Sanarwar ta ƙara da cewa, tawagar ta Zamfara ta yi hulɗa da kamfanonin Zhong Zhao International Group, Phoenix Wings, Shenzhen HighGreat Innovation Technology Development Co., Ltd, da Xiamen Magnetic North Technology Co., Ltd yayin da suke ƙasar Sin.

 

Tang Zhangwei, ya jagoranci wasu kamfanoni zuwa jihar Zamfara, domin ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu a sassa masu muhimmanci, domin bunƙasa tattalin arziki.

 

A nasa jawabin, gwamna Lawal ya yaba da ƙoƙarin da kamfanonin ƙasar Sin ke yi na tabbatar da nasarar haɗin gwiwarsu.

 

“Ina so in yi muku barka da zuwa Jihar Zamfara. Muna maraba da ku. A watan Fabrairu, na jagoranci wata tawaga zuwa ƙasar Sin don ganawa da kamfanoni a sassa daban-daban da kuma gano ci gaban da za su samar. Tafiya ce mai tasirin gaske.

 

“Mun yi haɗin gwiwa da kamfanin ƙasa da ƙasa na Zhong Zhao, wanda ya kware a fannin takin zamani da noman zamani. Suna mai da hankali kan samar da takin gargajiya da fasahar kiwo na R&D. Mun rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna domin horar da manoman gida sana’o’in noma, ta hanyar amfani da injina da fasahar zamani wajen kafa masana’antar takin zamani a jihar Zamfara.

 

“Tawagar Zamfara ta yi hafin gwiwa da kamfanin Phoenix Wings, wani kamfanin ƙasar Sin da ya ƙware kan fasahar sa ido kan tsaro, gami da jirage marasa matuƙa. A tare, za su bullo da dabarun samar da ingantattun tsare-tsare na magance matsalar ‘yan bindiga, garkuwa da mutane, da ƙalubalen tsaro a jihar Zamfara.

 

“A taronmu da kamfanin Shenzhen HighGreat Innovation Technology Development Co., Ltd, mun tattauna batun ƙirƙire-ƙirƙire, samar da jirage marasa matuƙa da sauran fasahohi.

 

“Mun ɗauki nauyin kamfanonin Xiamen Magnetic North Technology Co., Ltd. da Xiamen King Long United Automobile Industry Co., Ltd. An gabatar da shawarwari don bunƙasa cibiyoyin sufuri na zamani da gabatar da tsarin zirga-zirgar jama’a don inganta sufuri a ciki da wajen jihar.

 

“Bugu da ƙari, mun yi taro mai nasara tare da kamfanin WEICAI LOVOL International Trading Company, wanda ke mai da hankali kan noman zamani, wanda a Turance ake kira ‘Smart Agriculture, ‘Integrated Management Platform’, da amfanin da injinan noma.

 

“Tawagar Zamfara ta gana da kamfanin Tibet Ming inda suka tattauna batun ƙara zuba jari a harkar haƙar ma’adanai, da jaddada ayyuka masu ɗorewa, ɗawainiyar jama’a, da fasahar zamani don bunƙasa haƙo ma’adinai a jihar Zamfara,” Inji Gwamna Lawal.

 

Tun da farko, sakataren gwamnatin jihar Zamfara, Malam Abubakar Nakwada, wanda ke cikin tawagar jihar a ƙasar Sin, ya bayyana nasarorin da suka samu a ziyarar aiki.

 

Ya ce, “Mun kai ziyarar aiki mai inganci a ƙasar Sin, kuma sakamakon ya bayyana a yau bayan da wasu manyan kamfanoni suka zo jihar Zamfara.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Matashi ya rasu yayin rikici a wajen radin suna a Bauchi

Wani matashi mai shekaru 20, Haruna Haruna, ya rasa ransa bayan fada ya barke a lokacin bikin radin suna a ƙauyen Kwata da ke Karamar Hukumar Warji ta Jihar Bauchi.

Bayanai sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata lokacin da sa’insa ta barke tsakanin wasu matasa ta rikide ta zama fada, wanda ya bar Haruna cikin rashin hayyacinsa.

Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa

“Wani matashi mai shekaru 20, Haruna Haruna na ƙauyen Kwata, Karamar Hukumar Warji, Jihar Bauchi, ya riga mu gidan gaskiya bayan rikici mai tsanani da ya barke a bikin radin suna a ranar 2 ga watan Disamba, 2025,” in ji Zagazola Makama, masani kan harkokin tsaro a yankin arewa maso gabas.

Ya kara da cewa rashin jituwa tsakanin wasu matasa a wajen bikin ta rikide zuwa fada, lamarin da ya bar wanda abin ya shafa ya suma nan take.

An ce an garzaya da Haruna zuwa Asibitin Gwamnati na Warji, amma ya rasu a yayin da ake masa jinya.

Da aka tuntubi mai magana da yawun ’yan sanda na jihar, Ahmed Wakili, ya ce yana cikin taro kuma ya yi alƙawarin dawowa da bayani, sai dai bai yi hakan ba har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi
  • Matashi ya rasu yayin rikici a wajen radin suna a Bauchi
  • Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale
  •  An Kira Yi Gwamnatin Canada Da Ta Kama Olmert Da Livini Na “Isra’ila
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja
  • Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta