Aminiya:
2025-10-20@21:54:12 GMT

Majalisar Wakilai ta ba da umarnin rufe shafukan intanet na batsa

Published: 11th, March 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta bai wa Hukumar Sadarwa ta NCC umarnin rufe duk wasu shafukan intanet masu nuna batsa a Nijeriya.

Majalisar ta ba da wannan umarni yayin zamanta na yau Talata, inda ta nemi hukumar sadarwar ta umarci duk kamfanonin da ke samar da intanet su rufe duk wasu shafukan intanet da ke nuna hotuna ko bidiyon batsa cikin gaggawa.

Manyan makarantu sun shiga yajin aiki a Adamawa Sanƙarau ta kashe mutum 26 a Kebbi

Wannan umarni na zuwa ne bayan wani ƙudiri da ɗan majalisa daga Jihar Katsina, Dalhatu Shehu Tafoki, ya gabatar.

Tafoki ya bayyana cewa bidiyoyin batsa da ke intanet na zama babbar matsala a duniya, kuma zuwa yanzu Nijeriya ba ta ɗauki wani matakin magance matsalar ba.

Ya kafa hujjar cewa Nijeriya ƙasa ce mai addini, inda manyan addinan ƙasar suka haramta batsa da kuma nuna tsiraici.

Tafoki ya kuma bayyana gargaɗin da masana halayyar ɗan Adam suka yi kan mummunan tasirin da kallon bidiyon batsa ke da shi, ciki har da yiwuwar kusantar zina, da karuwanci, da kuma kasa rabuwa da kallon.

Majalisar ta kuma buƙaci hukumar NCC ta hukunta duk kamfanin samar da intanet da ya bijirewa wannan umarnin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai tsiraici

এছাড়াও পড়ুন:

JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

Shi ma a nasa jawabin yayin gudanar da taron, shugaban kwamitin Alhaji Abdullahi Abdulmalik Digi, ya ce, a shekaru hudu da ya yi yana jagorancin kwamitin sun yi abin da yakamata su yi, inda ya ce, a Azumin bara an dauki yara marayu 2000 da aka raba musu abinci da suka hada da buhunan shinkafa da kuma kayan Sallah da za su dinka, mata aka raba musu shadda mata kuma atamfofi inda jimillar kudin da aka kashe ya zama Naira miliyan 64.2.

 

Bayan wannan an kashe Naira milin 26 wajen biya wa yara 520 kudin makaranta, inda kowane yaro ake biya masa Naira dubu 50 a kananan hukumomi shida na FCT Abuja.

 

Sannan an kashe Naira miliyan 3 wajen taimakawa wasu da suka yi wa kwamitin hidima da suka rasu da kuma wadanda a yanzu ba su da lafiya, inda aka aika wa kowannensu Naira dubu hamsin-hamsin har gida.

 

Ya kara da cewa a wannan taro kuma, mata ne iyayen marayu su 120 aka koyawa sana’o’i, inda aka dauki kusana makonni uku ana koyar da su domin su samu ikon rike marayun da aka mutu aka bar musu. A wannan aiki na koyarwa an kashe Naira miliyan 4.675, a wurin sayen kayan aikin koyar da su da kuma zirga-zirga. Kananan hukumomin guda shida su ma sun kawo ta su gudunmawar ta Naira miliyan 2.4, suka idan an kammala basu horon kowacce a ba ta Naira 20,000 su rike kamar jari, jimillar kudin da kashe a wannan ba da horo na sati uku, ya kama Naira miliyan 7.75.

 

Jimillar abin da kwamitin ya kashe tun daga watan Azumin bara tun daga miliyan 66.2 kawo yanzu, an kashe Naira miliyan dari da dubu dariyu da saba’in da biyar N1.275 a shekarar bana kadai

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba October 18, 2025 Labarai Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano October 18, 2025 Manyan Labarai Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna October 18, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara
  •  Miliyoyin Mutanen Amurka Sun Yi Zanga-zanagr Nuna Kin Jinin Donald Trump
  • Gwamnati ta ɗauki matakin rage shan gishiri a Nijeriya
  • Isra’ila ta ce mashigar Rafah za ta ci gaba da kasancewa a rufe har sai abin da hali ya yi
  • Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
  • JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i
  • Rashin tsaro: An rufe makarantu sama da 180 a Arewa
  • Ma’aurata 136 sun kashe juna a shekara 4
  • Yadda ma’aurata 136 sun kashe juna a shekara 4
  • Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili