Tsohon shugaban Philippines ya faɗa komar ’yan sanda
Published: 11th, March 2025 GMT
’Yan sanda sun cafke tsohon shugaban ƙasar Philippines, Rodrigo Duterte a filin jirgin saman birnin Manila a wannan Talatar.
Mista Duterte ya faɗa komar ’yan sandan ne bisa sammacin Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, jim kaɗan da saukarsa daga birnin Hong Kong.
Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet Ainihin abin da ke kawo wa Manchester United koma bayaHatsaniya ta ɓarke a filin jirgin saman lokacin da ’yan sanda suka kama Mista Duterte, sakamakon tirjiya daga masu tsaron lafiyarsa da likitansa da kuma lauyoyinsa, wadanda ke zargin cewa an take masa haƙƙinsa da kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba shi.
Fadar shugaban ƙasar Ferdinand Marcos ta ce tsohon shugaban na fuskantar tuhumar kisan ɗimbin jama’a a lokacin mulkinsa, wanda ya fake da yaƙi da masu ta’ammali da miyagun ƙwayoyi.
A lokacin dai ya sha alwashin kawar da fataucin miyagun ƙwayoyi, amma ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’dama sun ce lamarin ya rikiɗe zuwa wani abu daban, inda ake zargin ’yan sanda da kashe dubban mutane, ciki har da waɗanda da ba su ji ba ba su gani ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kotun Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Majalisar Dokokin Taraba 16 sun sauya sheka daga PDP zuwa APC
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Taraba, Rt Hon. Kizito Bonzena, tare da ’yan majalisar 15 sun sauya sheka daga jam’iyyarsu ta PDP zuwa APC.
A saifyar Litinin ne Rt Hon. Kizito Bonzena ya gabatar da takardarsa ta ficewa daga PDP tare da sauran mambobin zuwa APC.
Ya bayyana cewa da sauyin shekar tasu, yanzu APC ce ke da daukacin kujeru 24 da ke Majalisar Dokokin Jihar Taraba.
Hakan na zuwa ne jim kadan bayan Gwamnan Jihar Taraba, Kefas ya sanar da shirinsa na komawa APC daga PDP.
Masu ibadar Umarah 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka ’Yan ta’adda sun sace dalibai 25 a dakunan kwanansu a KebbiSauran mambobin majalisar da suka sauya sheka sun hada da Mataimakin Shugaban Malisar, Hamman Adama Abdullai (Bali 2) da Shugaban Masu Rinjaye, Jethro Yakubu (Wukari 1). Sauran sun hada da Tafarki Eneme (Kurmi ); Akila Nuhu (Lau ); Musa Chul (Gassol 1); da Josiah Yaro (Wukari 2).
Akwai kuma Tanko Yusuf (Takum 1), Veronica Alhassan (Bali 1), Anas Shuaibu (Karim Lamido 2), Nelson Len (Nguroje), Umar Adamu (Jalingo 1), Joseph Kassong (Yorro), John Lamba (Takum 2), Happy Shonruba (Ardo-Kola) da kuma Zakari Sanusi (Ibi Constituency).
Da yake sanar da sauyin shekar tasu, shugaban majalisar ya bayyana cewa sun yi hakan ne saboda bukatar al’umma ba don bukatar kansu ba.
Tsohon Shugaan Malisar Dokokin Jihar, Peter Diah, ya yi maraba da su a APC.