HausaTv:
2025-10-17@21:26:40 GMT

Iran ta soki matakin Amurka na hana shigar da wutar lantarki Iraki

Published: 11th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya soki matakin da sabuwar gwamnatin Amurka ta dauka na janye sassaucin da ta yi wa Iraki na shigo da wutar lantarki daga Iran.

Araghchi ya bayyana matakin da gwamnatin Trump ta dauka a matsayin “abin takaici.”

Ya kara da cewa gwamnatin Amurka ta na kokarin hana al’ummar iraki samun ababen more rayuwa kamar wutar lantarki, musamman gabanin watanni masu zafi na wannan shekara.

Babban jami’in diflomasiyyar Iran ya sake jaddada goyon bayan Jamhuriyar Musulunci ta Iran ga al’ummar Iraki.

Ya kara da cewa Iran ta tsaya tsayin daka kan kudurin ta ga gwamnatin Iraki na dakile ayyukan Amurka da suka sabawa doka.

Kalaman Araghchi sun zo ne bayan da Amurka ta sanar da janye sassaucin da ta yi wa Iran wanda ya bai wa Iraki damar shigo da wutar lantarki daga makociyarta ta gabas.

A martaninsa, shugaban kwamitin kudi na majalisar dokokin Iraki ya yi gargadin cewa duk wani mataki da Washington za ta dauka na takaita shigo da wutar lantarki daga Iran zai haifar da rugujewar wutar lantarki a Iraki.

A halin yanzu, kusan kashi 80 cikin 100 na makamashin da ake samu a Iraki ya dogara ne da iskar gas, wanda hakan ya sa kasar ta dogara sosai da Iran don ci gaba da samar da wutar lantarki.

A watan Yulin 2022, Iraki ta sanya hannu kan kwangilar shekaru biyar da Iran don samar da megawatt 400 na wutar lantarki.

A watan Maris din shekarar 2024, an cimma wata yarjejeniya ta kara yawan iskar gas din Iran zuwa mita cubic miliyan 50 a kowace rana, wanda darajarsa ta kai dala biliyan 6 a duk shekara.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

 

Daga nan sai kakakin ya ce, “Ba zai yiwu bangaren Amurka ya nemi tattaunawa a bangare guda, alhali a daya hannun yana barazanar kaddamar da sabbin takunkumai kan kasar Sin ba. Wannan ba ita ce hanya mai dacewa ta gudanar da cudanya da Sin ba.” (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani October 14, 2025 Daga Birnin Sin Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa  October 14, 2025 Daga Birnin Sin Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin October 14, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO
  • Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafin Kayayyakin Sana’o’i A Karamar Hukumar Gagarawa
  • Iran: Yawan Karafan Da Ake Sayarwa Zuwa Kasashen Waje Ya Kai Dalar Amurka Billion $4
  • Gwamnatin Kamaru Ta Gargadi Dan Takarar Da Ya Shelanta Kansa A Matsayin Wanda Ya Lashe Zabe
  • Isra’ila ta taƙaita shigar da kayan agaji Gaza
  • Matakin Da Kasashen Yamma Su Ka yi Na Maidowa Da Iran Takunkumi Ya Sabawa Doka.
  • An Bukaci An Bukaci Asusun JICHIMA Ya Fadada Hanyoyin Samun Kudade Baya Ga Gwamnatin Jigawa
  • ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako
  • Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya