Kasar Masar Ta Tabbatrawa Falasdinawa, Tana Bayansu Kafin Taron Kasashe Larabawa
Published: 2nd, March 2025 GMT
Gwamnatin kasar masar ta tabbatarwa gwamnatin Falasdinawa kan cewa tana goyon bayan falasdinawa a cikin dawo da hakkinsu, na kafa kasarsu mai cikekken yanci wacce take da gabacin birnin Qudus a matsayin babban birnin Kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Mostafa Madbouly ministan harkokin wajen kasar Masar yana fadar haka a lokacin ganawarsa da tokwaransa na gwamnatin Falasdinawa a Ramallah Mohammada Mustafa a birnin Alkahira.
Madbouly ya kara da cewa gwamnatin kasar Masar tana son ganin an gaggauta sake ginza Gaza da kuma maida rayuwa kamar yadda take a gaza da gaggawa.
Ya ce kasashen larabawa ba zasu taba yarda da kasar Falasdina kasa da yarjeniyar 4 ga watan Yunin shekara ta 1967.
A ranar Talata 4 ga watan Maris da muke ciki ne za’a gudanar da taron gaggawa na kungiyar kasashen larabawa a birnin Alkahira na kasar Masar don tattauna halin da Falasdinawa suke ciki musamman a Gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Masar
এছাড়াও পড়ুন:
Firaministan Singapore: Jama’ar Sin Suna Da Kwarewar Kirkire-Kirkiren Fasahohi
Firaministan kasar Singapore, Lawrence Wong, ya yi hira da wata wakiliyar CMG a kwanan baya, inda ya ce, yana da cikakken imani kan kasar Sin, saboda jama’ar kasar suna da kwarewar kirkire-kirkiren sabbin fasahohi da hikimar daidaita al’amura. A cewarsa, kokarin neman ci gaban harkoki da jajircewa na al’ummar Sin sun sa shi dakon ganin makomar kasar Sin mai cike da haske.
Wong ya kara da cewa, ya taba cudanya da jami’an gwamnatin kasar Sin na matakai daban daban a shekarun baya, wadanda suka nuna kwarewar aiki da hazaka a fannin fahimtar ayyuka. Ban da haka, Wong ya ce, jami’an kasar Sin suna son sauraron ra’ayoyi na bangarori daban daban, da kokarin neman dabara mafi dacewa wajen daidaita matsala. A cewarsa, nagartaccen tsarin gudanar da mulki ya shafi tantance ayyukan da ake gudanar da su, da koyon sabon ilimi don inganta harkoki a-kai-a-kai, kana dukkan wadannan abubuwa ana iya ganinsu cikin tsarin gudanar da mulki na kasar Sin.
Bayan haka, dangane da matakin karbar karin harajin fito kan kayayyakin sauran kasashe da kasar Amurka take yi, mista Lawrence Wong ya ce, idan Amurka za ta iya nuna sanin ya kamata, da saukin kai wajen duba ma’anar manufar kare moriyar kanta, to, za ta ga damar samun dimbin alfanu na hakika, ta hanyar kasancewa cikin tsarin cinikin duniya da ake amfani da shi yanzu. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp