Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Makarantu A Jihar Kwara
Published: 13th, March 2025 GMT
Sama da mutane 100 ne mazauna garin Ijagbo da ke karamar hukumar Oyun ta jihar Kwara suka rasa matsugunansu sakamakon ruwan sama ya yi barna a cikin al’umma.
Gidan Rediyon Najeriya ya tattaro cewa an lalata cibiyoyin ilimi da gidajen zama da rumfunan kasuwa tare da lalata dukiyoyi.
Guguwar ruwan sama ta yi barna a kwalejin Ansar Deen da ke Ijagbo yayin da ajujuwa sama da 10 suka yi lalace, inda dalibai da malamai suka makale.
An gano cewa guguwar ta afku ne da misalin karfe 4 na yamma. a ranar Litinin, tare da yaga rufin ajujuwan tare da lalata muhimman kayan koyo da kuma kawo cikas ga ayyukan ilimi.
Da suke Magana game da wannan ibdi’in, shugabannin makarantar, Mista Olaniyi Musbaudeen da Misis Saheed, sun yi kira ga gwamna AbdulRahman AbdulRazaq da ya gaggauta kawo musu tallafi domin dawo da ababen more rayuwa da suka lalace.
“Mun yi matukar bakin ciki da wannan bala’in. Rugujewar wadannan ajujuwa na haifar da babbar barazana ga karatun dalibanmu,” in ji Mista Musbaudeen.
A halin yanzu kwamishinan ilimi na jihar Kwara Dr Lawal Olohungbebe ya ziyarci makarantar da lamarin ya shafa domin tantance irin barnar da aka yi .
Ya kuma baiwa mahukuntan makarantun da sauran al’ummar jihar tabbacin shirin gwamnatin jihar na maido da kayayyakin da abin ya shafa.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara Ruwan Sama
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido A Karamar Hukumar Gwiwa
Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa Alhaji Aminu Zakari, yace ziyarar kwamatin a kananan hukumomin jihar 27 tana bada damar ganawa kai tsaye a tsakanin masu ruwa da tsaki domin karfafa dabi’ar aiki tare da juna da kuma kyautata alaka a tsakanin bangarori daban daban.
Ya yi wannan tsokaci ne lokacin da ya jagoranci ‘yan kwamatin domin ziyarar aiki a sakatariyar karamar hukumar Gwiwa.
Yace a lokacin irin wannan ziyarar, kwamatin yana duba kundin bayanan sha’anin mulki da na harkokin kudi domin tabbatar da gudanar harkokin kananan hukumomi kamar yadda ya kamata, ta hanyar aiki da tanade-tanade da kuma ka’idojin kashe kudade.
Alhaji Aminu Zakari ya kuma lura cewar Kwamatin yana kafa kananan kwamitoci domin ziyarar gani da ido dan tantance ayyukan raya kasa a lungu da sakon karamar hukumar domin tabbatar da cin moriyar kashe kudaden gwamnati ta hanyar ayyuka masu inganci.
A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Gwiwa, Malam Muhammad Abubakar Zakari, ya bayyana kwarin gwiwar cewa ziyarar kwamatin za ta zaburar da shugabanni wajen kashe kudade ta hanyar da ta dace, tare da wanzar da shugabanci nagari.
Malam Muhammad Zakari ya kuma sha alwashin bada cikakken hadin kai da goyon baya domin samun nasarar ziyarar.
Kazalika, ya bada tabbacin amfani da shawarwarin kwamatin domin ci gaban karamar hukumar sa.
Sauran ‘Yan kwamatin sun hada da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama, Alhaji Sani Sale Zaburan da wakilin Malam Madori Alhaji Hamza Adamu Ibrahim Babayaro da sakataren Kwamatin da mataimakan sa da Oditoci biyu.
Usman Mohammed Zaria