Natasha ta yi ƙarar Akpabio a Majalisar Dinkin Duniya
Published: 12th, March 2025 GMT
Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya da aka dakatar, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta yi ƙarar Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Godswill Akpabio a Majalisar Ɗinkin Duniya.
Ta gabatar da kokenta a zaman taron mata da aka gudanar a hedikwatar Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) a birnin New York, inda ta nemi ƙungiyoyin kare dimokuraɗiyya na duniya su bi mata haƙƙinta.
Natasha, ta ce dakatar da ita daga Majalisar Dattawan Nijeriya da aka yi ba bisa ƙa’ida ba ne, kuma ta nuna damuwa kan cewa za a iya ƙoƙarin tsare ta saboda yin magana a fili.
Taƙaddamar da ke tsakanin Sanata Natasha da Sanata Akpabio ta ƙara tsanani bayan rigimar sauya mata wajen zama a zauren majalisa da ta faru a ranar 20 ga watan Fabrairu, 2025.
Ta zargi Akpabio da cin zarafinta da kuma amfani da muƙaminsa ta hanyar da ba ta dace ba, zarge-zargen da duk ya musanta.
Bayan lamarin ya yi ƙamari, Natasha ta maka Akpabio a kotu kan zargin ɓatanci, tana neman diyyar Naira biliyan 100.
A makon da ya gabata ne dai Majalisar Dattawan ta sanar da dakatar da Sanata Natasha Uduaghan tsawon watanni shida bayan kwamitin ladabtarwa na majalisar ya zarge ta da karya wasu daga cikin dokokinta.
Kwamitin ya yi zargin cewa Sanata Natasha ta yi magana ba tare da izini ba, kuma ta ƙi komawa sabon wurin zaman da aka sauya mata a zauren majalisar.
Har ila yau, an dakatar da albashinta da sauran haƙƙoƙinta na kuɗaɗe har tsawon lokacin dakatarwar, kuma an hana ta gabatar da kanta a matsayin Sanata.
Dambarwar Natasha da Akpabio na ci gaba da ɗaukar hankali a ciki da wajen Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: dakatarwa Ƙara Majalisar Dattawa Majalisar Ɗinkin Duniya a Majalisar
এছাড়াও পড়ুন:
Dauda Lawal: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba
Baya ga haka, sabon ginin ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta Jihar Zamfara da aka sake ginawa da kuma sabon ginin kwalejin fasaha da kimiyya na Jihar Zamfara (ZACAS) da aka gyara, sun yi matuƙar haskaka Gwamnatin Dauda Lawal.
Har ila yau, jihar ta samu gagarumin ci gaba wajen inganta fannin kiwon lafiya ta hanyar zuba jari, wajen gyarawa da inganta asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a faɗin jihar.
A ƙoƙarinsa na rage mace-macen mata masu juna biyu da mace-macen jarirai, an ɗauki ma’aikatan kiwon lafiya tare da horar da su da sayen magunguna da kayan aiki da ɓullo da ayyukan kula da lafiyar mata da ƙananan yara kyauta.
Sannan, an gyara asibitin ƙwararru na Yeriman Bakura tare da samar da kayan aiki na zamani. Haka kuma an gyara tare da samar da kayan aiki ga babban asibitin da ke Ƙaramar Hukumar Kauran Namoda a jihar. Babban asibitin da ke Kauran Namoda da sauran al’ummomin da ke makwabtaka da shi, an samar da kayan aiki don isar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya yadda ya kamata. Kazalika, an sanya na’urorin bincike, gadaje, injinan ECG, injin centrifuge, injinan gwaje-gwajen jini, na’urar tantance jini ta atomatik da sauran wasu kayan aiki.
Kazalika, an kuma inganta babban asibitin Nasarawar Burkullu da ke Ƙaramar Hukumar Bukkuyum. Bayan ayyukan kiwon lafiya da suka haɗa da na gaggawa, aikin tiyata, kula da lafiyar mata da yara, tsarin wurin keɓewa, wurin ajiyar gawa, ɗakunan tiyata na maza da mata, GOPD, ɗakin gwaje-gwaje, shagon magani, kula da mata masu juna biyu da kula da yar, duk an gina su. Sauran gyare-gyaren, sun haɗa da shingen gudanarwa, wuraren ma’aikata, masallatai da rijiyoyin burtsatse.
Haka kuma, a Ƙaramar Hukumar Maru, an gyara babban asibitin tare da samar da kayan aiki na zamani.
Gwamnan ya kuma kaƙƙamar da aikin sabunta birane, wanda ya kai ga gyara manyan tituna a jihar.
Dangane da batun tsaro kuwa, a shekarun baya-bayan nan, Zamfara ta ɗan samu jinkiri. A wannan lokaci na Gwamna Lawal, kashe-kashe da garkuwa da mutane ya ragu matuƙa a jihar. Hakan ya biyo bayan kafa jami’an tsaron da aka kafa a dukkanin kananan hukumomi 14 na Jihar Zamfara.
An horar da mutanen da aka zaɓo a tsanake, bisa cikakkiyar kulawar jami’an tsaron hukumar DSS, sannan suna yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro na yau da kullum, domin yaƙi da ‘yan fashi a jihar. A kwanakin baya ne gwamnan ya raba motocin aiki guda 140 da aka ware wa ƙungiyoyin tsaro daban-daban a faɗin jihar.
An haifi Dauda Lawal Dare, a ranar 2 ga Satumbar 1965, a Jihar Zamfara. Bayan kammala karatunsa na Firamare da Sakandare, ya halarci Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, inda ya yi digirinsa na farko a fannin Kimiyyar Siyasa. Ya kuma yi digirinsa na biyu (M.Sc) a fannin kimiyyar siyasa/Hukunce-hukuncen ƙasa da ƙasa duk a jami’ar. Ya ƙara da digirin-digirgir (PhD) a fannin harkokin kasuwanci a jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato.
Bayan kammala karatunsa na digiri na uku, ya yi kwasa-kwasai a Makarantar Kasuwanci ta Harɓard, Makarantar Kasuwanci ta Jami’ar Oɗford, Makarantar Tattalin Arziƙi ta Landan, Makarantar Kasuwancin Legas da sauransu.
Gwamnan ya yi aiki a matsayin jami’in ilimin siyasa tare da MAMSER, hukumar wayar da kan jama’a, don tabbatar da adalci da dogaro da kai a Nijeriya. A 1989, ya shiga Westeɗ Nigeria Limited a matsayin mataimakin babban manaja.
An naɗa shi a matsayin mataimakin ƙaramin jami’in shige da fice (immigration), a shekarar 1994, sannan ya zama babban jami’in hulɗa da jama’a a ofishin Jakadancin Nijeriya, Washington, DC, Amurka.
A shekarar 2003, ya koma bankin First Bank, a matsayin manajan hulɗa da jama’a, kuma a lokuta daban-daban ya kasance babban manaja a ofishin Abuja. A shekarar 2011, ya samu muƙamin mataimakin shugaban zartaswa, sashen gwamnati na Arewa na bankin na First Bank, bayan ya yi ayyuka da dama. A shekarar 2012, Dauda Lawal ya zama babban darakta a sashen gwamnati na Arewa, na First Bank.
Daga baya ya shiga siyasa ya kuma tsaya takarar Gwamnan Jihar Zamfara. A zaɓen fidda gwani na APC da aka gudanar a shekarar 2018, ya sha kaye a hannun Idris Shehu Mukhtar. A zaben Gwamnan Jihar Zamfara na 2023, ya tsaya takara; kuma ya yi nasara a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA