HausaTv:
2025-07-08@06:15:55 GMT

Shugaban Ghana ya ziyarci kasashen Sahel da suka balle daga Ecowas

Published: 10th, March 2025 GMT

Shugabana kasar Ghana John Dramani Mahama, ya ziyarci kasashen Mali da Nijar a wani bangare na ran gadin diflomatsiyya da ya fara a kasashen sahel din nan uku da suka balle daga kungiyar Ecowas.

Bayan birnin Bamako a ranar Asabar, shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya je birnin Yamai a ranar Lahadi, inda wasu rahotanni ke cewa ya je ne da nufin dinke barakar da ke tsakanin kungiyar ta raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) da kasashen uku na Sahel.

Saidai a cikin wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin na Nijar, hukumomin kasar sun tabbatar da cewa kasashen sun tabbatar da aniyarsu ta karfafa dangantakar abokantaka da hadin gwiwa a tsakanin kasashensu a fannonin siyasa, tattalin arziki da tsaro.

Kafin Nijar, John Dramani Mahama ya je Mali inda Janar Assimi Goïta ya tarbe shi. A cewar fadar shugaban kasar Ghana, ganawar da aka yi tsakanin mutanen biyu ta ba da damar fara tattaunawa kan karfafa hadin gwiwa a fannin tsaro.

Shugaban na Ghana ya kuma yi amfani da wannan dama wajen bayyana mahimmancin kasuwanci ta hanyar hanyar tashoshin jiragen ruwa na Ghana da ke Tekun Atlantika ga Mali.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Miliyoyin Mutane Sun Yi Juyayin Imam Husain ( a.s) A Karbala

A kasar Iraki,miliyoyin mutane sun cika birnin Karbala domin yin juyayin shahadar  Ahlul Bayti ( a.s) da iyalansa tsarkaka, a tsakanin hubbaren Imam Hussain da dan’uwansa Abul Fadal Abbas ( a.s).

Masoya Ahlul Bayti ( a s.) da su ka fito daga cikin kasar ta Iraki da kuma wasu kasashe, sun yi cincirindo a cikin birnin na Karbala a tsakanin hubbaren Imam Hussain da Abul Fadal Abbas ( a.s).

Cibiyar da take kula da wuraren masu tsarki a Karbala ta yi tsari na kula a tafiyar da juyayin a cikin tsaro  da kuma gabatar da hidima ga masu Ziyara.

An girke jami’an tsaro masu tsaro yawa a cikin birnin na Karbala da zagayen haramin Imam Hussain ( a.s) , haka nan kuma an girke na’urorin gano abubuwa masu fashewa a wurare mabanbanta da su ka hada da mashiga hudu ta garin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan
  • China Ta Mayar Da Martani Kan Barazanar Trump Na Ƙarin Haraji Ga Kasashen BRICS
  • Sojoji Sun Fatattaki Ƴan Bindigar Da Suka Zo Sace Wani Ɗan China
  • Kasar Rasha Tana Ci Gaba Da Karya Kadarin Kasashen Turai A Yakin Da Suke Yi A Ukraine  
  • Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
  •  Nijar: An Kashe Sojoji 10 A Wasu Hare-hare Biyu Na ‘Yan Ta’adda
  • Miliyoyin Mutane Sun Yi Juyayin Imam Husain ( a.s) A Karbala
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 41 a Nijar
  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu