Syria: Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai Suna Ci Gaba Da Kai Wa Kauyukan Lazikiyya Da Tartus Hare-hare
Published: 9th, March 2025 GMT
Tashar talbijin din ‘almayadin’ mai watsa shirye-shirye daga Lebanon ta ambaci cewa; Wasu kauyuka na mabiya mazhabar Alawiyya dake Tartus, da kuma Lazikiyya, sun fuskanci hare-hare daga masu dauke da makamai.
A yau Lahadi, masu dauke da makaman sun kutsa cikin wasu kauyukan Ramilah, Naq’a dake kusa da Jabalah.
Daga jiya zuwa yau masu dauke da makaman sun yi kisan kiyashi a wurare fiye da 10.
Majiyar Almayadin ta ce ya zuwa yanzu adadin wadanda aka kashe bisa bangaranci sun kai 1000.
Sai dai kuma tshohon mai bai wa shugaban majalisar ‘yan Alawiyya shawara Muhammad Nasir, ya ce, adadin wadanda aka kashe din sun kai 1,700.
Hare-haren sun hada da kona kauyuka 6 a yankin gabar ruwan Midtreniya na kasar Syria.
Da akwai wasu daruruwan gawawwaki a kwance akan titunan garuruwa da kauyuka da biranen yakin Lazikiyya da Hasakah.
A cikin wasu kauyukan mutane da dama sun gudu zuwa kan duwatsu da dajuka domin su tsira da rayukansu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka
Marubuci kuma mai lambar yabo ta Nobel, Wole Soyinka, ya ce kamata ya yi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya tura ɗansa, Seyi Tinubu, zuwa Jamhuriyar Benin domin “kwantar da” yunƙurin juyin mulki da bai yi nasara ba.
Soyinka ya soki matakin Tinubu na tura dakarun rundunar Sojojin Sama ta Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin bayan yunƙurin juyin mulki da aka yi domin kifar da Shugaba Patrice Talon daga mulki.
Ya yi wannan jawabi ne a bikin bayar da kyaututtuka na shekara karo na 20 da Cibiyar Binciken Kwakwaf ta Wole Soyinka (WSCIJ) ta shirya a Legas ranar Litinin.
Fitaccen marubucin ya tuna yadda ya ga jami’an tsaro masu makamai sosai suna gadin Seyi Tinubu a Legas.
Ya ce: “Shugaba Tinubu bai kamata ya tura Sojojin Sama da na ƙasa ba domin shawo kan wannan tayar da hankali da ke barazana ga tsaronmu da daidaituwarmu; a’a akwai hanyoyi mafi sauƙi na yin hakan.
“Bari in gaya muku inda Tinubu ya kamata ya nemi rundunar da za ta shawo kan wannan tayar da hankali, na nan a Legas ko ma a Abuja, amma babu buƙatar kiran sojojin ƙasa ko na sama.
“Zan gaya muku abin da ya faru a ɗaya daga cikin ziyarata zuwa gida watanni biyu da suka gabata, ina fita daga wani otel sai na ga abin da ya yi kama da wurin yin fim, wani matashi ya rabu da ’yan wasan ya zo ya gaishe ni cikin ladabi.
“Na kalli wurin sai na ga kusan rundunar sojoji ce gaba ɗaya sun mamaye filin otel ɗin a Ikoyi. Na koma cikin motata na tambaya wanene wannan matashin, sai aka gaya min.
“Na ga sojoji, haɗin jami’an tsaro masu makamai sosai, akalla 15 suna ɗauke da manyan makamai, abin da ya isa ya tsare karamar makwabciya kamar Benin.
“Na yi tunanin cewa a gaba mai girma shugaban ƙasa ya kamata kawai ya kira ya ce ‘Seyi je ka kwantar da fitina a can’. Na yi matuƙar mamaki har na fara neman Mashawaracin Shugaban Kasa a fannin tsaro,” in ji Soyinka.
Soyinka ya kuma ce ba Tinubu ne shugaban da ya fara mulkar Najeriya yana da ’ya’ya ba, don haka bai ga dalilin da zai sa a girke tarin jami’an tsaro kawai don su rika gadin dansa ba.