Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-18@16:15:51 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina

Published: 13th, March 2025 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina

Majalisar dokokin jihar Kano ta wanke Arc. Ibrahim Yakubu Adamu a matsayin kwamishina kuma mamba a majalisar zartarwa ta jiha.

 

 

A yayin aikin tantance kwamishinonin, ya jaddada mahimmancin kiyaye babban tsarin ga birane da yankunan karkara.

 

Ya kuma yi alkawarin bayar da gudunmowarsa wajen sauke nauyin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dora masa.

 

Adamu wanda a baya ya taba rike mukamin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tsare-Tsare Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), ya bayyana jin dadinsa ga majalisar a yayin zaman majalisar.

 

Shugaban majalisar Jibril Ismail Falgore ya bukaci Adamu da ya kara samun nasarori a KNUPDA tare da yi masa fatan Alheri a sabon mukaminsa.

 

Nadin Adamu ya yi daidai da ikon da tsarin mulki na Gwamna Yusuf ya ba shi na nada ‘yan majalisar zartarwa ta jiha.

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwashina

এছাড়াও পড়ুন:

Birtaniya Ta Fitar Da Sabbin Tsauraran Dokokin Zama A Ƙasar

Hukumomin kasar za su fitar da gamsasshen bayani mai dauke da sababbin tsauraran matakan, wadanda za su kunshi na mallakar izinin karatu da aiki a Birtaniya.

Sakataren harkokin baki na Birtaniya Ybette Cooper ta bayyana wa BBC cewa lokaci ya yi da za su rage daukar ma’aikatan jinya daga kasashen waje.

Ta ce wannan matakin zai taimaka wajen rage kusan mutum 50,000 wadanda ba kwararru ba ne sosai da suke shiga kasar daga kasashen ketare a duk shekara.

Firaministan ya ce sababbin matakan za su taimaka wajen “sake mallake bakin iyakokin kasarmu.”

Idan aka dabbaka sabbin matakan nan da gwamnatin kasar za ta dauka, ‘yan kasashen mutane daga kasashen Nijeriya da Pakistan da Sri Lanka za su fuskanci kalubale wajen samun izinin shiga kasar Birtaniya domin karatu.

Abin da hakan ke nufi

Starmer ya ce Birtaniya za ta rika neman wadanda suka fi kwarewa ne a duniya wajen daukar aiki, sannan za su bincika me ya sa wani bangaren aikin kasar ya fi mayar da hanakali kan “neman sauki wajen daukar aiki.”

Firaministan ya ce sabbin matakan za su fayyace komai da komai game da tsare-tsaren shige da fice a kasar – iyali da karatu da aiki.

“Zan tabbatar da matakan nan saboda za su tabbatar da adalci, kuma abin da ya dace ke nan,” in ji Starmer a wani taron manema labarai.

Ya ce bai kamata a rika mayar da hankali kan neman sauki wajen daukar ma’aikata ba, maimakon mayar da hankali kan horar da matasan kasar.

Starmer ya kara da cewa bakin da suke shigowa kasar a gwamnatin baya sun kai kusan miliyan 1 a shekarar 2023, wanda shi ne adadi mafi yawa.

Ya ce adadin bakin ya kai adadin mutanen birnin Birmingham baki daya, wanda kuma shi ne birni na biyu mafi girma a Birtaniya.

“Wannan ba ci gaba ba ne, kasada ce. Ba zai yiwu a ce da kuskure hakan ya faru ba, wannan ganganci aka yi.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Birtaniya Ta Fitar Da Sabbin Tsauraran Dokokin Zama A Ƙasar
  • Gwamnatin Kano ta haramta ‘Ƙauyawa Day’ a lokacin bikin aure
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara
  • Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas
  • A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC
  • Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce Amurka Tana Da Hannu Dumu-Dumu A Kisan Kiyashin Gaza
  • Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025
  • Ganduje ya halarci Majalisar Wakilai don sheda ’Yan Majalisa 2 zuwa APC