Shugaban Ghana ya ziyarci kasashen Sahel da suka balle daga Ecowas
Published: 10th, March 2025 GMT
Shugabana kasar Ghana John Dramani Mahama, ya ziyarci kasashen Mali da Nijar a wani bangare na ran gadin diflomatsiyya da ya fara a kasashen sahel din nan uku da suka balle daga kungiyar Ecowas.
Bayan birnin Bamako a ranar Asabar, shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya je birnin Yamai a ranar Lahadi, inda wasu rahotanni ke cewa ya je ne da nufin dinke barakar da ke tsakanin kungiyar ta raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) da kasashen uku na Sahel.
Saidai a cikin wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin na Nijar, hukumomin kasar sun tabbatar da cewa kasashen sun tabbatar da aniyarsu ta karfafa dangantakar abokantaka da hadin gwiwa a tsakanin kasashensu a fannonin siyasa, tattalin arziki da tsaro.
Kafin Nijar, John Dramani Mahama ya je Mali inda Janar Assimi Goïta ya tarbe shi. A cewar fadar shugaban kasar Ghana, ganawar da aka yi tsakanin mutanen biyu ta ba da damar fara tattaunawa kan karfafa hadin gwiwa a fannin tsaro.
Shugaban na Ghana ya kuma yi amfani da wannan dama wajen bayyana mahimmancin kasuwanci ta hanyar hanyar tashoshin jiragen ruwa na Ghana da ke Tekun Atlantika ga Mali.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
BUA ya tallafa wa ɗaliban Sakkwato 200 da miliyan 40
Kamfanin samar da siminti na BUA ya bayar da tallafin karatu Naira miliyan 40 ga ɗalibai 200 da ke manyan makarantu a jihohin tsohuwar Jihar Sakkwato.
An bayar da tallafin domin ganin sun cimma burinsu a fannin ilmi.
An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin motaƊaliban da suka ci gajiyar sun haɗa da matasa 50 daga Sakkwato, 50 daga Kebbi da 50 daga Zamfara, sai 50 a Wamakko inda cibiyar kamfanin simintin yake.
Kowane ɗalibi zai karɓi Naira dubu 200, an samu ninkin ɗaliban kuɗin ma an samu ƙari da kashi 100 bisa ga shekarun baya.
Shugaba kuma Daraktan kamfanin, Injiniya Yusuf Binji ya ce sun ninka yawan ɗalibai daga 100 zuwa 200 haka kuɗin daga dubu 100 zuwa 200.
Injiniya Binji ya bayyana tallafin karatun matsayin saka jari ne da zai samar da al’ummar mai ɗorawa a gaba.
Ya yi kira ga waɗanda suka ci gajiyar su yi abin da ya dace kuma kamfani zai bibiyi karatunsu.
Shugaban Kamfanin na BUA ya gode wa gwamnatin jiha kan samar musu filin kasuwanci ba tsangwama.
Mai baiwa Gwamanan Sakkwato shawara, Honarabul Usman Arzika Fako ya ce tallafin zai bunƙasa ilmi da samar da aikin yi ga matasa.
Ya yaba wa kamfanin ga wannan hoɓɓasar, akwai buƙatar a duba wasu ɓangarori suma a yi abin da ya kamata.
Balkisu Bello Muhammad, ɗaliba daga Kebbi ta bayyana BUA ginshiƙi ne na samar da cigaba ta gode wa kamfanin kan wannan saka jarin da suka yi da za su ci gajiyarsa a gaba.
Umar Bello ɗalibi daga Zamfara ya nuna farin cikinsa ga kamfanin yadda ya ɗaga karatunsa zai samu nasara a gaba.