Aminiya:
2025-12-07@10:46:00 GMT

Abba ya ƙaddamar da bincike kan zaftare albashin ma’aikatan Kano

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi tsattsauran gargaɗi dangane da rahotannin da ke yawo kan cirar kuɗi daga albashin ma’aikatan gwamnati ko kuma ƙin biyan su gaba ɗaya.

Ya bayyana hakan a matsayin cin zarafin ma’aikata da cin amanar jama’a, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci hakan ba.

Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi

Biyo bayan korafe-korafen da ma’aikata suka yi, na cewa wasu daga cikinsu sun shafe watanni ba tare da samun hakkokinsu ba, Gwamna Yusuf ya sha alwashin gano masu hannu a wannan ɗanyen aiki da kuma hukunta su.

“Gwamnatin nan ba za ta yarda da zalunci ma’aikatanta ba. Duk wanda aka samu da hannu a wannan mummunan aiki zai fuskanci hukunci mai tsanani,” in ji Gwamnan.

Gwamnan ya kafa kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin matsalar, wanda zai gudanar da cikakken bincike kan tsarin biyan albashi daga watan Oktoba 2024 zuwa Fabrairu 2025

An ɗora wa kwamitin alhakin gano ma’aikatan da abin ya shafa, tasirin hakan kan kuɗin gwamnati, tare da ba da shawarwari kan yadda za a magance matsalar da kuma hukunta masu hannu a ciki.

Kwamitin, wanda ke da mambobi bakwai yana karkashin jagorancin Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma kuma tsohon Akanta Janar na Jiha, Abdulkadir Abdussalam.

Mambobin sun hada da: – Abdulkadir Abdussalam – Shugaban Kwamitin kuma Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma da Dokta Bashir Abdu Muzakkari – Mai ba da shawara na musamman kan tattalin arzikin zamani.

Sai Dokta Aliyu Isa Aliyu – Darakta Janar na Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano da Dokta Hamisu Sadi Ali – Darakta Janar na Hukumar Kula da Bashin Jihar Kano da Hajiya Zainab Abdulkadir – Darakta ta Cibiyar Kwamfuta ta Jihar Kano.

Akwai kuma Aliyu Muhammad Sani – Darakta na Bincike da Tantancewa a Ofishin Sakataren Gwamnati da Ummulkulthum Ladan Kailani – Mataimakiyar Sakatariya, Ofishin Sakataren Gwamnati.

An bai wa kwamitin wa’adin kwanaki bakwai domin kammala binciken tare da mika rahoto wanda zai ƙunshi sunayen masu laifi, asarar da aka yi, da kuma shawarwarin magance matsalar gaba ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da ya sa ’yan sanda suka kama ni — Muhuyi

Tsohon Shugaban Hukumar Kaɓar Koke-koke da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano (PCACC), Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya bayyana dalilin da ya sa ’yan sanda suka kama shi.

Ya ce an kama shi ne saboda jagorantar shari’ar almundahanar biliyoyin Naira na Dala Inland Dry Port, wadda ta shafi tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, da iyalinsa.

Jirgin sojin sama ya yi hatsari a Neja Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno

Muhuyi, ya shaida wa DCL Hausa cewa an tafi da shi Abuja cikin dare.

“Da aka kama ni, suka sanya jami’ai biyu ɗauke da bindiga a gefena, sai wasu uku a gaba. Haka muka tafi daga Kano zuwa Abuja cikin dare,” in ji shi.

Ya ce ’yan sandan sun ƙi nuna masa takardar izinin kama shi har sai da suka isa Abuja.

“Da muka isa, suka gabatar min da sabbi  tuhume-tuhume na ɓatanci da kutse.

“A ina ne wanda ake zargi zai ki kare kansa ya kuma umarci ’yan sanda su kama babban lauya mai shigar da ƙara?” ya tambaya.

An bayar da belinsa, amma an umarce shi da ya koma Abuja a ranar Laraba tare da miƙa fasfo d5insa.

Ganduje da ’ya’yansa na fuskantar shari’a kan zargin canja mallakar kaso 20 a aikin Dala Inland Dry Port ba bisa ƙa’ida ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya
  • Dalilin da ya sa ’yan sanda suka kama ni — Muhuyi
  • Yan Sanda Sun Kama Muhuyi Magaji, Tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci a Kano
  • Yaƙin M23 Ya ci Gaba a Congo Duk da Sulhu da Rwanda
  • Iran da Rasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna guda 20, kwangilolin haɗin gwiwa na fasaha guda biyar
  • Na’im Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Kasar Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye
  • Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • An harbe manomi saboda rikici kan filin kiwo a Borno
  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa