Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-22@13:29:52 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina

Published: 13th, March 2025 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina

Majalisar dokokin jihar Kano ta wanke Arc. Ibrahim Yakubu Adamu a matsayin kwamishina kuma mamba a majalisar zartarwa ta jiha.

 

 

A yayin aikin tantance kwamishinonin, ya jaddada mahimmancin kiyaye babban tsarin ga birane da yankunan karkara.

 

Ya kuma yi alkawarin bayar da gudunmowarsa wajen sauke nauyin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dora masa.

 

Adamu wanda a baya ya taba rike mukamin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tsare-Tsare Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), ya bayyana jin dadinsa ga majalisar a yayin zaman majalisar.

 

Shugaban majalisar Jibril Ismail Falgore ya bukaci Adamu da ya kara samun nasarori a KNUPDA tare da yi masa fatan Alheri a sabon mukaminsa.

 

Nadin Adamu ya yi daidai da ikon da tsarin mulki na Gwamna Yusuf ya ba shi na nada ‘yan majalisar zartarwa ta jiha.

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwashina

এছাড়াও পড়ুন:

Iyalan Waɗanda Aka Kashe Yayin Zanga-zangar Bangladesh Sun Yi Maraba Da hukuncin Kisan Tsohuwar Firaminstar

Iyalai da ‘yan uwan wadanda aka kashe a lokacin zanga-zangar da ta kawo karshen gwamnatin tsohuwar Firaminstar Bangaledash Sheikh Hasina a bara, sun yi maraba da hukuncin kisa da wata kotun birnin Dhaka ta yanke mata.

An samu Sheikh Hasina da laifin cin zarafin bil adama tare da ba ‘yan sanda umurnin kashe masu zanga-zanga, inda aka yanke mata hukuncin a bayan idonta.

Gwamnatin Bangaledash ta bukaci Indiya da ta tasa keyar Hasina da ke gudun hijira a can domin ta fuskanci hukuncin.

Wakiliyar BBC ta ce  Hukumomin Indiya na cewa suna ci gaba da bibiyar lamarin tsakanin Sheikh Hasina da mahukuntan Bangaledash kuma hakan na nufin Indiya na neman wata hanyar diflomasiyya akan lamarin.

 

BBC

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yan Majalisar Dokokin Amurka Sun Sami Rarrabuwar Kai Dangane Da ‘Keshe Kiristoci A Najeriya’
  • Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa
  • Sojoji sun bar makarantar Maga kafin ’yan bindiga su kai hari — Gwamna Kebbi 
  • Zargi: Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • Jihar Jigawa Ta Amince da Naira Biliyan 3.5 a Matsayin Kudaden Tallafin UBEC 2025
  • Iyalan Waɗanda Aka Kashe Yayin Zanga-zangar Bangladesh Sun Yi Maraba Da hukuncin Kisan Tsohuwar Firaminstar
  • Gwamna Abba Kabir Zai Gabatar Da Kudirin Kafin 2026 Ga Majalisar Kano Ranar Laraba
  • Gwamna Abba ya gabatar da N1.36trn a matsayin kasafin 2026
  • Gwamna Abba ya gabatar da kasafin 2026 na N1.36trn