Aminiya:
2025-12-02@20:03:11 GMT

Abba ya ƙaddamar da bincike kan zaftare albashin ma’aikatan Kano

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi tsattsauran gargaɗi dangane da rahotannin da ke yawo kan cirar kuɗi daga albashin ma’aikatan gwamnati ko kuma ƙin biyan su gaba ɗaya.

Ya bayyana hakan a matsayin cin zarafin ma’aikata da cin amanar jama’a, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci hakan ba.

Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi

Biyo bayan korafe-korafen da ma’aikata suka yi, na cewa wasu daga cikinsu sun shafe watanni ba tare da samun hakkokinsu ba, Gwamna Yusuf ya sha alwashin gano masu hannu a wannan ɗanyen aiki da kuma hukunta su.

“Gwamnatin nan ba za ta yarda da zalunci ma’aikatanta ba. Duk wanda aka samu da hannu a wannan mummunan aiki zai fuskanci hukunci mai tsanani,” in ji Gwamnan.

Gwamnan ya kafa kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin matsalar, wanda zai gudanar da cikakken bincike kan tsarin biyan albashi daga watan Oktoba 2024 zuwa Fabrairu 2025

An ɗora wa kwamitin alhakin gano ma’aikatan da abin ya shafa, tasirin hakan kan kuɗin gwamnati, tare da ba da shawarwari kan yadda za a magance matsalar da kuma hukunta masu hannu a ciki.

Kwamitin, wanda ke da mambobi bakwai yana karkashin jagorancin Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma kuma tsohon Akanta Janar na Jiha, Abdulkadir Abdussalam.

Mambobin sun hada da: – Abdulkadir Abdussalam – Shugaban Kwamitin kuma Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma da Dokta Bashir Abdu Muzakkari – Mai ba da shawara na musamman kan tattalin arzikin zamani.

Sai Dokta Aliyu Isa Aliyu – Darakta Janar na Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano da Dokta Hamisu Sadi Ali – Darakta Janar na Hukumar Kula da Bashin Jihar Kano da Hajiya Zainab Abdulkadir – Darakta ta Cibiyar Kwamfuta ta Jihar Kano.

Akwai kuma Aliyu Muhammad Sani – Darakta na Bincike da Tantancewa a Ofishin Sakataren Gwamnati da Ummulkulthum Ladan Kailani – Mataimakiyar Sakatariya, Ofishin Sakataren Gwamnati.

An bai wa kwamitin wa’adin kwanaki bakwai domin kammala binciken tare da mika rahoto wanda zai ƙunshi sunayen masu laifi, asarar da aka yi, da kuma shawarwarin magance matsalar gaba ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

N750,000 kuɗin bikin yaye ɗaliban Jami’ar MAAUN ya tayar da ƙura a Kano

Ana ci gaba da ta ƙaddama kan Naira dubu ɗari bakwai da hamsin da Jami’ar Amurka ta Maryam Abacha  (MAAUN) da ke Jihar Kano ta wajabta wa ɗalibanta da suka kammala karatu biya a matsayin kuɗin bikin yaye ɗalibai.

Jami’ar MAAUN ta sanya wa kowane ɗalibin da ya kammala karatu biyan Naira dubu ɗari bakwai da hamsin a matsayin kuɗin bikin yaye ɗalibai, kafin ta ba shi takardar shaidar kammala karatu da gabatar da bayanansa domin samun damar halartar aikin yi wa ƙasa hidima (NYSC).

Sai dai kuma, Hukumar Karɓar Ƙorafi ta Jihar Kano (PCACC) ta umarci iyayen ɗaliban cewa su dakata da biyan kuɗin har sai ta kammala bincike kan ƙorafin da suka gabatar mata a kan lamarin.

Sanarwar da Shugaban Sashen Ayyuka na PCACC, Salisu Saleh, ya fitar bayan samun ƙorafi daga iyayen ɗaliban, ta umarci hukumar gudanarwar Jami’ar MAAUN da ta jingine shirinta na riƙe takardar kammala karatun ɗaliban ko tura sunayensu domin shirye-shiryen NYSC, saboda rashin biyan kuɗin.

’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno

A gefe guda kuma, hukumar gudanarwar Jami’ar MAAUN ta dage a kan cewa, za ta gudanar da bikin yadda ta riga ta tsara, wanda bai gamsu ba ya tafi kotu.

Mai mallakar Jami’ar MAAUN, Farfesa Abubakar Adamu Gwarzo, ya shaida wa wakilinmu cewa jami’ar za ta gudanar da taron bikin yaye ɗaliban nata kamar yadda ta tsara a cikin wannan wata na Disamba, 2025.

Ya jaddada cewa jami’ar zaman kanta take, don haka tana da ikon sanya kuɗin bikin yaye ɗalibanta.

A cewarsa, kuɗin da MAAUN ta sanya bai kai abin da wata jami’a mai zaman kanta a Jihar ba ta sanya, amma bai ambaci suna ba. Don haka ya kalubalanci Hukumar kan rashin dakatar da biyan kuɗaɗen a ɗaya jami’ar ba.

Ya ce, “Za mu gudanar da bikin a watan Disamba a kamar yadda muka tsara, kuma za mu gayyaci ’yan jarida su ɗauki rahoto.”

Wata wasiƙar ƙorafi a madadin ɗalibai ta nuna damuwa kan yunƙurin tattaunawa da ɗalibai a ɗaiɗaikunsu domin neman ragin kuɗin da jami’ar ta sanya.

Ta bayyana cewa wannan ya saɓa wa abin da aka tsara cewa tattaunawar za ta ƙunshi iyayen ɗalibai da hukumomin jami’ar da kuma wakilan gwamnati.

A yayin da iyaye ke jiran samun tabbacin tsarin da aka yi a hukumance, hukumar gudanarwar Jami’ar MAAUN ta nace cewa babu gudu, babu ja da baya wajen gudanar da taron kamar yadda ta riga ta tsara — duk wanda bai gamsu ba ya tafi kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya naɗa Janar Christopher Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
  • An aiwatar da sauye-sauye a wasu muhimman kwamitocin Majalisar Dattawa
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani
  • N750,000 kuɗin bikin yaye ɗaliban Jami’ar MAAUN ya tayar da ƙura a Kano
  • Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano
  • Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa