Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — Muhammad
Published: 10th, March 2025 GMT
Wani matashi mai sana’ar ɗinki, Malam Muhammad Sani Tela ya bayyana cewar, ya shafe fiye da shekara 30 ya na ɗinki.
Ya ce wannan sana’a ta zama tamkar jini da tsoka a gare shi sakamakon yadda ya riƙe ta da hannu bibbiyu.
Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a AdamawaYa ƙara da cewar, wannan sana’a ta ɗinki sana’a ce da ke da matuƙar albarka idan ka sa juriya a ciki domin kuwa ba sana’a ce da za ka tara kuɗi akai-akai ba nan take.
“Sai dai kuma muddin ka tsayar da gaskiya tare da cika alƙawari to lalle za ka samu babban rufin asirin da baya misaltuwa domin kuwa a kullum in ka fito to kuwa za ka samu abin da za ka yi cefanen gidan ka da sauran buƙatu.
A cewarsa, ya samu fa’ida sosai a wannan sana’a ta ɗinki, domin a cikin ta ya yi aure har ma da ‘ya’ya da sauran kadarori.
“Alhamdulillah, kuma babu abin da ya taimaka min na cimma nasara fiye da jajircewa a kanta.
“Kamar kowace sana’a ita ma sana’ar ɗinki t na da nata irin ƙalubalen domin kamar a shekarar da ta shude sakamakon matsalar rayuwa da al’umma suka samu kansu ciki sai da ta kai ga wannan sana’a ta mu ta samu tasgaro na rashin samun ɗinki.
“Domin lokacin ba ta kayan sawa ake yi ba, jama’a na fafutukar abin da za a ci ne ba’a batun ɗinka sutura.
“Amma a bana lamarin sai godiya domin ya kasance muna ɗinkin sosai idan an kwatanta da shekarun baya.
“Saboda yadda ake samun ɗinki tuni mun rufe karɓar ɗinkin sallah sakamakon al’umma sun fara dawowa hayyacin su saboda sauƙin rayuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: wannan sana a ta
এছাড়াও পড়ুন:
An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi
Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun gano wurin da ’yan bindiga suka tsugunar da ɗalibai mata 25 da suka sace daga makarantar kwana ta Maga da ke Jihar Kebbi.
A wani taron manema labarai a Birnin Kebbi, Matawalle ya ce a halin yanzu an tsananta aikin leƙen asiri da tsare-tsare, tare da bayyana cewa ba da jimawa ba za a kuɓutar da ɗaliban cikin nasara, idan komai ya tafi yadda ake so.
An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEFYa nemi goyon bayan al’umma, yana mai cewa, “Haɗin kan jama’a na da matuƙar muhimmanci domin ganin an kammala wannan aiki lafiya lau, tare da dawo da yaran cikin iyayensu ba tare da wata matsala ba.”
A ranar Litinin da ta gabata ne ’yan bindiga suka kai mummunan hari makarantar ta Maga, inda suka yi awon gaba da ɗalibai mata 25, lamarin da ya tayar da hankalin al’umma musamman ma iyayen yaran.
Ministan ya ce tun bayan faruwar lamarin, Gwamnatin Tarayya ta tura ƙarin jami’an tsaro, ciki har da rundunar sojin sama da ta ƙasa, waɗanda ke aiki tare domin gano hanyar shiga ba tare da hallaka ko jikkata ɗaliban ba.
Ya ce, “Mun gano wurin da aka tsare yaran kuma da Yardar Allah za mu ceto su nan ba da jimawa ba. A yanzu haka muna a matakin ɗaukar tsattsauran mataki cikin hikima, domin tabbatar da cewa babu wata illa da za ta same su.”
“Ina kira ga al’ummar Kebbi da su ci gaba da haƙuri da kuma bayar da haɗin kai ga jami’an tsaro. A irin wannan lamari, bayanan sirri daga jama’a na da matuƙar muhimmanci,” in ji shi.
Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a KebbiA bayan nan ne Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarci Ƙaramin Ministan Tsaron da ya koma Jihar Kebbi da aiki sakamakon sace ɗaliban da wasu ’yan bindiga suka yi a jihar.
Tinubu ya umurci Matawalle, wanda tsohon Gwamnan Jihar Zamfara ne, da ya zauna a Kebbi domin sa ido kan dukkan matakan tsaro da ake ɗauka domin kuɓutar da ɗaliban da aka sace.
A cewar mai magana da yawun fadar shugaban ƙasa, Bayo Onanuga wanda ya bayyana umarnin a cikin wata sanarwa da yammacin Alhamis, ana sa ran Matawalle zai isa Birnin Kebbi da safiyar Juma’a.
“Yana da ƙwarewa sosai wajen fuskantar ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane a lokacin da yake gwamnan Jihar Zamfara daga 2019 zuwa 2023,” in ji sanarwar.
“A ranar 26 ga watan Fabrairu, 2021, ’yan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai mata 279 masu shekaru tsakanin 10 da 17 a makarantar kwana ta GGSSS Jangebe, Jihar Zamfara. ’Yan bindigar sun saki dukkan waɗanda suka yi garkuwar da su a ranar 2 ga watan Maris, 2021.”
Aminiya ta ruwaito cewa, shi ma dai Shugaba Tinubu ya ɗage tafiyarsa da aka tsara zuwa Johannesburg, Afirka ta Kudu, da Luanda a ƙasar Angola, domin ci gaba da samun rahotannin tsaro kan satar ɗaliban na Kebbi da kuma harin da aka kai wa masu ibada a cocin Eruku da ke Jihar Kwara.