Hukumar Kwastam Da DSS Za Su Yi Haɗin Gwiwa Don Yaƙi Da Masu Fasa-ƙwari
Published: 10th, March 2025 GMT
Adelaja ya jaddada mahimmancin ƙarfafa musayar bayanan sirri da haɗin gwiwar hukumomi, duba da irin kaifin basira da masu fasa-kwari ke amfani da wasu a ‘yan kwanakin nan wurin cimma muradunsu.
“Masu fasa kwauri na ci gaba da bunkasa a ayyukansu, kuma don tunkararsu yadda ya kamata, dole ne mu hada kai ta hanyar bayar da bayanan sirri don cimma nasarar ayyukanmu,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Umarnin janye ’yan sanda masu gadin manyan mutane na iya zama zance kawai —Shehu Sani
Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Kwamred Shehu Sani, ya ce umarnin Shugaba Tinubu na janye ’yan sanda daga gadin manyan mutane zai iya zama magana kawai babu aiki.
A daidai wannan lokaci na ƙara yawaitar rashin tsaro, Shugaba Tinubu ya ce yana sa ido sosai kan al’amuran tsaro a faɗin ƙasa tare da jajircewa wajen kare ’yan Najeriya.
A wani taro da ya yi da hukumomin tsaro a ranar Lahadi, Shugaban Ƙasa ya bayar da umarnin cewa a janye ’yan sanda da ke gadin manyan mutane.
A cewar mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, daga yanzu rundunar ’yan sanda za ta mayar da jami’anta kan ayyukan tsaro na asali.
Yau Atiku zai karɓi katin zama ɗan a Jama’iyyar ADC Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwanaUmarnin ya kuma bayyana cewa duk wani babban mutum da ke buƙatar tsaro zai nemi jami’an hukumar tsaron fararen kaya (NSCDC).
Sai dai a martaninsa a shafinsa na X, Sanata Sani ya nuna damuwa cewa wannan umarni na iya zama magana kawai ba tare da cikakken aiwatarwa ba.
Ya rubuta cewa: “Janye ’Yan Sanda daga manyan mutane ra’ayi ne mai kyau da kuma kyakkyawan tsari duba da gaggawar buƙatun tsaron ƙasa, amma zai iya farawa kuma ya ƙare a matsayin magana kawai.”
Najeriya ta sake fuskantar tashin hankali, ciki har da hare-haren Boko Haram a Borno da kuma farmakin ’yan bindiga a jihohin Kebbi, Neja, Kwara da Borno da Bauchi.