Aminiya:
2025-03-28@09:40:58 GMT

Tsohon shugaban Philippines ya faɗa komar ’yan sanda

Published: 11th, March 2025 GMT

’Yan sanda sun cafke tsohon shugaban ƙasar Philippines,  Rodrigo Duterte a filin jirgin saman birnin Manila a wannan Talatar.

Mista Duterte ya faɗa komar ’yan sandan ne bisa sammacin Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, jim kaɗan da saukarsa daga birnin Hong Kong.

Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet Ainihin abin da ke kawo wa Manchester United koma baya

Hatsaniya ta ɓarke a filin jirgin saman lokacin da ’yan sanda suka kama Mista Duterte, sakamakon tirjiya daga masu tsaron lafiyarsa da likitansa da kuma lauyoyinsa, wadanda ke zargin cewa an take masa haƙƙinsa da kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba shi.

Fadar shugaban ƙasar Ferdinand Marcos ta ce tsohon shugaban na fuskantar tuhumar kisan ɗimbin jama’a a lokacin mulkinsa, wanda ya fake da yaƙi da masu ta’ammali da miyagun ƙwayoyi.

A lokacin dai ya sha alwashin kawar da fataucin miyagun ƙwayoyi, amma ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’dama sun ce lamarin ya rikiɗe zuwa wani abu daban, inda ake zargin ’yan sanda da kashe dubban mutane, ciki har da waɗanda da ba su ji ba ba su gani ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kotun Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdulahi Usman, ya rasu

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Taraba, SP Abdulahi Usman, ya rasu bayan fama da doguwar jinya.

Kakakin rundunar ’yan sandan Najeriya, Olumuyiwa Adejobi ne, ya tabbatar da rasuwarsa cikin wata sanarwa a ranar Laraba.

’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa Ribas: Za mu ɗauki matakan da za su shafi tattalin arzikin Nijeriya — ’Yan ƙwadago

Ya bayyana Usman a matsayin jajirtaccen ɗan sanda kuma gada tsakanin jami’an tsaro da al’umma.

“SP Usman ya shafe shekaru uku yana ƙarfafa hulɗa tsakanin ’yan sanda da jama’ar Taraba.

“Ƙwarewarsa, mutuntaka da jajircewarsa wajen neman adalci sun an samu tasiri,” in ji Adejobi.

Ya ƙara da cewa rasuwar Usman babban rashi ne ga rundunar ’yan sanda, abokan aikinsa da duk wanda ya san shi.

Sashen hulɗa da jama’a na ’yan sanda ya miƙa ta’aziyya ga iyalansa da kuma ‘yan uwansa, tare da yin addu’ar Allah Ya masa rahama.

Za a ci gaba da tunawa da Usman saboda sadaukarwar a aikinsa da ƙoƙarinsa na kyautata hulɗa tsakanin ’yan sanda da al’umma a Jihar Taraba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisa ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  • Majalisar Wakilai ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  • Majalisar Wakilai ta janye ƙudirin da ke neman tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  • An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu
  • Nijar : An nada Janar Tiani, a mukamin shugaban rikon kwarya
  • Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu
  • Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasu
  • Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdulahi Usman, ya rasu
  • Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo
  • Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati