HausaTv:
2025-03-19@14:54:37 GMT

Iran ta soki matakin Amurka na hana shigar da wutar lantarki Iraki

Published: 11th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya soki matakin da sabuwar gwamnatin Amurka ta dauka na janye sassaucin da ta yi wa Iraki na shigo da wutar lantarki daga Iran.

Araghchi ya bayyana matakin da gwamnatin Trump ta dauka a matsayin “abin takaici.”

Ya kara da cewa gwamnatin Amurka ta na kokarin hana al’ummar iraki samun ababen more rayuwa kamar wutar lantarki, musamman gabanin watanni masu zafi na wannan shekara.

Babban jami’in diflomasiyyar Iran ya sake jaddada goyon bayan Jamhuriyar Musulunci ta Iran ga al’ummar Iraki.

Ya kara da cewa Iran ta tsaya tsayin daka kan kudurin ta ga gwamnatin Iraki na dakile ayyukan Amurka da suka sabawa doka.

Kalaman Araghchi sun zo ne bayan da Amurka ta sanar da janye sassaucin da ta yi wa Iran wanda ya bai wa Iraki damar shigo da wutar lantarki daga makociyarta ta gabas.

A martaninsa, shugaban kwamitin kudi na majalisar dokokin Iraki ya yi gargadin cewa duk wani mataki da Washington za ta dauka na takaita shigo da wutar lantarki daga Iran zai haifar da rugujewar wutar lantarki a Iraki.

A halin yanzu, kusan kashi 80 cikin 100 na makamashin da ake samu a Iraki ya dogara ne da iskar gas, wanda hakan ya sa kasar ta dogara sosai da Iran don ci gaba da samar da wutar lantarki.

A watan Yulin 2022, Iraki ta sanya hannu kan kwangilar shekaru biyar da Iran don samar da megawatt 400 na wutar lantarki.

A watan Maris din shekarar 2024, an cimma wata yarjejeniya ta kara yawan iskar gas din Iran zuwa mita cubic miliyan 50 a kowace rana, wanda darajarsa ta kai dala biliyan 6 a duk shekara.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Adadin Shahidan Falasdinawa A Gaza Ya Karu Da 14 A Jiya Lahadi Saboda Hare-Haren Sojojin HKI

Sojojin HKI sun ci gaba da keta hurumin yarjeniyan tsagaita budewa juna wata tsakaninta da Gaza inda a jiya Lahadi kadai ta kashe Falasdinwa 14 a wurare daban daban a yankin.

Tashar talabijin ta Almayadden ta kasar Lebanon ta bayyana cewa yawan shahidai a kan tafarkin Kudus a Gaza ya kai 48,872 da kuma wadanda suka ji rauni tun fara yakin ya karu zuwa 112,032.

Dan rahoton tashar al-mayadeen ya bayyana cewa a jiya Lahadi bafalasdiniya guda ta yi shahada a cikin gidanta a sansanin yan gudun hijira na Nusairat a lokacinda sojojin yahudawan suka bude wuta a kan gidanta.

Rahoton ya kara da cewa wani jirgin yakin da ake sarrafa shi daga nesa ya bude wuta kan wasu Falasdinawa a kauyen Hijru-ddik a tsakiyar zirin gaza na Gaza. Sannan rahoton ya kara da cewa wata tankar yakin HKI ta bude wuta kan wasu wurare a kauyen Al-qararah daga arewa masu gabacin  garin Khan Yunus, inda nan ma da dama suka yi shahada.

Labarin ya kara da cewa an dauko shahidai 17, 8 daga cikinsu ba’a gano ko su waye ba, kuma suna daga cikin wadanda suka yi shahada tun lokacin yakin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin Ribas 
  • Amurka ce Kadai Ta Ki Yin Allawadai Da Killace Gaza A Tsakanin Mambobin Kwamitin Tsaro na MDD
  • Atiku Ya Soki Tinubu Kan Ayyana Dokar Ta-ɓaci a Jihar Ribas
  • Shugaban Putin Na Kasar Rasha Zai Zanta Ta Wayar Tarho Da Tokwaransa Na Kasar Amurka Donal Trump
  • HKI Ta Nuna Damuwarta Da Jibge Sojojin Da Gwamnatin Masar Ta Yi A Yankin Sina
  • Iran An Dauke Wa Mahdi Karubi Daurin Talalar Da Aka Yi Masa A Gida
  • Iran : Zamu fifita diflomasiyya da kasashe makwabtanmu
  • Shugaban Kasar Amurka Ya Kara Yawan Kasashen Da Ya Sa Wa Takunkumin Shiga Amurka
  • Adadin Shahidan Falasdinawa A Gaza Ya Karu Da 14 A Jiya Lahadi Saboda Hare-Haren Sojojin HKI
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [9]