Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Kan Kalaman Sakataren Baitul Malin Amurka
Published: 11th, March 2025 GMT
Sakataren baitul malin Amurka Scott Bessent ya sha nanata cewa, tattalin arzikin kasar Sin ya dogara a kan kayayyakin da ake fitarwa zuwa kasashen ketare fiye da kima, kuma Amurka na neman yin ciniki bisa adalci da daidaito. Sai dai kuma, da yake mayar da martani a yau Litinin 10 ga watan Maris, yayin wani taron manema labaru na yau da kullum, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning ta yi nuni da cewa, maganar da ake yi a kullum kan “rasa madafa” da neman cikakken daidaiton cinikayya ta saba wa ilimin tattalin arziki na asali, da yin watsi da hukunci da muradun kamfanoni da masu sayayya na Amurka.
Mao Ning ta ce, halin da ake ciki na cinikayya a tsakanin Amurka da kasar Sin yanzu haka ya samo asali ne sakamakon rawar da kasuwanni ke takawa, kuma abubuwa da dama sun shafi tsarin tattalin arzikin kasashen biyu,da manufofin ciniki da kuma matsayin dalar Amurka.
Ta kara da cewa, kasar Sin ba ta taba neman cin bulus da gangan ba. Hasali ma, Amurka ce ta fi tsintar dami a kala daga cinikayyarta da Sin. Mao Ning ta jaddada cewa, ba a sauya wa tuwo suna, domin ko ta yaya Amurka ta sauya akalar abin, ba za ta iya boye yunkurinta na siyasantarwa da mayar da batutuwan tattalin arziki da cinikayya a matsayin makamin dakilewa da neman murkushe kasar Sin ba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare
Majalisar Dokokin Jihar Akwa Ibom ta ƙi amincewa da wani kudiri da ya nemi haramta ci da sayar da naman kare a jihar.
Kudirin, wanda ɗan majalisa mai wakiltar mazabar Etinan, Uduak Ekpoufot ya gabatar ranar Talata, bai samu ko da dan majalisa daya da ya mara masa baya ba.
Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohiJaridar nan ta gano cewa Uduak ya roki majalisar da ta yi la’akari da matsalolin kiwon lafiya da ke tattare da cin nama kare, yana gargadin cewa yadda ake yanka dabbobin ba tare da tsafta ba na iya jefa masu cin nama cikin haɗarin kamuwa da cututtuka irin su rabies, salmonella, trichinella da sauran kwayoyin cuta.
Ya kuma bayyana hanyoyin da ake amfani da su wajen kashe karnuka a kasuwancin a matsayin na rashin tausayi.
Duk da hujjojin da ya gabatar, babu wani ɗan majalisa da ya goyi bayan kudirin, lamarin da ya tilasta wa kakakin majalisar ya yi hukunci da cewa an ƙi amincewa da shi.
Akwai dai sassa da dama na Najeriya, musamman a kudancin kasar nan da ma wasu sass ana Arewacin kasar da ke cin nama kare.
A farkon wannan shekara, wani masani kan namun daji, Edem Eniang, ya ce mata ’yan Najeriya suna cin nama kare fiye da maza, bisa wasu al’adu da ke ɗaukar cewa naman yana inganta laushin fata.
Ya ce wannan al’ada ta fara fitowa fili ne a wata lakca da wani masanin dabbobi, Richard King, ya gabatar.
Eniang ya kuma nuna damuwa kan raguwar adadin karnuka saboda yawan cin naman su da ake yi.
Ya ba da misalan wasu lamarin da suka faru a Ibeno da Oron a jihar ta Akwa Ibom, inda aka sace karnuka aka yanka su don abinci, cikin su har da wata karya mai shayarwa da ’ya’yanta ƙanana.