Adelaja ya jaddada mahimmancin ƙarfafa musayar bayanan sirri da haɗin gwiwar hukumomi, duba da irin kaifin basira da masu fasa-kwari ke amfani da wasu a ‘yan kwanakin nan wurin cimma muradunsu.

 

“Masu fasa kwauri na ci gaba da bunkasa a ayyukansu, kuma don tunkararsu yadda ya kamata, dole ne mu hada kai ta hanyar bayar da bayanan sirri don cimma nasarar ayyukanmu,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai

Ƙungiyar ɗalibai ’yan Jihar Kano ta roƙi Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnoni da ’yan Majalisar Tarayya da su kawo ƙarshen taƙaddamar Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta ASUU.

Ƙungiyar ɗaliban ta ƙasa reshen Jihar Kano (NAKS) ta roƙi shugabannin da su gaggauta aiwatar da duk mai yiwuwa domin warware taƙaddamar da ke tsakanin gwamnati da ASUU.

IAEA ta buƙaci Iran ta bayyana yawan makamashin nukiliyar da ta mallaka An yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai

Aminiyar ta ruwaito cewa, ɗaliban sun yi wannan kiran ne yayin wani taron manema labarai da shugabannin ƙungiyar a jami’o’in Bayero da kuma North West —Mudassir Adamu Musa da Asahabulkhair Labaran Usman —suka jagoranta.

Ɗaliban sun bayyana cewa yajin aikin da ƙungiyar ASUU ke shiga lokaci zuwa lokaci a dalilin taƙaddama da gwamnati yana gurgunta makomar karatunsu da kuma ilimi a ƙasar baki ɗaya.

Ƙungiyar ɗaliban ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da cika duk wata yarjejeniyar da ta ƙulla da ASUU, tana mai cewa muddin aka samu wani abu akasin haka, to babu shakka lamarin zai ci gaba da kawo tasgaro a harkokin ilimi a faɗin ƙasar.

Ɗaliban sun tunatar da duk masu ruwa da tsakin cewa ba su halin karatu a jami’o’in masu zaman kansa ballantana fita neman ilimi a ƙasashen ƙetare irin su Birtaniya, Indiya ko Amurka kamar yadda suke gani ’ya’yan masu hannu da shuni suna yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Za Ta Mayar Da Rarar Kudi Ga Maniyyatan 2026
  • Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa
  • Zargi: Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa
  • Sace ɗalibai: Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi
  • Rundunar Hadin Gwiwa na Faɗaɗa Bincike Don Ceto Daliban da Aka Sace a Neja
  • Dalibai a Jihohin Arewa Maso Yamma Sun Koka Game da Ƙalubalen Tsaro a Yankin
  • Hukumar Hisbah Ta Rufe Wani Wuri da Ake Zargin Ana Aikata Badala A Kano
  • Araqchi: Yarjejeniyar  Da Aka Cimma Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA A Kasar Masar Ta Rushe
  • Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai
  • NAJERIYA A YAU: Halin Kunci Da Matan Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ke Tsintar Kansu A Ciki