Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi Patrick Adaba ya rasu
Published: 10th, March 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi, Cif Patrick Adaba ya riga mu gidan gaskiya.
An ruwaito cewa Cif Adaba wanda ya shafe shekaru 78 a doron ƙasa ya rasu ne bayan ya yi fama da jinya a Abuja.
Abba ya ƙaddamar da bincike kan zaftare albashin ma’aikatan Kano Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanciWata majiya daga iyalansa ta ce tsohon Mataimakin Gwamnan ya rasu ne cikin daren ranar Lahadi.
Cif Patrick Adaba shi ne ya yi wa Prince Abubakar Audu mataimakin gwamna bayan samun nasara a Zaɓen 1999.
Tsohon Mataimakin Gwamnan wanda ya fito daga Ƙaramar Hukumar Adavi da ke Jihar Kogin, ƙani ne ga tsohon Darekta Janar na Hukumar Kula da Kafofin Watsa Labarai (NBC), marigayi Tom Adaba wanda ya rasu a watan jiya na Fabarairu.
Majiyar ta ce za a binne gawar marigayi Patrick Adaba a Abuja, inda aka binne yayan nasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar NBC Jihar Kogi mataimakin gwamna Mataimakin Gwamnan
এছাড়াও পড়ুন:
Sarakuna sun goyi bayan Gwamnatin Gombe kan yaƙi da cin zarafin mata
Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Gombe ƙarƙashin Kwamishina, Asma’u Muhammad Iganus, ta ziyarci masarautun Nafada da Funakaye domin ƙaddamar da kwamitocin yaƙi da cin zarafi ga mata da yara.
A ziyarar ta farko a Masarautar Nafada, Kwamishiniyar ta ce alƙaluma sun nuna cewa cin zarafi ya kai kashi 87.46 a jihar.
Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali Yadda mutane suka yi cikar ƙwari don halartar jana’izar Sheikh Dahiru BauchiTa ce ya ce ya zama dole a haɗa kai da sarakunan gargajiya don kawar da matsalar.
Sarkin Nafada, Alhaji Muhammad Dadum Hamza, ya yi tir da yawaitar laifukan aikata fyaɗe a yankin.
Ya bayyana cewa babu wani gurbi da mai laifin aikata fyaɗe zai samu mafaka.
Ya ce za su tabbatar da an hukunta duk wanda aka kama, tare da goyon bayan ƙarin hukuncin ɗaurin sama da shekaru 14 da doka ke yi a yanzu.
A Masarautar Funakaye, Sarkin Funakaye, Alhaji Yakubu Muhammad Kwairanga IV, ya nuna cikakken goyon bayansa ga matakin gwamnati.
Ya ce ba za a yi wa masu aikata fyaɗe sassauci ba, domin hukunci mai tsanani shi ne zai rage aikata laifin.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Funakaye, Alhaji Abdurrahman Shua’ibu Adam, ya tabbatar da cewa za su ci gaba da aiki tare da ma’aikatar domin kare mata da yara.
Kwamishiniyar, ta miƙa kundin Dokar VAPP ga masarautar Funakaye domin fara aiki da shi kai-tsaye.