Aminiya:
2025-12-01@17:41:32 GMT

Abba ya ƙaddamar da bincike kan zaftare albashin ma’aikatan Kano

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi tsattsauran gargaɗi dangane da rahotannin da ke yawo kan cirar kuɗi daga albashin ma’aikatan gwamnati ko kuma ƙin biyan su gaba ɗaya.

Ya bayyana hakan a matsayin cin zarafin ma’aikata da cin amanar jama’a, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci hakan ba.

Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi

Biyo bayan korafe-korafen da ma’aikata suka yi, na cewa wasu daga cikinsu sun shafe watanni ba tare da samun hakkokinsu ba, Gwamna Yusuf ya sha alwashin gano masu hannu a wannan ɗanyen aiki da kuma hukunta su.

“Gwamnatin nan ba za ta yarda da zalunci ma’aikatanta ba. Duk wanda aka samu da hannu a wannan mummunan aiki zai fuskanci hukunci mai tsanani,” in ji Gwamnan.

Gwamnan ya kafa kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin matsalar, wanda zai gudanar da cikakken bincike kan tsarin biyan albashi daga watan Oktoba 2024 zuwa Fabrairu 2025

An ɗora wa kwamitin alhakin gano ma’aikatan da abin ya shafa, tasirin hakan kan kuɗin gwamnati, tare da ba da shawarwari kan yadda za a magance matsalar da kuma hukunta masu hannu a ciki.

Kwamitin, wanda ke da mambobi bakwai yana karkashin jagorancin Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma kuma tsohon Akanta Janar na Jiha, Abdulkadir Abdussalam.

Mambobin sun hada da: – Abdulkadir Abdussalam – Shugaban Kwamitin kuma Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma da Dokta Bashir Abdu Muzakkari – Mai ba da shawara na musamman kan tattalin arzikin zamani.

Sai Dokta Aliyu Isa Aliyu – Darakta Janar na Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano da Dokta Hamisu Sadi Ali – Darakta Janar na Hukumar Kula da Bashin Jihar Kano da Hajiya Zainab Abdulkadir – Darakta ta Cibiyar Kwamfuta ta Jihar Kano.

Akwai kuma Aliyu Muhammad Sani – Darakta na Bincike da Tantancewa a Ofishin Sakataren Gwamnati da Ummulkulthum Ladan Kailani – Mataimakiyar Sakatariya, Ofishin Sakataren Gwamnati.

An bai wa kwamitin wa’adin kwanaki bakwai domin kammala binciken tare da mika rahoto wanda zai ƙunshi sunayen masu laifi, asarar da aka yi, da kuma shawarwarin magance matsalar gaba ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%

Hukumar kididdiga ta HKI ta basa sanarwan cewa yawan yahudawa da suke ficewa daga haramtacciyar kasar .

Tashar talabijin ta Almayadeen na kasar Lebanon ta nakalto hukumar na bada labarin cewa a shekara ta 2010 yawan masana wadanda suke da shahadar Jami’a ya karu ha rya kai kashi 46% sannan wannan adadin ya cilla sama a shekara ta 2023 bayan fara yakin tufanul aksa zuwa kashi 60.4 %.

Har’ila yau kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya bayyana cewa a cikin yan shekarun da suka gabata, yahudawa masu ilmin Jami’a da dama sun bar kasar, saboda yana yaki wanda baya karewa a kasar.

Hukumar kididdiga na HKI a cikin yan kwanakin da suka gabata ta yada rahoto dangane da hijiran yahudawa, musamman daga cikin masu ilmi, wanda ya ga masu shigowa kasar sun ragu matuka a kan wadanda suke ficewa zuwa wasu kasashen duniya don neman inda ake zaman lafiya.

Bisa tsohon tsarin kididdiga na HKI, duk wani bayahude wanda ya share shekara guda a kasashen waje bai shiga HKI ko da nay an kwanaki ba to ana daukarsa a matsayin wanda yayi hijira daga kasar.

Amma a sabon tsarin gwamnatin yahudawan, duk wani bayahude wanda yayi kwanaki 275, wato kasa da shekara guda a kasashen waje, ko da yana zuwa kasar nay an kwanaki za’a lissafa shi daga cikin wadanda suka kaura daga kasar.

Bisa tsohon tsarin mutane dubu 16 suke ficewa daga kasar ba tare da sake dawowa ba, a ko wace shekara. Amma a cikin sabon tsarin an nuna cewa wannan adadin ya karu zuwa mutane dubu 36 a ko wace shekara ne suke ficewa ba tare da sun dawo ba. Daga fara yakinnTufanul Aksa a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 zuwa yanzu adadin yahudawa masu ilmi, wadanda suka hada da likitoci, inginiyoyi da sauransu ne suka fi ficewa daga kasar don duk inda suka je a duniya zasu sami aikin yi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta December 1, 2025 Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta December 1, 2025 Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani December 1, 2025 Tawagar ECOWAS za ta je Guinea-Bissau, bayan juyin mulkin soji December 1, 2025 Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran December 1, 2025 Pezeshkian: Makiya na neman kawo cikas ga ci gaban kasashen Musulmi December 1, 2025 Maduro Ya Gargadi Amurka Game Da Hankoron Mamaye Rijiyoyin Mai Na Venezuela December 1, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa December 1, 2025 Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran. December 1, 2025 Lebanon: Sakon Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano
  • Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa
  • Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba
  • MDD ta yi kira da a gudanar da cikakken bincike kan kisan gillar da aka yi wa Falasdinawa
  • Lebanon ta shigar da kara ga Kwamitin Tsaro bayan Isra’ila ta Gina katanga a Yankinta
  • Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a Kano
  • Yadda ’yan mata ke kufancewa da kasuwancin fara a Kano
  • Portugal ta lashe Kofin Duniya na ’yan ƙasa da shekaru 17 a karon farko
  • Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali