Gwamnan Zamfara Ya Haɗa Kai Da Kamfanonin Sin Don Habaka Tsaro
Published: 13th, March 2025 GMT
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya haɗa hannu da kamfanonin ƙasar Sin don samar da ingantattun fasahohin zamani da inganta noma, sufuri da ma’adanai na jihar.
A ranar Talata ne gwamnan ya karbi baƙuncin masu kamfanoni na ƙasar Sin a gidan gwamnati da ke Gusau.
A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa gwamna Lawal ya jagoranci tawagar gwamnatin jihar a ziyarar aiki a ƙasar Sin daga ranar 15 zuwa 21 ga watan Fabrairun 2025, domin yin haɗin gwiwa a muhimman sassa.
Sanarwar ta ƙara da cewa, tawagar ta Zamfara ta yi hulɗa da kamfanonin Zhong Zhao International Group, Phoenix Wings, Shenzhen HighGreat Innovation Technology Development Co., Ltd, da Xiamen Magnetic North Technology Co., Ltd yayin da suke ƙasar Sin.
Tang Zhangwei, ya jagoranci wasu kamfanoni zuwa jihar Zamfara, domin ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu a sassa masu muhimmanci, domin bunƙasa tattalin arziki.
A nasa jawabin, gwamna Lawal ya yaba da ƙoƙarin da kamfanonin ƙasar Sin ke yi na tabbatar da nasarar haɗin gwiwarsu.
“Ina so in yi muku barka da zuwa Jihar Zamfara. Muna maraba da ku. A watan Fabrairu, na jagoranci wata tawaga zuwa ƙasar Sin don ganawa da kamfanoni a sassa daban-daban da kuma gano ci gaban da za su samar. Tafiya ce mai tasirin gaske.
“Mun yi haɗin gwiwa da kamfanin ƙasa da ƙasa na Zhong Zhao, wanda ya kware a fannin takin zamani da noman zamani. Suna mai da hankali kan samar da takin gargajiya da fasahar kiwo na R&D. Mun rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna domin horar da manoman gida sana’o’in noma, ta hanyar amfani da injina da fasahar zamani wajen kafa masana’antar takin zamani a jihar Zamfara.
“Tawagar Zamfara ta yi hafin gwiwa da kamfanin Phoenix Wings, wani kamfanin ƙasar Sin da ya ƙware kan fasahar sa ido kan tsaro, gami da jirage marasa matuƙa. A tare, za su bullo da dabarun samar da ingantattun tsare-tsare na magance matsalar ‘yan bindiga, garkuwa da mutane, da ƙalubalen tsaro a jihar Zamfara.
“A taronmu da kamfanin Shenzhen HighGreat Innovation Technology Development Co., Ltd, mun tattauna batun ƙirƙire-ƙirƙire, samar da jirage marasa matuƙa da sauran fasahohi.
“Mun ɗauki nauyin kamfanonin Xiamen Magnetic North Technology Co., Ltd. da Xiamen King Long United Automobile Industry Co., Ltd. An gabatar da shawarwari don bunƙasa cibiyoyin sufuri na zamani da gabatar da tsarin zirga-zirgar jama’a don inganta sufuri a ciki da wajen jihar.
“Bugu da ƙari, mun yi taro mai nasara tare da kamfanin WEICAI LOVOL International Trading Company, wanda ke mai da hankali kan noman zamani, wanda a Turance ake kira ‘Smart Agriculture, ‘Integrated Management Platform’, da amfanin da injinan noma.
“Tawagar Zamfara ta gana da kamfanin Tibet Ming inda suka tattauna batun ƙara zuba jari a harkar haƙar ma’adanai, da jaddada ayyuka masu ɗorewa, ɗawainiyar jama’a, da fasahar zamani don bunƙasa haƙo ma’adinai a jihar Zamfara,” Inji Gwamna Lawal.
Tun da farko, sakataren gwamnatin jihar Zamfara, Malam Abubakar Nakwada, wanda ke cikin tawagar jihar a ƙasar Sin, ya bayyana nasarorin da suka samu a ziyarar aiki.
Ya ce, “Mun kai ziyarar aiki mai inganci a ƙasar Sin, kuma sakamakon ya bayyana a yau bayan da wasu manyan kamfanoni suka zo jihar Zamfara.”
Aminu Dalhatu/Gusau
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Tsaro Zamfara a jihar Zamfara haɗin gwiwa a ƙasar Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya maƙale a Guinea-Bissau bayan da sojoji suka yi juyin mulki tare da karɓe ragamar mulkin ƙasar.
Jonathan da sauran baƙi baƙi masu sanya ido kan zaɓen da aka gudanar, ba za su iya barin ƙasar ba domin sojoji sun rufe iyakokin ƙasar baki ɗaya, tare da dakatar da zaɓen gaba ɗaya.
Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniyaLamarin ya samo asali ne bayan manyan ’yan takara biyu sun yi iƙirarin samun nasara a zaɓen shugaban ƙasa da ya gudana.
Ba jimawa wasu dakarun sojin ƙasar suka hamɓarar da gwamnatin farar hula ta ƙasar.
Sun kuma sanar da dokar hana fita da kuma kama manyan jami’an da ke da alaƙa da zaɓen.
“An hamɓarar da gwamnatina,” in ji Shugaba Umaro Sissoco Embalo cikin wata tattaunawa ta waya da gidan talabijin na ƙasashen waje.
Jonathan ya je Guinea-Bissau ne a matsayin shugaban tawagar West African Elders Forum (WAEF) domin sanya ido kan zaɓen.
Ya ziyarci wasu rumfunan zaɓe a ƙasar kuma ya wallafa bayanai a kafafen sada zumunta kafin juyin mulkin.
Mutanen da ke tare da shi sun ce yana cikin ƙoshin lafiya, amma ba shi da damar barin ƙasar.
Sojojin suna kuma ƙoƙarin katse Intanet, lamarin da ya sa ake samun tangarɗa wajen sadarwa a ƙasar.
Hakan ya sa ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa suka fara nuna damuwa kan tsaron manyan ’yan siyasa da jami’an zaɓe.
A cikin wata sanarwa, Jonathan da wasu shugabannin Afirka sun yi Allah-wadai da juyin mulkin.
“Mun yi Allah-wadai da wannan yunƙuri na daƙile tsarin dimokuraɗiyya, kuma muna kira ga Tarayyar Afirka da ECOWAS su ɗauki matakin dawo da tsarin mulki,” in ji su.
Sun buƙaci mutanen Guinea-Bissau su kwantar da hankalinsu, tare da kira ga sojoji su saki dukkanin jami’an da suka kama domin a ci gaba da gudanar da zaɓe cikin lumana.