Aminiya:
2025-12-07@09:03:25 GMT

Yadda za a samu rufin asiri da sana’ar ɗinki — Muhammad

Published: 10th, March 2025 GMT

Wani matashi mai sana’ar ɗinki, Malam Muhammad Sani Tela ya bayyana cewar, ya shafe fiye da shekara 30 ya na ɗinki.

Ya ce wannan sana’a ta zama tamkar jini da tsoka a gare shi sakamakon yadda ya riƙe ta da hannu bibbiyu.

Ko dai Gwamna Fubara ya yi murabus ko a tsige shi — APC An cafke mutum uku kan satar wayoyin lantarki a Adamawa

Ya ƙara da cewar, wannan sana’a ta ɗinki sana’a ce da ke da matuƙar albarka idan ka sa juriya a ciki domin kuwa ba sana’a ce da za ka tara kuɗi akai-akai ba nan take.

“Sai dai kuma muddin ka tsayar da gaskiya tare da cika alƙawari to lalle za ka samu babban rufin asirin da baya misaltuwa domin kuwa a kullum in ka fito to kuwa za ka samu abin da za ka yi cefanen gidan ka da sauran buƙatu.

A cewarsa, ya samu fa’ida sosai a wannan sana’a ta ɗinki, domin a cikin ta ya yi aure har ma da ‘ya’ya da sauran kadarori.

“Alhamdulillah, kuma babu abin da ya taimaka min na cimma nasara fiye da jajircewa a kanta.

“Kamar kowace sana’a ita ma sana’ar ɗinki t na da nata irin ƙalubalen domin kamar a shekarar da ta shude sakamakon matsalar rayuwa da al’umma suka samu kansu ciki sai da ta kai ga wannan sana’a ta mu ta samu tasgaro na rashin samun ɗinki.

“Domin lokacin ba ta kayan sawa ake yi ba, jama’a na fafutukar abin da za a ci ne ba’a batun ɗinka sutura.

“Amma a bana lamarin sai godiya domin ya kasance muna ɗinkin sosai idan an kwatanta da shekarun baya.

“Saboda yadda ake samun ɗinki tuni mun rufe karɓar ɗinkin sallah sakamakon al’umma sun fara dawowa hayyacin su saboda sauƙin rayuwa.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: wannan sana a ta

এছাড়াও পড়ুন:

Dorinar Ruwa ta Yi Ajalin Mutane Biyu, ta Raunata Shida a Gombe

Mutanen garin Dadin-Kowa da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba a Jihar Gombe, sun shiga damuwa kan yadda wata Dorinar ruwa ta addabi yankin, ta hanyar kashe mutane da kuma lalata gonaki.

Cikin watanni biyu, Dorinar ta kashe mutum biyu, ta karya wasu biyu, sannan ta jikkata wasu huɗu, waɗanda yawanci manoma da masunta ne a Dam ɗin Dadin-Kowa.

Matsalar ta sa ɗan Majalisar Tarayya na Yamaltu Deba, Inuwa Garba, ya kai koke gaban Majalisar Wakilai, inda ya nemi gwamnati ta hanzarta kawo wa mazauna yankin ɗauki.

Ya ce, “Ta’addancin Dorinar ya yi yawa. Idan ba a taimaka mana ba, za ta ci gaba da kashe mutane da lalata amfanin gona.”

A makon da ya gabata, Dorinar ta farmaki wani matashi mai suna Sama’ila Garba (Mai Lasa), bayan ya faɗa cikin ruwa.

Shaidu, sun ce dabbar ta yi ƙoƙarin kashe matashin, ta yadda hanjin cikinsa sai da ya fito, kafin a ceto shi.

Garba Zafi, ɗan uwansa, ya ce Sama’ila ya je bakin ruwa ne kawai sai ya ji ya faɗa, daga nan Dorinar ta afka masa.

Wani mazaunin garin, Akilu Gyara Sa’a, ya roƙi gwamnati ta kai musu agaji duba da yadda rayuwar mutane ke da muhimmanci.

Ya ce: “Dorinar tana lalata gonaki, tana kashe mutane. Gwamnati ta hanzarta magance matsalar kafin abin ya ta’azzara.”

Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce zai bincika domin samun cikakken bayani kan lamarin.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto bai yi ƙarin haske kan lamarin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano
  • Dorinar Ruwa ta Yi Ajalin Mutane Biyu, ta Raunata Shida a Gombe
  • Akwai hannun ƙasashen waje a rashin tsaron Najeriya —Sheikh Gumi
  • Cikakken jadawalin rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026
  • Dorinar ruwa ta kashe mutum 2, ta jikkata 6 a Gombe
  • Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum
  • Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale