Aminiya:
2025-07-05@17:59:47 GMT

Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi Patrick Adaba ya rasu

Published: 10th, March 2025 GMT

Tsohon Mataimakin Gwamnan Kogi, Cif Patrick Adaba ya riga mu gidan gaskiya.

An ruwaito cewa Cif Adaba wanda ya shafe shekaru 78 a doron ƙasa ya rasu ne bayan ya yi fama da jinya a Abuja.

Abba ya ƙaddamar da bincike kan zaftare albashin ma’aikatan Kano Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci

Wata majiya daga iyalansa ta ce tsohon Mataimakin Gwamnan ya rasu ne cikin daren ranar Lahadi.

Cif Patrick Adaba shi ne ya yi wa Prince Abubakar Audu mataimakin gwamna bayan samun nasara a Zaɓen 1999.

Tsohon Mataimakin Gwamnan wanda ya fito daga Ƙaramar Hukumar Adavi da ke Jihar Kogin, ƙani ne ga tsohon Darekta Janar na Hukumar Kula da Kafofin Watsa Labarai (NBC), marigayi Tom Adaba wanda ya rasu a watan jiya na Fabarairu.

Majiyar ta ce za a binne gawar marigayi Patrick Adaba a Abuja, inda aka binne yayan nasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar NBC Jihar Kogi mataimakin gwamna Mataimakin Gwamnan

এছাড়াও পড়ুন:

’Ya’yana na da ’yancin mallakar filaye a Abuja – Wike

Ministan Babban Birninn Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya musanta labarin cewa ya yanka wa ’ya’yansa manyan filaye a Abuja, inda ya ce in ma haka ne suna da hakki a matsayinsu na ’yan Najeriya.

Ana dai zargin Wike da ba biyu daga cikin ’ya’yansa fili mai fadin murabba’in hekta 2,082, dayan kuma mai fadin hekta 1,740, wanda aka kiyasta darajarsu ta haura Naira tiriliyan tara.

Da yake zantawa da ’yan jarida a Abuja ranar Alhamis, Wike ya karyata labarin na cewa ya ba ’ya’yan nasa filayen a unguwannin Maitama da Asokoro.

Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC Filato: Mahara sun cire hannun matashi a kan hanyar komawa gida daga jana’iza

To sai dai duk da haka, ya kare batun, inda ya ce a matsayin su na ’yan Najeriya, su ma sun cancanci su mallaki filayen matukar dai an bi ka’ida.

“Alal misali, amma ba wai na amsa haka ba ne, a ce ’ya’yana sun nemi filayen, shin ba su cancanta a ba su ba ne? ko su ’yan Ghana ne? ko kuwa a’a, kawai saboda ni ina minista shi ke nan ba su cancanta ba?,” in ji Wike.

Ministan ya zargi wasu mutane da ya ce ba su da suna daga jihar Adamawa da kitsa zancen domin kawai su bata masa suna.

“Da farko ma ka fara lissafa hekta 2,000 na fili sai ka fada min a ina za ka sami hakan a Asokoro da Maitama. Na san daga jihar Adamawa aka shirya wannan kitimurmurar,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila
  • Hadiman gwamnan Kano sun haura 300 bayan naɗa wasu sabbi 19
  • 2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC
  • Mai shekara 70 ya kashe ƙanwarsa kan gadon gona a Jigawa
  • Gwamnan Bauchi ya ƙaddamar da kwamitin ƙirƙiro da sabbin masarautu
  • “ADC za ta fuskanci matsala wajen zaɓen wanda zai yi mata takarar shugaban ƙasa”
  • ’Ya’yana na da ’yancin mallakar filaye a Abuja – Wike
  • Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC
  • Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota
  • 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC