Aminiya:
2025-11-21@02:16:00 GMT

Natasha ta yi ƙarar Akpabio a Majalisar Dinkin Duniya

Published: 12th, March 2025 GMT

Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya da aka dakatar, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta yi ƙarar Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Godswill Akpabio a Majalisar Ɗinkin Duniya.

Ta gabatar da kokenta a zaman taron mata da aka gudanar a hedikwatar Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) a birnin New York, inda ta nemi ƙungiyoyin kare dimokuraɗiyya na duniya su bi mata haƙƙinta.

Majalisar Wakilai ta ba da umarnin rufe shafukan intanet na batsa Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet

Natasha, ta ce dakatar da ita daga Majalisar Dattawan Nijeriya da aka yi ba bisa ƙa’ida ba ne, kuma ta nuna damuwa kan cewa za a iya ƙoƙarin tsare ta saboda yin magana a fili.

Taƙaddamar da ke tsakanin Sanata Natasha da Sanata Akpabio ta ƙara tsanani bayan rigimar sauya mata wajen zama a zauren majalisa da ta faru a ranar 20 ga watan Fabrairu, 2025.

Ta zargi Akpabio da cin zarafinta da kuma amfani da muƙaminsa ta hanyar da ba ta dace ba, zarge-zargen da duk ya musanta.

Bayan lamarin ya yi ƙamari, Natasha ta maka Akpabio a kotu kan zargin ɓatanci, tana neman diyyar Naira biliyan 100.

A makon da ya gabata ne dai Majalisar Dattawan ta sanar da dakatar da Sanata Natasha Uduaghan tsawon watanni shida bayan kwamitin ladabtarwa na majalisar ya zarge ta da karya wasu daga cikin dokokinta.

Kwamitin ya yi zargin cewa Sanata Natasha ta yi magana ba tare da izini ba, kuma ta ƙi komawa sabon wurin zaman da aka sauya mata a zauren majalisar.

Har ila yau, an dakatar da albashinta da sauran haƙƙoƙinta na kuɗaɗe har tsawon lokacin dakatarwar, kuma an hana ta gabatar da kanta a matsayin Sanata.

Dambarwar Natasha da Akpabio na ci gaba da ɗaukar hankali a ciki da wajen Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakatarwa Ƙara Majalisar Dattawa Majalisar Ɗinkin Duniya a Majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Ribadu Ya Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Amurka Kan Zargin Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan sha’anin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya jagoranci manyan jami’an Gwamnatin Nijeriya zuwa Amurka don tattaunawa game da zargin kisan ƙare dangi da ake yi wa Kiristoci.

Lamarin ya samo asali ne bayan Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima ya goyi bayan kafa ƙasashe biyu na Isra’ila da Gaza.

A farkon watan nan, Shugaba Donald Trump na Amurka ya yi barazanar daukar matakin soji a kan Nijeriya, kuma ya bukaci ‘yan majalisar dokokin kasar, ciki har da dan majalisa Riley Moore, su binciki lamarin.

Ko da yake Nijeriya ta karyata ikirarin, amma Amurka ta ci gaba da jadadda zargin kisan Kiristoci.

A ranar Talata, mawakiyar Amurka, Nicki Minaj a zauren Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi magana a kan zargin cin zarafin Kiristoci a Nijeriya.

Tawagar Nijeriya, wacce ta haɗa da manyan jami’ai kamar Bianca Ojukwu, Kayode Egbetokun, da Lateef Fagbemi, sun gana da Moore don bayyana ƙalubalen tsaro, yaƙi da ta’addanci, da kare al’ummar ƙasar.

Moore, ya ce tattaunawar “ta kasance ta gaskiya, kuma mai amfani” kuma ya jaddada cewa Amurka na son ganin an dauki matakai don kare Kiristoci daga tashin hankali da ta’addanci.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hukumar Kula Da Jiragen Sama Ta Najeriya Ta ci Tarar Kamfanin Jiragen Sama Na Qatar November 20, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Kara Dagulewar Al’amura Bayan Harin Isra’ila A Gaza November 20, 2025 Labanon Ta Bukaci Gudanar Da Taron Kwamitin Tsaro Na MDD Cikin Gaggawa November 20, 2025 Achraf Hakimi Ya Zama Gwarzon Wasan Kwallon Kafar Afirka Na Shekara Ta 2025 November 20, 2025 Kasashen Iran Da Malesiya Sun Rattaba Hannu Kan Jarjejeniyar Fadada Dangantakar Addini November 20, 2025 Isra’ila ta kashe akalla Falasdinawa 27 a wani sabon harin bam November 20, 2025 Iran : daftarin kudurin da Canada ta gabatar, siyasa ce da kin jininmu November 20, 2025 AU ta yi Allah-wadai da tsoma bakin kasashen waje a harkokin tsaron Afirka November 20, 2025 Amurka ta Shawarci Ukraine ta amince da yankunan da Rasha ta mamaye mata November 20, 2025 Sudan ta yaba da kokarin Amurka da Saudiyya na kawo karshen rikicin kasar November 20, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu wani addini da matsalar tsaron Nijeriya ta ƙyale — Fafaroma
  • Ribadu Ya Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Amurka Kan Zargin Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla
  • Iran : daftarin kudurin da Canada ta gabatar, siyasa kawai da kin jinin Iran
  • Wardley ya zama zakaran damben boksin na duniya
  • Cibiyar fasaha ta kaddamar da shirin bunkasa tattalin arzikin ’yan kasuwa mata a Jihohi 3
  • Sanatan Enugu ya mutu a Birtaniya
  • Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
  • Gwamnan Taraba ya dakatar da ficewa daga PDP saboda sace ɗalibai a Kebbi
  • Nijar: An Dakatar Da Ayyukan Kungiyoyin Agaji Da Dama
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai mata a Kebbi