Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai Ya Koma SDP
Published: 10th, March 2025 GMT
Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya fice daga jam’iyyar APC tare da komawa SDP.
Majiyoyi sun ce ficewarsa ta biyo bayan rashin gamsuwa da tafiyar jam’iyyar. A cewar El-Rufai, APC ta kauce daga ainihin manufofinta, don haka ba zai ci gaba da kasancewa a cikinta ba.
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – AtikuKoma wa SDP ya haifar da raɗe-raɗin cewa yana shirin tsayawa takarar shugabancin ƙasa a 2027, lamarin da ke nuna sauyar tsarin siyasa a Nijeriya, idan har za a samu ɗan takara daga arewa a 2027.
A halin yanzu, shugabannin APC na nazarin tasirin wannan sauyi, yayin da SDP ke maraba da zuwansa a jam’iyyar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF
Asusun kula da yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya bayyana cewa fiye da yara miliyan 400 a faɗin duniya na rayuwa cikin yanayin talauci mai tsanani.
A cikin sabon rahoton da ya fitar, UNICEF ya ce ƙarin ɗaruruwan miliyoyin yara na fuskantar hatsarin faɗawa talauci sakamakon katse tallafi, rikice-rikice, da kuma sauyin yanayi da ke gurgunta samun lafiya da walwala.
An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a JigawaRahoton ya nuna cewa yara miliyan 118 ba sa samun uku daga cikin muhimman buƙatun rayuwa guda biyar da suka haɗa da ilimi, lafiya, abinci mai gina jiki, ruwa da tsafta, da kuma muhallin da ya dace.
Haka kuma, yara miliyan 17 na rasa fiye da huɗu daga cikin waɗannan muhimman buƙatu na yau da kullum da suka zama wajibi a ce suna samu a rayuwarsu.
UNICEF ta bayyana cewa mafi yawan yaran da ke cikin mawuyacin hali na zaune ne a ƙasashen Kudu da Saharar Afrika da kuma Kudancin Asiya.
A ƙasar Chadi kadai, rahoton ya ce kashi 64% na yara ba sa samun aƙalla biyu daga cikin ababen da suka zama dole a rayuwar yaro.
Rahoton ya kuma nuna cewa matsalolin tsafta na ci gaba da addabar yara a duniya, inda kashi 65% na yaran ƙasashe masu ƙaramin ƙarfi ba su da damar yin amfani da makewayi mai inganci, sai kuma wasu kashi 26 a ƙasashe masu matsakaicin tattalin arziƙi, da kuma kashi 11 a manyan ƙasashe, lamarin dake barazana ga lafiyarsu.
UNICEF ta danganta wannan yanayi da yawan rikice-rikice, tasirin sauyin yanayi, basuka da su ka yi wa ƙasashe katutu, da kuma yawaitar jama’a, lamarin da gaba ɗaya ke ƙara dagula rayuwar yara a faɗin duniya.