Aminiya:
2025-11-27@20:19:15 GMT

Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi Patrick Adaba ya rasu

Published: 10th, March 2025 GMT

Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi, Cif Patrick Adaba ya riga mu gidan gaskiya.

An ruwaito cewa Cif Adaba wanda ya shafe shekaru 78 a doron ƙasa ya rasu ne bayan ya yi fama da jinya a Abuja.

Abba ya ƙaddamar da bincike kan zaftare albashin ma’aikatan Kano Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci

Wata majiya daga iyalansa ta ce tsohon Mataimakin Gwamnan ya rasu ne cikin daren ranar Lahadi.

Cif Patrick Adaba shi ne ya yi wa Prince Abubakar Audu mataimakin gwamna bayan samun nasara a Zaɓen 1999.

Tsohon Mataimakin Gwamnan wanda ya fito daga Ƙaramar Hukumar Adavi da ke Jihar Kogin, ƙani ne ga tsohon Darekta Janar na Hukumar Kula da Kafofin Watsa Labarai (NBC), marigayi Tom Adaba wanda ya rasu a watan jiya na Fabarairu.

Majiyar ta ce za a binne gawar marigayi Patrick Adaba a Abuja, inda aka binne yayan nasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar NBC Jihar Kogi mataimakin gwamna Mataimakin Gwamnan

এছাড়াও পড়ুন:

Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Chelsea za ta karɓi baƙuncin Barcelona a wasan mako na biyar na gasar cin Kofin Zakarun Turai (Champions League) da ke ci gaba da gudana a kakar nan.

Wasan da za a buga a filin Stamford Bridge, yana zuwa ne bayan da ’yan wasan Barcelona suka ƙauracewa atisayi a bainar jama’a domin ɓoye salon horon su.

Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa

Chelsea da Barcelona sun haɗu sau 14 a gasar Zakarun Turai, inda kowacce ƙungiyar ta yi nasara huɗu, sannan aka yi kunnen doki shida.

Wannan shi ne karo na farko da ƙungiyoyin za su kara tun kakar 2017/18 a zagayen ’yan 16, lokacin da Barcelona ta yi nasarar tsallakawa zagaye na gaba, bayan cin jimilla 4–1 a waje da gida — wanda aka tashi 1–1 a Stamford Bridge da kuma nasarar 3–0 a Sifaniya.

Chelsea ta sha kashi sau ɗaya ne kawai daga wasanninta bakwai da ta yi a gida a gasar Zakarun Turai da Barcelona — inda ta yi nasara huɗu tare da tashi kunnen doki biyu a Stamford Bridge.

Haka kuma, Chelsea ta  cin wasa biyu a fafatawa 61 baya a gasar Zakarun Turai a gida, sannan ba ta yi rashin nasara ba a fafatawa 16, wadda ta ci 12 da canjaras huɗu — tun bayan doke ta 1-0 da Valencia a Satumbar 2019.

A gefe guda, Barcelona ta yi rashin nasara uku ne kacal daga wasa 20 a Champions League da ta fuskanci wata ƙungiyar Ingila, bayan cin 13 da canjaras huɗu da kuma rashin nasara ɗaya daga fafatawa 11, baya ga samun nasara a karawa takwas da canjaras biyu daga ciki.

Lamine Yamal, wanda zai cika shekara 18 da kwana 135 ranar Talata, ya riga ya zura ƙwallo bakwai a Champions League kafin cikarsa shekara 19.

Yana buƙatar ƙarin uku domin ya yi daidai da tarihin Kylian Mbappé a wannan rukuni.

Barcelona ta zura ƙwallo 96 a raga cikin wasanninta 20 na baya-bayan nan a Champions League.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki
  • Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya
  • Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu.
  • Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina