Aminiya:
2025-12-14@18:00:11 GMT

Natasha ta yi ƙarar Akpabio a Majalisar Dinkin Duniya

Published: 12th, March 2025 GMT

Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya da aka dakatar, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta yi ƙarar Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Godswill Akpabio a Majalisar Ɗinkin Duniya.

Ta gabatar da kokenta a zaman taron mata da aka gudanar a hedikwatar Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) a birnin New York, inda ta nemi ƙungiyoyin kare dimokuraɗiyya na duniya su bi mata haƙƙinta.

Majalisar Wakilai ta ba da umarnin rufe shafukan intanet na batsa Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet

Natasha, ta ce dakatar da ita daga Majalisar Dattawan Nijeriya da aka yi ba bisa ƙa’ida ba ne, kuma ta nuna damuwa kan cewa za a iya ƙoƙarin tsare ta saboda yin magana a fili.

Taƙaddamar da ke tsakanin Sanata Natasha da Sanata Akpabio ta ƙara tsanani bayan rigimar sauya mata wajen zama a zauren majalisa da ta faru a ranar 20 ga watan Fabrairu, 2025.

Ta zargi Akpabio da cin zarafinta da kuma amfani da muƙaminsa ta hanyar da ba ta dace ba, zarge-zargen da duk ya musanta.

Bayan lamarin ya yi ƙamari, Natasha ta maka Akpabio a kotu kan zargin ɓatanci, tana neman diyyar Naira biliyan 100.

A makon da ya gabata ne dai Majalisar Dattawan ta sanar da dakatar da Sanata Natasha Uduaghan tsawon watanni shida bayan kwamitin ladabtarwa na majalisar ya zarge ta da karya wasu daga cikin dokokinta.

Kwamitin ya yi zargin cewa Sanata Natasha ta yi magana ba tare da izini ba, kuma ta ƙi komawa sabon wurin zaman da aka sauya mata a zauren majalisar.

Har ila yau, an dakatar da albashinta da sauran haƙƙoƙinta na kuɗaɗe har tsawon lokacin dakatarwar, kuma an hana ta gabatar da kanta a matsayin Sanata.

Dambarwar Natasha da Akpabio na ci gaba da ɗaukar hankali a ciki da wajen Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakatarwa Ƙara Majalisar Dattawa Majalisar Ɗinkin Duniya a Majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno

Wani kwalekwale da ke ɗauke da fasinjoji takwas ya kife yayin da yake ƙetare kogin da ke kan iyaka da garin Gamboru na Najeriya da Fotokol a ƙasar Kamaru, inda mutane uku suka mutu.

Lamarin ya faru ne da misalin qarfe 6:30 na yamma lokacin da kwalekwalen, wanda wani Mamman Nur Abbagana na Kasuwan Katako, Gamboru ke tuƙa shi ya kife a tsakiyar ruwa tare da jefa dukkan fasinjoji cikin ruwa.

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa dukkan fasinjoji takwas ’yan ƙasar Chadi ne da ke tafiya daga Jos, Jihar Filato, a kan hanyarsu ta zuwa N’Djamena, Jamhuriyar Chadi.

An ceto fasinjoji biyar, waɗanda aka tabbatar da suna raye ba su mutu ba.

Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA

Wata mata mai suna Alphosine Makebu Beboroum, mai shekaru 34, da ’ya’yanta mata biyu Centich Mamajibe, mai shekaru 3, da Mamajilem Bebaroum, ‘yan watanni 10, sun nutse kuma har yanzu ba a gano su ba har zuwa Kammala wannan rahoto, duk da ana cigaba da gudanar da aikin ceto da bincike.

A halin yanzu, hukumomin ’yan sanda sun kuma tabbatar da kama mai tuƙa kwale-kwalen saboda karya umarnin gwamnatin Jihar Borno na tilasta wa duk masu aikin kwalekwale da su yi amfani da jakar ceto.

Kakakin rundunar ASP Nahum Kenneth Daso ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan musabbabin faruwar lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NEPC Ta Horas da Mata Kan Damar Kasuwancin Fitar da Kayayyaki Zuwa Kasashen Waje
  • An Fara Gyaran Tashar Talabijin Ta Jigawa Don Kara Mata Nisan Zango
  • Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara
  • Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani
  • Dantsoho Ya Yaba Wa Ƙoƙarin Oyetola Na Dawo Da Nijeriya Tsarin Sufurin Jiragen Ruwa Na Duniya
  • ’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno
  • Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita.
  • Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan
  • ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman