Aminiya:
2025-11-26@17:40:16 GMT

Natasha ta yi ƙarar Akpabio a Majalisar Dinkin Duniya

Published: 12th, March 2025 GMT

Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya da aka dakatar, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta yi ƙarar Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Godswill Akpabio a Majalisar Ɗinkin Duniya.

Ta gabatar da kokenta a zaman taron mata da aka gudanar a hedikwatar Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) a birnin New York, inda ta nemi ƙungiyoyin kare dimokuraɗiyya na duniya su bi mata haƙƙinta.

Majalisar Wakilai ta ba da umarnin rufe shafukan intanet na batsa Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet

Natasha, ta ce dakatar da ita daga Majalisar Dattawan Nijeriya da aka yi ba bisa ƙa’ida ba ne, kuma ta nuna damuwa kan cewa za a iya ƙoƙarin tsare ta saboda yin magana a fili.

Taƙaddamar da ke tsakanin Sanata Natasha da Sanata Akpabio ta ƙara tsanani bayan rigimar sauya mata wajen zama a zauren majalisa da ta faru a ranar 20 ga watan Fabrairu, 2025.

Ta zargi Akpabio da cin zarafinta da kuma amfani da muƙaminsa ta hanyar da ba ta dace ba, zarge-zargen da duk ya musanta.

Bayan lamarin ya yi ƙamari, Natasha ta maka Akpabio a kotu kan zargin ɓatanci, tana neman diyyar Naira biliyan 100.

A makon da ya gabata ne dai Majalisar Dattawan ta sanar da dakatar da Sanata Natasha Uduaghan tsawon watanni shida bayan kwamitin ladabtarwa na majalisar ya zarge ta da karya wasu daga cikin dokokinta.

Kwamitin ya yi zargin cewa Sanata Natasha ta yi magana ba tare da izini ba, kuma ta ƙi komawa sabon wurin zaman da aka sauya mata a zauren majalisar.

Har ila yau, an dakatar da albashinta da sauran haƙƙoƙinta na kuɗaɗe har tsawon lokacin dakatarwar, kuma an hana ta gabatar da kanta a matsayin Sanata.

Dambarwar Natasha da Akpabio na ci gaba da ɗaukar hankali a ciki da wajen Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakatarwa Ƙara Majalisar Dattawa Majalisar Ɗinkin Duniya a Majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu

Yan Majalisar Tarayya daga yankin Kudu sun yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi wa jagoran ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, afuwa bayan da kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.

Kungiyar ’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu maso Gabas ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya yi amfani da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi, wajen yi wa Nnamdi Kanu afuwa wanda kotu ta same shi da laifin ta’addanci.

Alƙali James Omotosho na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ne ya yanke hukuncin, inda ya same shi da laifi a kan tuhumar da ake masa guda bakwai, sannan ya yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

Tuni aka tura Nnamdi Kanu zuwa gidan yari a Jihar Sakkwato inda yake zaman waƙafi.

A cikin sanarwa bayan taron gaggawa da suka gudanar a Abuja, ’yan majalisar sun ce duk da cewa suna girmama kotu da tsarin shari’a, lamarin ya rikiɗe zuwa matsalar ƙasa mai tasiri ga rayuwar jama’a, tattalin arziki da tsaro.

Da yake karanta sanarwar, Hon. Iduma Igariwey ya ce yin afuwa zai taimaka wajen rage tashin hankali da dawo da zaman lafiya a yankin.

Sun lissafa dalilai guda huɗu da suka sa suka yi wannan kira.

Dalilan da suke bayyana su ne ƙaruwa da rashin tsaro da tashin hankali da ke da alaƙa da tsare Kanu; Wahalar rayuwa da tattalin arziki da jama’a ke fuskanta da kuma buƙatar shugabanci mai tausayawa wajen shawo kan matsalolin ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • Mali: An Dakatar Da  Aikin Kafafen Watsa Labarun Faransa Biyu A Cikin Kasar Mali
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin
  • Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro
  • Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno
  • Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno
  • Tinubu ya dakatar da ’yan sanda daga tsaron manyan mutane a Najeriya