Syria: Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai Suna Ci Gaba Da Kai Wa Kauyukan Lazikiyya Da Tartus Hare-hare
Published: 9th, March 2025 GMT
Tashar talbijin din ‘almayadin’ mai watsa shirye-shirye daga Lebanon ta ambaci cewa; Wasu kauyuka na mabiya mazhabar Alawiyya dake Tartus, da kuma Lazikiyya, sun fuskanci hare-hare daga masu dauke da makamai.
A yau Lahadi, masu dauke da makaman sun kutsa cikin wasu kauyukan Ramilah, Naq’a dake kusa da Jabalah.
Daga jiya zuwa yau masu dauke da makaman sun yi kisan kiyashi a wurare fiye da 10.
Majiyar Almayadin ta ce ya zuwa yanzu adadin wadanda aka kashe bisa bangaranci sun kai 1000.
Sai dai kuma tshohon mai bai wa shugaban majalisar ‘yan Alawiyya shawara Muhammad Nasir, ya ce, adadin wadanda aka kashe din sun kai 1,700.
Hare-haren sun hada da kona kauyuka 6 a yankin gabar ruwan Midtreniya na kasar Syria.
Da akwai wasu daruruwan gawawwaki a kwance akan titunan garuruwa da kauyuka da biranen yakin Lazikiyya da Hasakah.
A cikin wasu kauyukan mutane da dama sun gudu zuwa kan duwatsu da dajuka domin su tsira da rayukansu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
Wata gobara da ta tashi da safiyar Litinin ta kashe magidanci da matarsa da ’ya’yansa uku a unguwar Kofar Sauri da ke cikin garin Katsina.
Wadanda gobarar ta rutsa da su sun haɗa da Muhammad Habibu mai shekara 35, matarsa Fatima Muhammad, da ’ya’yansu uku; Khadija, Abubakar, da Aliyu, wadanda dukkansu suka ƙone har lahira.
Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan TsaroGobarar ta kuma lalata dukiyoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira.
An gano cewa Muhammad Habibu ma’aikaci ne na wucin gadi a hukumar ruwa ta jihar Katsina kafin rasuwarsa.
Kodayake ba a tabbatar da ainihin dalilin gobarar ba tukuna, mazauna yankin suna zargin ta faru ne sakamakon tashin wuta mai ƙarfi lokacin da aka dawo da lantarki a yankin.
An ce gobarar ta fara ne daga falon gidan sannan ta bazu cikin sauri zuwa sauran sassan gidan, yayin da iyalin ke tsaka da sharer barci.
Bayanai sun ce lokacin da suka fahimci hatsarin, wutar ta riga ta toshe dukkan hanyoyin fita.
Ɗan uwa ga waɗanda suka rasu, Kasim Aliyu, ya ce da misalin ƙarfe 3:00 na safe ya ji muryar wata mace daga nesa tana karanta kalmar shahada: “Innalillahi wa inna ilayhi raji’un.” Da farko ya ɗauka al’ada ce, sai da misalin ƙarfe 3:30 na safe ya fara jin akwai matsala.
Kasim ya ƙara da cewa: “Mai gidan ƙanina ne ubanmu ɗaya. Gobarar ta kama gidan da misalin ƙarfe 3:00 na safe. Na ji wani abu a lokacin amma ban gane ba sai da aka kira ni da misalin ƙarfe 4:00 na safe aka shaida min cewa ƙanina da iyalinsa gaba ɗaya sun mutu a gobarar. Allah ya jikan su.”
Shaidun gani da ido sun ce ƙoƙarin makwabta da masu taimakon gaggawa wajen kashe gobarar ya ci tura.
Sun yi korafin cewa jami’an hukumar kashe gobara ta jihar Katsina sun iso daga baya amma zuwan nasu bai yi wani tasiri ba sosai.
Wani mazaunin yankin, Musa Hamza, ya ce: “Ina ganin lokacin da hukumar kashe gobara ta iso, mutanen cikin gidan sun riga sun mutu a gobarar. Amma zan iya cewa sun yi iya ƙoƙarinsu wajen kashe wutar, sai dai ba su samu nasarar ceto iyalin ba. Allah ya jikan su.”
Wani makwabci, Magaji Bala, ya yi korafi cewa mazauna yankin sau da yawa suna shafe kwanaki ba tare da lantarki ba, sai kuma tashin wuta mai ƙarfi ya jawo barna duk lokacin da aka dawo da wuta.
“Irin wannan lamari ya taɓa faruwa a wasu sassan garin Katsina. Kwanan nan ma kusan irin haka ya faru. Wannan ya sa dole mutane su yi taka-tsantsan,” in ji shi.
Da aka tuntubi Babban Jami’in Kashe Gobara na jihar Katsina, Rabe Audi Kurmuyal, ya tabbatar da cewa ma’aikatansa sun kashe gobarar, sabanin ikirarin da ake yi cewa sun iso daga baya.
Wasu mazauna sun dora laifin kan matsalar sauyin wuta da ake yawan samu daga kamfanin rarraba na shiyyar Kano (KEDCO), suna cewa yawan katsewa da dawowa da ƙarfin lantarki mai yawa na lalata kayan lantarki.
Sai dai kamfanin ya musanta zargin, inda ya ca ba zai yiwu a ce laifinsu ba ne, kasancewar gidan shi kadai ya kone a unguwar mai gidaje sama da 5,000.