Aminiya:
2025-11-22@04:59:00 GMT

Abba ya ƙaddamar da bincike kan zaftare albashin ma’aikatan Kano

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi tsattsauran gargaɗi dangane da rahotannin da ke yawo kan cirar kuɗi daga albashin ma’aikatan gwamnati ko kuma ƙin biyan su gaba ɗaya.

Ya bayyana hakan a matsayin cin zarafin ma’aikata da cin amanar jama’a, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci hakan ba.

Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi

Biyo bayan korafe-korafen da ma’aikata suka yi, na cewa wasu daga cikinsu sun shafe watanni ba tare da samun hakkokinsu ba, Gwamna Yusuf ya sha alwashin gano masu hannu a wannan ɗanyen aiki da kuma hukunta su.

“Gwamnatin nan ba za ta yarda da zalunci ma’aikatanta ba. Duk wanda aka samu da hannu a wannan mummunan aiki zai fuskanci hukunci mai tsanani,” in ji Gwamnan.

Gwamnan ya kafa kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin matsalar, wanda zai gudanar da cikakken bincike kan tsarin biyan albashi daga watan Oktoba 2024 zuwa Fabrairu 2025

An ɗora wa kwamitin alhakin gano ma’aikatan da abin ya shafa, tasirin hakan kan kuɗin gwamnati, tare da ba da shawarwari kan yadda za a magance matsalar da kuma hukunta masu hannu a ciki.

Kwamitin, wanda ke da mambobi bakwai yana karkashin jagorancin Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma kuma tsohon Akanta Janar na Jiha, Abdulkadir Abdussalam.

Mambobin sun hada da: – Abdulkadir Abdussalam – Shugaban Kwamitin kuma Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma da Dokta Bashir Abdu Muzakkari – Mai ba da shawara na musamman kan tattalin arzikin zamani.

Sai Dokta Aliyu Isa Aliyu – Darakta Janar na Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano da Dokta Hamisu Sadi Ali – Darakta Janar na Hukumar Kula da Bashin Jihar Kano da Hajiya Zainab Abdulkadir – Darakta ta Cibiyar Kwamfuta ta Jihar Kano.

Akwai kuma Aliyu Muhammad Sani – Darakta na Bincike da Tantancewa a Ofishin Sakataren Gwamnati da Ummulkulthum Ladan Kailani – Mataimakiyar Sakatariya, Ofishin Sakataren Gwamnati.

An bai wa kwamitin wa’adin kwanaki bakwai domin kammala binciken tare da mika rahoto wanda zai ƙunshi sunayen masu laifi, asarar da aka yi, da kuma shawarwarin magance matsalar gaba ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano

Wani magidanci tare da ɗaukacin iyalinsa huɗu sun rasu sakamakon wata gobara da ta tashi a sanadin kunna maganin sauro a layin Baba Impossible da ke Unguwar Kundila, da ke Ƙaramar Hukumar Tarauni a Jihar Kano.

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ta tabbatar da tashin wutar da misalin ƙarfe 4:13 na Asubar ranar Laraba.

NAJERIYA A YAU: Halin Kunci Da Matan Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ke Tsintar Kansu A Ciki Kotu ta sanya ranar fara shari’ar shugabannin ƙungiyar Ansaru

Mai magana da yawun hukumar, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya ce sun samu kiran wani ma’aikacinsu, HFS Abba Datti, game da gobarar.

A cewarsa ba tare da ɓata lokaci ba suka tura jami’ansu daga hedikwatar hukumar zuwa wajen da gobarar ta tashi.

“Lokacin da muka isa, mun ga wani gida mai girman ƙafa 40 da 30 yana ƙone gaba ɗaya. Gobarar ta shafi ɗakuna biyu, falo, bayan gida, da kuma ɗakin girki,” in ji sanarwar.

Mutane biyar ne gobarar ta rutsa da su; mai gidan mai suna Shodandi mai shekara 43, matarsa Rafi’a mai shekara 30.

Ragowar kuma ’ya’yansu ne; Mardiya Shodandi mai shekara uku, Yusira Shodandi ’yar shekara ɗaya da rabi da Aminu Shodandi ɗan watanni 12.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Huɗu daga cikinsu; uba, uwa, da ƙananan yara biyu sun ƙone kafin a ceto su. Amma an samu damar ceto Aminu ɗan watanni 12.”

Hukumar ta miƙa saƙon ta’aziyyarta ga iyalan mamatan, ta kuma ta gargaɗi mutane da suke kula sosai, musamman a lokacin sanyi.

Bincike ya nuna cewa gobarar ta samo asali ne daga maganin sauro da matatan suka kunna a falo, sannan suka yi barci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar Hadin Gwiwa na Faɗaɗa Bincike Don Ceto Daliban da Aka Sace a Neja
  • Gwamna Abba Kabir Zai Gabatar Da Kudirin Kafin 2026 Ga Majalisar Kano Ranar Laraba
  • Kwamitin Sulhu Na MDD Ya yi Tsokaci Kan Rashin Tsaro A Najeriya
  • Sai da Kwankwaso APC za ta iya samun nasara a 2027 — NNPP
  • Labanon Ta Bukaci Gudanar Da Taron Kwamitin Tsaro Na MDD Cikin Gaggawa
  • Kasashen Iran Da Malesiya Sun Rattaba Hannu Kan Jarjejeniyar Fadada Dangantakar Addini
  • Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano
  • Gwamna Abba ya gabatar da N1.36trn a matsayin kasafin 2026
  • Gwamna Abba ya gabatar da kasafin 2026 na N1.36trn
  • Mai taɓin hankali ya kashe soja a Legas