Leadership News Hausa:
2025-07-03@03:36:15 GMT

Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai Ya Koma SDP

Published: 10th, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai Ya Koma SDP

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya fice daga jam’iyyar APC tare da komawa SDP.

Majiyoyi sun ce ficewarsa ta biyo bayan rashin gamsuwa da tafiyar jam’iyyar. A cewar El-Rufai, APC ta kauce daga ainihin manufofinta, don haka ba zai ci gaba da kasancewa a cikinta ba.

Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Koma wa SDP ya haifar da raɗe-raɗin cewa yana shirin tsayawa takarar shugabancin ƙasa a 2027, lamarin da ke nuna sauyar tsarin siyasa a Nijeriya, idan har za a samu ɗan takara daga arewa a 2027.

A halin yanzu, shugabannin APC na nazarin tasirin wannan sauyi, yayin da SDP ke maraba da zuwansa a jam’iyyar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An sanya dokar hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon kwana guda a wasu sassan jihar.

Wannan na zuwa ne bayan wani hargitsi tsakanin jami’an tsaro da wasu ɓata-gari a yankin Kakuri.

Wuraren da dokar ta shafa sun haɗa da Kakuri Bus Stop, Kurmi Gwari, Monday Market, Afaka Road, da Kakuri GRA.

Wata sanarwa da Gwamnatin Kaduna ta fitar ta buƙaci mazauna da su kiyaye umarnin wannan doka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC
  • Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
  • Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
  • Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
  • David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu
  • Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea
  • Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
  • Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
  • Uwargidar Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma
  • An sanya dokar hana fita a Kaduna