HausaTv:
2025-06-26@08:22:35 GMT

Araghchi Ya Tafi Saudiyya Domin Halartar Taron OIC

Published: 7th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya tafi kasar Saudiyya domin halartar taron ministocin kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC, domin tattauna matakan da za a dauka na tinkarar shirin Amurka na tilastawa mutanen Gaza gudun hijira.

A yammacin ranar Alhamis ne Araghchi ya tashi zuwa birnin Jeddah na kasar Saudiyya inda za a gudanar da taron a yammacin ranar Juma’a, in ji ma’aikatar harkokin wajen Iran.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baghaei ya ce Iran ta bukaci taron ne domin jawo hankalin kungiyar OIC, a matsayinta na babbar kungiya a duniyar musulmi, kan batun da ya shafi al’ummar musulmi da kasashen musulmi.

Shirin shugaban Amurka Donald Trump na raba Falasdinawan Gaza da kasarsu ta asali ya fuskanci tofin Allah tsine a duniya.

“Iran ne ta gabatar da bukatar taron domin martani wa shirin na Trump.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram

Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar ya da umarnin fara duban watan Muharram na sabuwar shekarar musulunci ta 1447 daga gobe Laraba, 29 ga watan Zulhijjan 1446, wanda ya yi daidai da 25 ga watan Yulin 2025.

Hakan na ƙunshe cikin wata takarda da Wazirin Sakkwato kuma shugaban kwamitin bai wa majalisar Sarkin Musulmi shawara kan harkokin addinin musulunci, Farfesa Sambo Wali Junaid ya raba wa manema labarai.

Harin asibiti ya kashe mutum 40 a Sudan — WHO EFCC ya kama manyan jami’an NNPC kan badaƙalar Dala 7.2bn

Sarkin Musulmi ya ce duk wanda ya samu ganin jinjirin watan ya sanar wa hakimi ko uban ƙasa mafi kusa da shi don sanar da majalisar sarkin musulmi.

A ƙarshe sanarwar ta ce Sarkin ya roƙi Allah Ya kawo wa Nijeriya zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa.

Watan Muharram dai shi na wata na farko kalandar Musulunci wanda ake maraba da zuwansa yayin da ake bankwana da shekarar musulunci ta 1446 Bayan Hijira.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma
  • Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci
  • Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci
  • Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato
  • PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta
  • PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta
  • Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
  • Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya
  • Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin