Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Makarantu A Jihar Kwara
Published: 13th, March 2025 GMT
Sama da mutane 100 ne mazauna garin Ijagbo da ke karamar hukumar Oyun ta jihar Kwara suka rasa matsugunansu sakamakon ruwan sama ya yi barna a cikin al’umma.
Gidan Rediyon Najeriya ya tattaro cewa an lalata cibiyoyin ilimi da gidajen zama da rumfunan kasuwa tare da lalata dukiyoyi.
Guguwar ruwan sama ta yi barna a kwalejin Ansar Deen da ke Ijagbo yayin da ajujuwa sama da 10 suka yi lalace, inda dalibai da malamai suka makale.
An gano cewa guguwar ta afku ne da misalin karfe 4 na yamma. a ranar Litinin, tare da yaga rufin ajujuwan tare da lalata muhimman kayan koyo da kuma kawo cikas ga ayyukan ilimi.
Da suke Magana game da wannan ibdi’in, shugabannin makarantar, Mista Olaniyi Musbaudeen da Misis Saheed, sun yi kira ga gwamna AbdulRahman AbdulRazaq da ya gaggauta kawo musu tallafi domin dawo da ababen more rayuwa da suka lalace.
“Mun yi matukar bakin ciki da wannan bala’in. Rugujewar wadannan ajujuwa na haifar da babbar barazana ga karatun dalibanmu,” in ji Mista Musbaudeen.
A halin yanzu kwamishinan ilimi na jihar Kwara Dr Lawal Olohungbebe ya ziyarci makarantar da lamarin ya shafa domin tantance irin barnar da aka yi .
Ya kuma baiwa mahukuntan makarantun da sauran al’ummar jihar tabbacin shirin gwamnatin jihar na maido da kayayyakin da abin ya shafa.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara Ruwan Sama
এছাড়াও পড়ুন:
Save The Children Ta Shirya Taron Bita Ga Yan Jarida Da Kungiyoyi Masu Zaman Kansu A Kaduna.
A wani yunƙuri na ƙarfafa ilimi mai inganci, adalci da shigar da kowa a cikinsa ga yara da matasa a Jihar Kaduna, ƙungiyar Save the Children ta shirya taron bita na kwana biyu ga yan jarida da kungiyoyi masu zaman kansu a Kaduna.
Taron ya haɗa wakilai daga sashen ilimi, kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin masu zaman kansu.
Taron wani ɓangare ne na babban shiri da ke da nufin haskaka ƙalubale da damar da ke akwai wajen dawo da yara makarantun da kuma tabbatar da samun ingantaccen ilimi.
Rahoton Hukumar Ƙididdiga ta Jihar Kaduna na shekarar 2020 ya nuna cewa fiye da yara dubu 700,000 ne basa zuwa makaranta a jihar – adadi mafi yawa a Najeriya.
Wannan matsala ta nuna bukatar daukar matakai na gaggawa da samarda domin kawar da duk wasu kalubale da ke hana yara shiga makaranta, ƙara adadin masu rajistar shiga makaranta da kuma inganta yadda ake koyarwa da koya.
Da yake jawabi a taron, Daraktan Tsare-tsare na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Malam Salisu Baba Lawal, tare da Mataimakin Shugaban Ayyuka, Hassan Abdul, sun tabbatar da cewa gwamnatin jihar na da niyyar rage adadin yaran da basa zuwa makaranta.
Sun bayyana cewa jihar na aiki tare da abokan haɗin gwiwa ciki har da Save the Children da UNICEF, domin shigar da yara akalla 200,000 cikin tsarin ilimi na yau da kullum.
Sun jaddada muhimmancin tabbatar da cewa shirin ya shafi kowane ɗalibi, musamman masu buƙatu na musamman.
Sun bayyana cewa aiwatar da wannan shiri mai da hankali kan yara yana da matuƙar muhimmanci, musamman a makarantun da ke da yawan yara masu cutar autism, domin hakan zai iya haɓaka ingancin karatu da tabbatar da cewa ba a bar ko wane yaro a baya ba.
Wadanda suka halarci taron sun jaddada rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen wayar da kai da kuma ƙarfafa fafutukar neman ilimi mai shigar da kowa.
Daya daga cikin manyan abubuwan da aka cimma a taron shi ne tsara shirin tallata batun yara da basa zuwa makaranta ta hanyar amfani da labarun rayuwa, fasahar da muradun yara domin tasiri ga manufofi da kuma ƙarfafa haɗin kan al’umma.
Shugaban Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen Jihar Kaduna, Malam AbdulGhaffar Alabewele, ya yaba wa masu shirya taron bisa yadda suka haɗa ‘yan jarida tun daga farko.
Ya ce hakan zai taimaka wajen fahimtar shirin da kyau da kuma samar da haɗin kai mai ma’ana.
Wani mahalarci daga Radio Nigeria Kaduna, Malam Adamu Yusuf, ya roƙi Gwamnatin Jihar Kaduna da ta ɗauki malamai ƙwararru a makarantun firamare, musamman a cikin yankunan karkara da ke da buƙata sosai.
Wasu daga cikin mahalarta sun bayyana taron a matsayin Wanda ya zo a lokacin da ya dace la’akari da yawan yara masu cutar autism da ke ƙaruwa da kuma buƙatar ƙarin tsarin tallafi.
Wani daga cikin mahalartan ya jaddada muhimmancin fara shirye-shiryen gwamnati da ke mai da hankali kan yara masu buƙatu na musamman, yana mai cewa fara tun da wuri yana da matuƙar tasiri wajen gina makoma mai haɗin kai da ci gaba.
A lokacin taron, an gabatar da bayanai daban-daban da suka bayyana manyan ƙalubalen da ilimi ke fuskanta a Jihar Kaduna da kuma hanyoyin aiwatar da shirin shekaru huɗu cikin nasara domin tabbatar da cewa kowane yaro ya samu ilimi mai nagarta.
Wannan shiri wani ɓangare ne na babban yunƙuri domin tabbatar da cewa dukkan yara a Jihar Kaduna—ko daga wane asali ko halin rayuwa—an ba su damar koyo, girma da cimma burinsu a rayuwa.
COV: Adamu Yusuf