Ƙin yin sulhu da ’yan bindiga na haifar da alheri – Gwamnan Zamfara
Published: 6th, March 2025 GMT
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ce matsayarsa na ƙin amincewa a yi sulhu da ’yan bindiga na taimakawa wajen dawo da zaman lafiya a jihar.
Ya bayyana haka ne a ranar Alhamis yayin da yake karɓi baƙuncin Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Hassan Bala Abubakar.
An kama ’yan Pakistan biyu da laifin yin garkuwa a Legas HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Sheikh Hassan Jingir a JosAir Marshal Abubakar, ya ziyarci jihar domin yin ta’aziyya harin bam da rundunar sojin sama ta kai wa wasu mutane bisa kuskure.
Gwamna Lawal ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta canza matsayarta ba game da ƙin sasanci da miyagun mutane.
“Muna shaida wa kowa cewa ba za mu zauna da ’yan bindiga ba,” in ji shi.
“Hanyar da muka ɗauka tana haifar da sakamako mai kyau, kuma muna ganin zaman lafiya yana samuwa a Zamfara.”
Gwamnan ya kuma yaba da yadda jami’an tsaro ke hanzarin amsa kiran gaggawa a jihar.
“Ina gode wa Hafsan Sojin Sama saboda matakin gaggawa da ya ɗauka. Kafin wannan ziyarar, ya aike da manyan jami’ai domin jajanta mana.
“Wannan yana nuna ƙwazo da jajircewarsu wajen kare lafiyar mutanenmu,” in ji shi.
Hakazalika, Gwamna Lawal ya bayyana cewa ana gina sabon filin jirgin sama a Zamfara, kuma ya buƙaci a gina wajen ajiye jiragen rundunar sojin sama a ciki don ɗaukar matakan gaggawa kan matsalolin tsaro.
“Muna gina filin jirgin sama a Zamfara. Da zarar an kammala, muna fatan samun wajen ajiye jiragen sojin sama a cikinsa domin hanzarta ɗaukar matakan tsaro,” a cewarsa.
Air Marshal Hassan Abubakar ya gode wa gwamnan bisa yadda ya fahimci cewar harin da sojin rundunar suka kai ba da gangan ba ne.
Ya bayyana cewa sojojin sun kai hari ne bisa bayanan sirri kan ayyukan ’yan bindiga, amma daga baya aka gano cewa wasu ’yan sa-kai sun rasa rayukansu a dalilin harin.
Ya tabbatar wa mutanen Zamfara cewa rundunar sojin sama za ta ci gaba da inganta ayyukanta domin kauce wa irin wannan kuskure a nan gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gwamna Lawal Sakamako Mai Kyau Zamfara yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Yi Gargadi Game Da Sabawa Dokokin Fitillun Bada Hannu A Titinan Jihar
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayar da gargadi game da hawan keken masu kananan shekaru da rashin biyayya ga fitilun ababen hawa a cikin babban birnin Kano.
Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanya wa hannu, kuma aka rabawa manema labarai a Kano.
Gargadin na zuwa ne bayan an samu munanan hadurran kan tituna guda 16 a cikin watan Agustan 2025, wanda ya yi sanadin jikkata da asarar dukiyoyi.
Rundunar ta lura cewa hawan keken ƙananan yara yana haifar da babban haɗari ga mahaya da sauran masu amfani da hanyar.
An shawarci iyaye da masu kula da su da su guji barin ‘ya’yansu da ba su da shekaru su yi amfani da keken mai kafa uku, domin hakan zai jawo hukunci mai tsanani a karkashin dokar.
Rundunar ta kuma lura da yanayin rashin biyayya ga fitilun ababen hawa da kuma dokokin hanya daga wasu masu amfani da hanyar.
“Wannan dabi’a tana haifar da cunkoson ababen hawa da ba dole ba, da kuma hadurran da za a iya kaucewa, da jefa rayukan mutane cikin hadari da kuma kawo cikas ga zirga-zirgar ababen hawa.”
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kebe jami’an tsaro domin tabbatar da bin ka’idojin zirga-zirga.
Rundunar ta bukaci duk ‘yan kasar da su bi dokokin hanya da kuma bayar da rahoton duk wani abu na hawan keken kanana, tukin ganganci, ko wasu keta haddi.
Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaro na rayuka da dukiyoyi a jihar.
Abdullahi jalaluddeen/Kano