Syria: Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai Suna Ci Gaba Da Kai Wa Kauyukan Lazikiyya Da Tartus Hare-hare
Published: 9th, March 2025 GMT
Tashar talbijin din ‘almayadin’ mai watsa shirye-shirye daga Lebanon ta ambaci cewa; Wasu kauyuka na mabiya mazhabar Alawiyya dake Tartus, da kuma Lazikiyya, sun fuskanci hare-hare daga masu dauke da makamai.
A yau Lahadi, masu dauke da makaman sun kutsa cikin wasu kauyukan Ramilah, Naq’a dake kusa da Jabalah.
Daga jiya zuwa yau masu dauke da makaman sun yi kisan kiyashi a wurare fiye da 10.
Majiyar Almayadin ta ce ya zuwa yanzu adadin wadanda aka kashe bisa bangaranci sun kai 1000.
Sai dai kuma tshohon mai bai wa shugaban majalisar ‘yan Alawiyya shawara Muhammad Nasir, ya ce, adadin wadanda aka kashe din sun kai 1,700.
Hare-haren sun hada da kona kauyuka 6 a yankin gabar ruwan Midtreniya na kasar Syria.
Da akwai wasu daruruwan gawawwaki a kwance akan titunan garuruwa da kauyuka da biranen yakin Lazikiyya da Hasakah.
A cikin wasu kauyukan mutane da dama sun gudu zuwa kan duwatsu da dajuka domin su tsira da rayukansu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Magance Matsalar Yara Da Ba Sa Zuwa Makaranta: Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyarwa A Makarantun Jihar
A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, ƙaddama da shirin na nuni da ƙwazon gwamnatinsa na yin aiki tare da masu ruwa da tsaki domin aiwatar da dabaru daban-daban na ƙara yawan ɗalibai a makarantun jihar Zamfara.
Ya ci gaba da cewa, “Alƙawarinmu na yin garambawul ya haɗa da tsare-tsare na yaƙi da rugujewar sassan ilimi da samar da haɗin gwiwa, kamar Bankin Duniya ta hanyar shirin AGILE da kuma UNICEF. A kwanakin baya Ma’aikatar Ilimi, Kimiya da Fasaha tare da haɗin gwiwar UNICEF, sun kafa wani kwamitin fasaha na shugabannin hukumomin da masu ruwa da tsaki domin ziyartar mananan hukumomi 14, da tantance yaran da ba su zuwa makaranta, da kuma tabbatar da shigar su makarantu.
“Shirin ciyar da ɗalibai a makarantu da muke ƙaddamarwa a yau, wani bangare ne na shirye-shiryen bayar da agajin gaggawa na inganta rajista da kuma riƙe ɗalibai a makarantu tare da yaƙi da yunwa da rashin abinci mai gina jiki. Wannan baya ga ƙoƙarin mu da wasu ƙungiyoyi masu zaman kansu guda biyu, Cibiyar Ci Gaban Tattalin Arziki ta Ƙasa da Ƙasa da Gidauniyar FINPACT, waɗanda suka amince da tallafa wa gwamnati wajen aiwatar da shirin domin yin aiki a matsayin tushen ilimi.
“A cikin sharuɗɗan, gidauniyar FINPACT za ta ɗauki nauyin ciyar da ɗalibai 1000 a Gusau, Maru, Anka, da Talatar Mafara, yayin da Cibiyar Raya Tattalin Arziki ta Duniya ke ɗaukar nauyin ciyar da ɗalibai 3300 a faɗin Gusau, Talatar Mafara, da Shinkafi.
“Ina kira ga duk masu ruwa da tsaki da sauran hukumomin bayar da agaji da su ƙara binciko hanyoyin samar da ƙarin ayyuka da shirye-shirye, wanda ba wai kawai hakan zai ƙara ƙaimi wajen samar da ilimi mai inganci ba ne, amma zai rage adadin yaran da ba su zuwa makaranta, ta yadda tare za mu mai da jiharmu ta zama abin koyi.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp