammani wani ci gaban kasa yana da alaka da irin tsarin ilimin da take da shi/ ko amfani da shi wato kasafin kudi irin yawan kidin da ake warewa bangaren.Kasashe su kan rasa abubuwan more rayuwa da suka zama dole kamar tsaftataccen ruwan sha,irin su ba za a sa ran za su taimakawa samar da ingantaccen ilimi ko irin ilimin da yake na bai daya da ya shafi makarantar da mutum ya fara. (Lumen, n.d.)

Duk da yake da akwai nau’oin ilimi da akwai makarantar gargajiya wadda ake amfan da ita domin a gane irin fahimta ko hazakar shi dalibin. 

(Abulencia, 2021)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar NAHCON Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Jihar Jigawa
  • ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno
  • Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara
  • Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas
  • Max Air Zai Yi Jigilar Alhazan Jihar Jigawa A Ranakun 20 Da 21 Ga Watan Mayu
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga da ƙwato shanun sata 1000 a Taraba 
  • Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka
  • Mashawarci tsohon shugaban Ƙasa kan Sufuri Jiragen Sama ya rasu
  • Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)