Syria: Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai Suna Ci Gaba Da Kai Wa Kauyukan Lazikiyya Da Tartus Hare-hare
Published: 9th, March 2025 GMT
Tashar talbijin din ‘almayadin’ mai watsa shirye-shirye daga Lebanon ta ambaci cewa; Wasu kauyuka na mabiya mazhabar Alawiyya dake Tartus, da kuma Lazikiyya, sun fuskanci hare-hare daga masu dauke da makamai.
A yau Lahadi, masu dauke da makaman sun kutsa cikin wasu kauyukan Ramilah, Naq’a dake kusa da Jabalah.
Daga jiya zuwa yau masu dauke da makaman sun yi kisan kiyashi a wurare fiye da 10.
Majiyar Almayadin ta ce ya zuwa yanzu adadin wadanda aka kashe bisa bangaranci sun kai 1000.
Sai dai kuma tshohon mai bai wa shugaban majalisar ‘yan Alawiyya shawara Muhammad Nasir, ya ce, adadin wadanda aka kashe din sun kai 1,700.
Hare-haren sun hada da kona kauyuka 6 a yankin gabar ruwan Midtreniya na kasar Syria.
Da akwai wasu daruruwan gawawwaki a kwance akan titunan garuruwa da kauyuka da biranen yakin Lazikiyya da Hasakah.
A cikin wasu kauyukan mutane da dama sun gudu zuwa kan duwatsu da dajuka domin su tsira da rayukansu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An kama ’yan Najeriya 3 a Kenya kan zargin aikata damfara
An kama ’yan Najeriya uku a rukunin gidaje na Mwaliko da ke garin Mwea a ƙasar Kenya, bisa zargin su da damfara ta intanet.
Rahoton da wata kafar labarai a Kenya mai suna Tuko News ta fitar ya ce Hukumar Binciken Laifuka ta ƙasar (DCI) ce ta kama waɗanda ake zargin a ranar Laraba.
Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030 Yahudawa sun banka wa masallaci wuta a Yammacin Kogin JodanWaɗanda aka kama sun haɗa da Peter Chukwujekwu, Alazor Chukulute Sunday, da Nnalue Chiagozie Samwe.
A cewar rahoton da aka fitar a ranar Alhamis, an kama su a gidansu bayan jama’a sun kai ƙorafi kan take-takensu musamman da daddare a cikin ginin.
DCI ta tabbatar da kama su, tana mai cewa an gudanar da “farmakin haɗin gwiwa tsakanin hukumomi da dama domin kama wata ƙungiyar masu damfara ta intanet” a yankin.
Rahoton ya ambato DCI tana cewa: “An kama ’yan Najeriya uku a wani farmakin haɗin gwiwa a Kirinyaga. Wannan farmaki da aka tsara sosai a rukunin gidaje na Mwaliko cikin garin Mwea ya tona asirin wata ƙungiyar masu damfara ta intanet da ’yan Najeriya uku ke gudanarwa.”
Waɗanda ake zargin sun ce suna gudanar da kasuwanci ta yanar gizo, amma rahoton ya nuna cewa suna zaune a Kenya ba tare da izini ba, kuma ba su da takardun aiki na doka.
Kamun nasu dai na cikin jerin kame-kamen da ake yi wa ’yan Najeriya a ƙasashen waje kan laifuka daban-daban, ciki har da damfara ta intanet, safarar miyagun ƙwayoyi, da safarar mutane.
Ko a watan Yunin 2023, sai da ’yan sandan a kasar ta Kenya suka kama ’yan Najeriya 19 a Nairobi, babban birnin kasar, bisa zargin damfara ta intanet da ke kai hari ga ’yan ƙasar.
A cewar DCI, mutanen da shekarunsu ke tsakanin 19 da 33, sun yi amfani da kafafen sada zumunta wajen fara damfarar, suna yaudarar ’yan Kenya da sunan za su tura musu kaya daga ƙasashen waje.