Tashar talbijin din ‘almayadin’ mai watsa shirye-shirye daga Lebanon ta ambaci cewa; Wasu kauyuka na mabiya mazhabar Alawiyya dake Tartus, da kuma Lazikiyya, sun fuskanci hare-hare daga masu dauke da makamai.

A yau Lahadi, masu dauke da makaman sun kutsa cikin wasu kauyukan Ramilah, Naq’a dake kusa da Jabalah.

Daga jiya zuwa yau masu dauke da makaman sun yi kisan kiyashi a wurare  fiye da 10.

Majiyar Almayadin ta ce ya zuwa yanzu adadin wadanda aka kashe bisa bangaranci sun kai 1000.

Sai dai kuma tshohon mai bai wa shugaban majalisar ‘yan Alawiyya shawara Muhammad Nasir, ya ce, adadin wadanda aka kashe din sun kai 1,700.

Hare-haren sun hada da kona kauyuka 6 a yankin gabar ruwan Midtreniya na kasar Syria.

Da akwai wasu daruruwan gawawwaki a kwance akan titunan garuruwa da kauyuka da biranen yakin Lazikiyya da Hasakah.

A cikin wasu kauyukan mutane da dama sun gudu zuwa kan duwatsu da dajuka domin su tsira da rayukansu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu

Majalisar Dattawa ta amince da wani sabon ƙudiri da ke neman a gyara dokar yaƙi da ta’addanci, domin a ɗauki garkuwa da mutane a matsayin babban laifi na ta’addanci.

Ƙudirin, wanda Sanata Opeyemi Bamidele ya gabatar, ya tanadi hukuncin kisa ga duk wanda aka kama da laifin satar mutane, ba tare da wata zaɓin tara ba.

Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja

Sanata Bamidele, ya ce ƙudirin ya yi daidai da yunƙurin gwamnati da majalisa na kawo ƙarshen matsalar tsaro a ƙasar nan.

Yayin gabatar da ƙudirin, ya ce garkuwa da mutane na ƙara yawaita, kuma ƙungiyoyin miyagu na amfani da shi wajen tara k6udi, abin da ke jefa jama’a cikin tsoro da kuma daƙile karatun yara a jihohi da dama.

Sanatoci da dama sun goyi bayan hukuncin kisa, inda suka bayyana cewa hakan zai zama gargaɗi ga masu aikata wannan mummunan laifi.

Wasu kuma sun nemi a hukunta bankunan da ke taimakawa wajen aikewa ko karɓar kuɗaɗen fansa, yayin da wasu suka ce ya kamata a daina yi wa ’yan ta’adda afuwa.

Majalisar ta tura ƙudirin zuwa kwamitoci na musamman domin bincike, tare da umarnin su kawo rahoto cikin makonni biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
  • Tsaro: Gwamnonin Arewa na shirin dakatar da haƙar ma’adinai
  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI
  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher CG Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi