Tashar talbijin din ‘almayadin’ mai watsa shirye-shirye daga Lebanon ta ambaci cewa; Wasu kauyuka na mabiya mazhabar Alawiyya dake Tartus, da kuma Lazikiyya, sun fuskanci hare-hare daga masu dauke da makamai.

A yau Lahadi, masu dauke da makaman sun kutsa cikin wasu kauyukan Ramilah, Naq’a dake kusa da Jabalah.

Daga jiya zuwa yau masu dauke da makaman sun yi kisan kiyashi a wurare  fiye da 10.

Majiyar Almayadin ta ce ya zuwa yanzu adadin wadanda aka kashe bisa bangaranci sun kai 1000.

Sai dai kuma tshohon mai bai wa shugaban majalisar ‘yan Alawiyya shawara Muhammad Nasir, ya ce, adadin wadanda aka kashe din sun kai 1,700.

Hare-haren sun hada da kona kauyuka 6 a yankin gabar ruwan Midtreniya na kasar Syria.

Da akwai wasu daruruwan gawawwaki a kwance akan titunan garuruwa da kauyuka da biranen yakin Lazikiyya da Hasakah.

A cikin wasu kauyukan mutane da dama sun gudu zuwa kan duwatsu da dajuka domin su tsira da rayukansu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai

Ƙungiyar ɗalibai ’yan Jihar Kano ta roƙi Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnoni da ’yan Majalisar Tarayya da su kawo ƙarshen taƙaddamar Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta ASUU.

Ƙungiyar ɗaliban ta ƙasa reshen Jihar Kano (NAKS) ta roƙi shugabannin da su gaggauta aiwatar da duk mai yiwuwa domin warware taƙaddamar da ke tsakanin gwamnati da ASUU.

IAEA ta buƙaci Iran ta bayyana yawan makamashin nukiliyar da ta mallaka An yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai

Aminiyar ta ruwaito cewa, ɗaliban sun yi wannan kiran ne yayin wani taron manema labarai da shugabannin ƙungiyar a jami’o’in Bayero da kuma North West —Mudassir Adamu Musa da Asahabulkhair Labaran Usman —suka jagoranta.

Ɗaliban sun bayyana cewa yajin aikin da ƙungiyar ASUU ke shiga lokaci zuwa lokaci a dalilin taƙaddama da gwamnati yana gurgunta makomar karatunsu da kuma ilimi a ƙasar baki ɗaya.

Ƙungiyar ɗaliban ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da cika duk wata yarjejeniyar da ta ƙulla da ASUU, tana mai cewa muddin aka samu wani abu akasin haka, to babu shakka lamarin zai ci gaba da kawo tasgaro a harkokin ilimi a faɗin ƙasar.

Ɗaliban sun tunatar da duk masu ruwa da tsakin cewa ba su halin karatu a jami’o’in masu zaman kansa ballantana fita neman ilimi a ƙasashen ƙetare irin su Birtaniya, Indiya ko Amurka kamar yadda suke gani ’ya’yan masu hannu da shuni suna yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani Tsohon Ma’aikacin CIA Ya Ce HKI Ta Yi Barazanar Amfani Da Makaman Nukliya Kan Iran
  • ’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin su
  • Sace ɗalibai: Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi
  • CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara
  • Iran Ta yi Gargadi Game Da Sakamakon Da  Zai Iya Faruwa A Yankin Bayan Shigar Isra’ila Kasar Siriya
  • Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai
  • Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka
  • Labanon Ta Bukaci Gudanar Da Taron Kwamitin Tsaro Na MDD Cikin Gaggawa
  • Daraktar Hukumar IAEA Ya Ce: Suna Tuntubar Juna Da Iran Kuma Masu Bincikensu Sun Kamo Kasar
  • Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa