Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina
Published: 13th, March 2025 GMT
Majalisar dokokin jihar Kano ta wanke Arc. Ibrahim Yakubu Adamu a matsayin kwamishina kuma mamba a majalisar zartarwa ta jiha.
A yayin aikin tantance kwamishinonin, ya jaddada mahimmancin kiyaye babban tsarin ga birane da yankunan karkara.
Ya kuma yi alkawarin bayar da gudunmowarsa wajen sauke nauyin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dora masa.
Adamu wanda a baya ya taba rike mukamin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tsare-Tsare Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), ya bayyana jin dadinsa ga majalisar a yayin zaman majalisar.
Shugaban majalisar Jibril Ismail Falgore ya bukaci Adamu da ya kara samun nasarori a KNUPDA tare da yi masa fatan Alheri a sabon mukaminsa.
Nadin Adamu ya yi daidai da ikon da tsarin mulki na Gwamna Yusuf ya ba shi na nada ‘yan majalisar zartarwa ta jiha.
KHADIJAH ALIYU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwashina
এছাড়াও পড়ুন:
An rufe duk makarantu a Kebbi
Gwamnatin Jihar Kebbi ta ba da umarnin rufe dukkan makarantun sakandire na gwamnati da na masu zaman kansu nan take.
Haka kuma, gwamnatin ta rufe dukkan manyan makarantun gaba da sakandire a faɗin jihar, banda Kwalejin Nazarin Aikin Jinya da Ungozoma da ke Birnin Kebbi.
An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin NajeriyaWannan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Ilimi na manyan makarantu, Alhaji Issa Abubakar-Tunga, tare da Kwamishiyar Ilimin Firamare da Sakandare, Dokta Halima Bande, suka fitar a Birnin Kebbi, ranar Lahadi.
Sanarwar ta ce an ɗauki wannan mataki ne sakamakon barazanar hare-haren da ake samu a wasu sassan jihar a kwanakin nan.
Manyan makarantu da abin ya shafa sun haɗa da Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Dakingari, Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Kebbi (KSUSTA) da ke Aliero, Kwalejin Kiwon Lafiya ta Jega, da kuma Kwalejin Ilimi ta Argungu.
Sanarwar ta ce Kwalejin Nazarin Aikin Jinya da Ungozoma da ke Birnin Kebbi ba ta cikin jerin makarantun da aka rufe.
Gwamnati ta buƙaci hukumomin dukkan makarantun da su yi wa wannan umarni biyayya, tare da kwantar da hankalin al’umma, tana mai bayyana cewa nan gaba kaɗan za a ayyana ranar komawa makarantun da zarar komai ya daidaita.
Aminiya ta ruwaito yadda a bayan nan jihohi da dama musamman a Arewacin suka bayar da umarnin rufe makarantu saboda fargabar matsalar tsaro da ake ci gaba da samu a kwanakin nan.
Wasu daga cikin jihohin da suka rufe makarantu sun haɗa da Kwara, Neja, Katsina, Taraba, Yobe da kuma Filato.
Wannan dai na zuwa ne bayan ’yan bindiga sun sace ɗalibai 25 a wata Makarantar Sakandire ta Maga da ke Jihar Kebbi.
Sai kuma harin da aka samu a wani coci da ke Jihar Kwara da kuma sace fiye da ɗalibai 300 da ’yan ta’adda suka yi a wata makarantar St Mary da ke Jihar Neja.