HausaTv:
2025-06-30@22:41:40 GMT

Iran ta soki matakin Amurka na hana shigar da wutar lantarki Iraki

Published: 11th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya soki matakin da sabuwar gwamnatin Amurka ta dauka na janye sassaucin da ta yi wa Iraki na shigo da wutar lantarki daga Iran.

Araghchi ya bayyana matakin da gwamnatin Trump ta dauka a matsayin “abin takaici.”

Ya kara da cewa gwamnatin Amurka ta na kokarin hana al’ummar iraki samun ababen more rayuwa kamar wutar lantarki, musamman gabanin watanni masu zafi na wannan shekara.

Babban jami’in diflomasiyyar Iran ya sake jaddada goyon bayan Jamhuriyar Musulunci ta Iran ga al’ummar Iraki.

Ya kara da cewa Iran ta tsaya tsayin daka kan kudurin ta ga gwamnatin Iraki na dakile ayyukan Amurka da suka sabawa doka.

Kalaman Araghchi sun zo ne bayan da Amurka ta sanar da janye sassaucin da ta yi wa Iran wanda ya bai wa Iraki damar shigo da wutar lantarki daga makociyarta ta gabas.

A martaninsa, shugaban kwamitin kudi na majalisar dokokin Iraki ya yi gargadin cewa duk wani mataki da Washington za ta dauka na takaita shigo da wutar lantarki daga Iran zai haifar da rugujewar wutar lantarki a Iraki.

A halin yanzu, kusan kashi 80 cikin 100 na makamashin da ake samu a Iraki ya dogara ne da iskar gas, wanda hakan ya sa kasar ta dogara sosai da Iran don ci gaba da samar da wutar lantarki.

A watan Yulin 2022, Iraki ta sanya hannu kan kwangilar shekaru biyar da Iran don samar da megawatt 400 na wutar lantarki.

A watan Maris din shekarar 2024, an cimma wata yarjejeniya ta kara yawan iskar gas din Iran zuwa mita cubic miliyan 50 a kowace rana, wanda darajarsa ta kai dala biliyan 6 a duk shekara.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Bawo Mayakan Huthi Fasahar Kera Makamai Masu Linzami Daga Cikin Ruwa

JMI ta bawa kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen makamai masu linzami wadanda ake iya cillasu daga cikin tekuna mai suna Ghadr.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya ce makamai mai linzami samfurin Ghadir wanda ake iya cilla shi daga cikin teku ya shiga hannun sojojin kasar Yemen sannan bisa bayanan wasu kasashen yamma hakan wani hatsari ne ga kasashen Amurka da kawayenta a yankin, musamman HKI.

Makamin wanda ake iya cillashi daga tekun red sea yana yin barna mai yawa ga makaman makiya.  Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran bata yi wani karin bayani dangane da wannan labarin ba, majiyar ofishin daraktan tsaron kasa na Amurka ta bayyana cewa, JMI tana ta fi ko wace kasa a yankin mallakan makamai masu linzami kuma sune a gaba a duniya wajen kera jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga Nesa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban kasar Iran ya soki lamirin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA
  • An sanya dokar hana fita a Kaduna
  • Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
  • Iran Ta Bawo Mayakan Huthi Fasahar Kera Makamai Masu Linzami Daga Cikin Ruwa
  • Kafar Labaran Amurka Ta Ce: Isra’ila Ta Yi Mummunar Hasara A Yakinta Da Kasar Iran
  • Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya
  • Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau 
  • Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
  • Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD