Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-15@03:20:54 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina

Published: 13th, March 2025 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina

Majalisar dokokin jihar Kano ta wanke Arc. Ibrahim Yakubu Adamu a matsayin kwamishina kuma mamba a majalisar zartarwa ta jiha.

 

 

A yayin aikin tantance kwamishinonin, ya jaddada mahimmancin kiyaye babban tsarin ga birane da yankunan karkara.

 

Ya kuma yi alkawarin bayar da gudunmowarsa wajen sauke nauyin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dora masa.

 

Adamu wanda a baya ya taba rike mukamin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tsare-Tsare Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), ya bayyana jin dadinsa ga majalisar a yayin zaman majalisar.

 

Shugaban majalisar Jibril Ismail Falgore ya bukaci Adamu da ya kara samun nasarori a KNUPDA tare da yi masa fatan Alheri a sabon mukaminsa.

 

Nadin Adamu ya yi daidai da ikon da tsarin mulki na Gwamna Yusuf ya ba shi na nada ‘yan majalisar zartarwa ta jiha.

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwashina

এছাড়াও পড়ুন:

Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano

Wani jirgin sama mallakin kamfanin Flybird, ya yi hatsari yayin sauka a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano.

Jirgin ya taso daga Abuja, kuma lamarin ya faru ne a lokacin da yake ƙoƙarin sauka a filin jirgin saman Kano, a ranar Lahadi.

Tsaro: Abba ya kafa runduna ta musamman da za ta ke tsaron tashoshin mota a Kano An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 

Majiyoyi daga filin jirgin saman, sun bayyana cewa babu wani fasinja ko ma’aikacin jirgin da ya ji rauni.

Wani jami’in filin jirgin ya shaida wa Aminiya, cewa hukumomin sufurin jiragen sama ko Hedikwatar Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Tarayya (FAAN) ne, kaɗai za su iya yin ƙarin bayani kan lamarin.

Wata majiya kuma ta tabbatar da cewa fasinjoji 11 ne ke cikin jirgin a lokacin da lamarin ya faru.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano
  • Shuwagabannin Majalisar Kasar Iran Da Na Ethiopia Sun Gudanar Da Taron Manema Labarai
  • Shirin kafa ‘Hisbar Ganduje’ ya tayar da ƙura a Kano
  • Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara
  • Farfesa na Farko a fannin Ilimi a Arewa, Adamu Baikie, ya rasu yana da shekara 94
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano