Aminiya:
2025-12-14@03:36:44 GMT

Abba ya ƙaddamar da bincike kan zaftare albashin ma’aikatan Kano

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi tsattsauran gargaɗi dangane da rahotannin da ke yawo kan cirar kuɗi daga albashin ma’aikatan gwamnati ko kuma ƙin biyan su gaba ɗaya.

Ya bayyana hakan a matsayin cin zarafin ma’aikata da cin amanar jama’a, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci hakan ba.

Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi

Biyo bayan korafe-korafen da ma’aikata suka yi, na cewa wasu daga cikinsu sun shafe watanni ba tare da samun hakkokinsu ba, Gwamna Yusuf ya sha alwashin gano masu hannu a wannan ɗanyen aiki da kuma hukunta su.

“Gwamnatin nan ba za ta yarda da zalunci ma’aikatanta ba. Duk wanda aka samu da hannu a wannan mummunan aiki zai fuskanci hukunci mai tsanani,” in ji Gwamnan.

Gwamnan ya kafa kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin matsalar, wanda zai gudanar da cikakken bincike kan tsarin biyan albashi daga watan Oktoba 2024 zuwa Fabrairu 2025

An ɗora wa kwamitin alhakin gano ma’aikatan da abin ya shafa, tasirin hakan kan kuɗin gwamnati, tare da ba da shawarwari kan yadda za a magance matsalar da kuma hukunta masu hannu a ciki.

Kwamitin, wanda ke da mambobi bakwai yana karkashin jagorancin Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma kuma tsohon Akanta Janar na Jiha, Abdulkadir Abdussalam.

Mambobin sun hada da: – Abdulkadir Abdussalam – Shugaban Kwamitin kuma Kwamishinan Raya Karkara da Ci-gaban Al’umma da Dokta Bashir Abdu Muzakkari – Mai ba da shawara na musamman kan tattalin arzikin zamani.

Sai Dokta Aliyu Isa Aliyu – Darakta Janar na Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano da Dokta Hamisu Sadi Ali – Darakta Janar na Hukumar Kula da Bashin Jihar Kano da Hajiya Zainab Abdulkadir – Darakta ta Cibiyar Kwamfuta ta Jihar Kano.

Akwai kuma Aliyu Muhammad Sani – Darakta na Bincike da Tantancewa a Ofishin Sakataren Gwamnati da Ummulkulthum Ladan Kailani – Mataimakiyar Sakatariya, Ofishin Sakataren Gwamnati.

An bai wa kwamitin wa’adin kwanaki bakwai domin kammala binciken tare da mika rahoto wanda zai ƙunshi sunayen masu laifi, asarar da aka yi, da kuma shawarwarin magance matsalar gaba ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta

Gwamnatin Jihar Kano, ta haramta kafa Hukumar Hisbah mai zaman kanta tana, wadda tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, yake ƙoƙarin kafawa.

Gwamnatin ta ce kafa hukumar ya saɓa da doka, kuma zai iya zama barazana ga zaman lafiya a jihar.

Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago

A cikin wata takarda da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu a ranar 8 ga watan Disamba, 2025, gwamnatin ta ce ta gano an fara ɗaukar mutane aiki a hukumar ba tare da neman izini ba.

Gwamnatin ta ce hakan ya saɓa wa Dokar Hukumar Hisbah ta Jihar Kano.

Da yake zantawa da ’yan jarida, Kwamishinan YaɗaLabarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya ce Hukumar Hisbah ce kaɗai doka ta amince da ita wajen gudanar da ayyuka a jihar.

Ya ce kafa wata ƙungiya ko hukuma ta daban ba bisa ƙa’ida ba na iya kawo cikas ga zaman lafiya.

Umarnin ya bayyana cewa babu wani mutum ko ƙungiya da ke da ikon ɗaukar mutane aiki, tara su, horas da su ko tura su domin kafa wata hukumar Hisbah mai zaman kanta a jihar.

Gwamna Abba, ya kuma ayyana ayyukan hukumar a matsayin haramtattu, tare da gargaɗin cewa duk wanda ya yi amfani da kayan Hisbah, alamominta ko ikonta ba tare da izini ba zai fuskanci hukunci.

Gwamnan, ya umarci jami’an tsaro, ciki har da ’Yan Sanda, DSS, NSCDC, da sauran hukumomin tsaro, da su binciki waɗanda suka kafa sabuwar hukumar.

Gwamnatin ta kuma gargaɗi jama’a cewa duk wanda ya shiga, ya goyi baya ko ya haɗa kai da sabuwar hukumar, zai fuskanci hukunci.

An shawarci waɗanda aka ɗauka aiki su fice daga hukumar nan take tare da komawa ofishin Hisbah, ko Ƙaramar Hukuma.

Umarnin ya kuma tanadi hukunci ga waɗanda suka saɓa wa dokar, ciki har da gurfanar da su a gaban kotu bisa laifin gudanar da taro ba bisa ƙa’ida ba, kwaikwayon hukumomin gwamnati, da kafa rundunar tsaro ba tare da neman izini ba.

Wannan umarni ya fara aiki nan take, kuma za a yaɗa shi a kafofin watsa labarun Gwamnatin Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara
  • Yadda Rashin Bincike Ke Haifar Da Yawaitar Mutuwar Aure
  • Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi