Aminiya:
2025-11-23@14:19:39 GMT

Abba ya ƙaddamar da bincike kan zaftare albashin ma’aikatan Kano

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi tsattsauran gargaɗi dangane da rahotannin da ke yawo kan cirar kuɗi daga albashin ma’aikatan gwamnati ko kuma ƙin biyan su gaba ɗaya.

Ya bayyana hakan a matsayin cin zarafin ma’aikata da cin amanar jama’a, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci hakan ba.

Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi

Biyo bayan korafe-korafen da ma’aikata suka yi, na cewa wasu daga cikinsu sun shafe watanni ba tare da samun hakkokinsu ba, Gwamna Yusuf ya sha alwashin gano masu hannu a wannan ɗanyen aiki da kuma hukunta su.

“Gwamnatin nan ba za ta yarda da zalunci ma’aikatanta ba. Duk wanda aka samu da hannu a wannan mummunan aiki zai fuskanci hukunci mai tsanani,” in ji Gwamnan.

Gwamnan ya kafa kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin matsalar, wanda zai gudanar da cikakken bincike kan tsarin biyan albashi daga watan Oktoba 2024 zuwa Fabrairu 2025

An ɗora wa kwamitin alhakin gano ma’aikatan da abin ya shafa, tasirin hakan kan kuɗin gwamnati, tare da ba da shawarwari kan yadda za a magance matsalar da kuma hukunta masu hannu a ciki.

Kwamitin, wanda ke da mambobi bakwai yana karkashin jagorancin Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma kuma tsohon Akanta Janar na Jiha, Abdulkadir Abdussalam.

Mambobin sun hada da: – Abdulkadir Abdussalam – Shugaban Kwamitin kuma Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma da Dokta Bashir Abdu Muzakkari – Mai ba da shawara na musamman kan tattalin arzikin zamani.

Sai Dokta Aliyu Isa Aliyu – Darakta Janar na Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano da Dokta Hamisu Sadi Ali – Darakta Janar na Hukumar Kula da Bashin Jihar Kano da Hajiya Zainab Abdulkadir – Darakta ta Cibiyar Kwamfuta ta Jihar Kano.

Akwai kuma Aliyu Muhammad Sani – Darakta na Bincike da Tantancewa a Ofishin Sakataren Gwamnati da Ummulkulthum Ladan Kailani – Mataimakiyar Sakatariya, Ofishin Sakataren Gwamnati.

An bai wa kwamitin wa’adin kwanaki bakwai domin kammala binciken tare da mika rahoto wanda zai ƙunshi sunayen masu laifi, asarar da aka yi, da kuma shawarwarin magance matsalar gaba ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa

Majalisar Dokokin Jihar Kano, ta wanke Shugaban Ƙaramar Hukumar Rano da aka dakatar, Alhaji Naziru Yau, daga dukkanin zarge-zargen da aka masa.

Wannan ya ba shi damar komawa bakin aikinsa da shugabancin Ƙaramar Hukumar Rano.

An kama Faston da ake zargi da yi wa mambobin cocinsa 3 fyade ’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin su

An dakatar da Yauyayin da ake bincike a kansa.

Bayan sanar da dawo da shi kan kujerunsa, dubban magoya bayansa ne suka tarbe shi da murna a kan iyakar Rano da Bunkure.

Daga nan ya wuce zuwa fadar Sarkin Rano, Muhammad Isa Umaru, wanda ya yi masa addu’a kafin ya sake komawa ofis ɗinsa da ke sakateriyar Ƙaramar Hukumar Rano.

Da yake yi wa ma’aikata da magoya bayansa jawabi, Yau, ya gode wa Allah da Ya tsare masa mutuncinsa.

Sannan ya gode wa Majalisar Dokokin jihar da ta wanke shi.

Ya yi godiya ga Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, Gwamna Abba Kabir Yusuf, shugabannin NNPP da sauran masu ruwa da tsaki da suka taimaka wajen dawo da shi kan kujerarsa.

Tun farko an dakatar da shi ne bayan kwamitin karɓar ƙorafe-ƙorafe na majalisar ya miƙa rahoton wucin-gadi.

Rahoton ya zarge shi da aikata ba daidai ba, cin zarafin ofishinsa, karkatar da dukiyar jama’a da kuma aikata rashin gaskiya wajen sarrafa kuɗaɗen gwamnati.

Sauran zarge-zargen sun haɗa da haifar da rikici tsakanin shugabannin siyasa, sayar da taki sama da farashin da gwamnati ta ƙayyade, da kuma rashin bayyana gaskiya wajen karɓar kuɗaɗen haraji na kasuwanni.

Haka kuma an zarge shi da sayar da rumfunan kasuwa ba bisa ƙa’ida ba.

Yanzu da an wanke shi daga dukkanin zarge-zargen, ya koma bakin aikinsa a matsayin Shugaban Ƙaramar Hukumar Rano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 
  • Tuƙin ganganci: KASTELEA  Ƙaddamar Da gangamin wayar da kai a Zariya
  • Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa
  • An kama Faston da ake zargi da yi wa mambobin cocinsa 3 fyade
  • Rundunar Hadin Gwiwa na Faɗaɗa Bincike Don Ceto Daliban da Aka Sace a Neja
  • Dalibai a Jihohin Arewa Maso Yamma Sun Koka Game da Ƙalubalen Tsaro a Yankin
  • Hukumar Hisbah Ta Rufe Wani Wuri da Ake Zargin Ana Aikata Badala A Kano
  • Gwamna Abba Kabir Zai Gabatar Da Kudirin Kafin 2026 Ga Majalisar Kano Ranar Laraba
  • Kwamitin Sulhu Na MDD Ya yi Tsokaci Kan Rashin Tsaro A Najeriya
  • Sai da Kwankwaso APC za ta iya samun nasara a 2027 — NNPP