Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina
Published: 13th, March 2025 GMT
Majalisar dokokin jihar Kano ta wanke Arc. Ibrahim Yakubu Adamu a matsayin kwamishina kuma mamba a majalisar zartarwa ta jiha.
A yayin aikin tantance kwamishinonin, ya jaddada mahimmancin kiyaye babban tsarin ga birane da yankunan karkara.
Ya kuma yi alkawarin bayar da gudunmowarsa wajen sauke nauyin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dora masa.
Adamu wanda a baya ya taba rike mukamin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tsare-Tsare Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), ya bayyana jin dadinsa ga majalisar a yayin zaman majalisar.
Shugaban majalisar Jibril Ismail Falgore ya bukaci Adamu da ya kara samun nasarori a KNUPDA tare da yi masa fatan Alheri a sabon mukaminsa.
Nadin Adamu ya yi daidai da ikon da tsarin mulki na Gwamna Yusuf ya ba shi na nada ‘yan majalisar zartarwa ta jiha.
KHADIJAH ALIYU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwashina
এছাড়াও পড়ুন:
Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano
Wani jirgin sama mallakin kamfanin Flybird, ya yi hatsari yayin sauka a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano.
Jirgin ya taso daga Abuja, kuma lamarin ya faru ne a lokacin da yake ƙoƙarin sauka a filin jirgin saman Kano, a ranar Lahadi.
Tsaro: Abba ya kafa runduna ta musamman da za ta ke tsaron tashoshin mota a Kano An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a OstireliyaMajiyoyi daga filin jirgin saman, sun bayyana cewa babu wani fasinja ko ma’aikacin jirgin da ya ji rauni.
Wani jami’in filin jirgin ya shaida wa Aminiya, cewa hukumomin sufurin jiragen sama ko Hedikwatar Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Tarayya (FAAN) ne, kaɗai za su iya yin ƙarin bayani kan lamarin.
Wata majiya kuma ta tabbatar da cewa fasinjoji 11 ne ke cikin jirgin a lokacin da lamarin ya faru.