Leadership News Hausa:
2025-11-03@11:22:40 GMT

Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha

Published: 28th, February 2025 GMT

Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha

Yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da Sergei Shoigu, sakataren majalisar tsaro ta kasar Rasha, a nan birnin Beijing.

Yayin ganawar, Xi Jinping ya ce, Sin da Rasha sun kasance masu tuntubar juna a dukkan matakai, da aiwatar da matsayar da suka cimma da shugaba Putin da hadin gwiwa mai muhimmanci da moriyar juna tare da zurfafa hadin gwiwarsu a kai a kai, domin taimakawa muradunsu na bai daya na samun ci gaba da farfado da kasashen biyu.

Ya kara da cewa, ya kamata kasashen 2 su karfafa hadin kai a harkokin da suka shafi yanki da ma duniya, su kuma goyi bayan rawar da kasashen BRICS da kungiyar hadin kai ta Shanghai suke takawa, tare da karfafa saita alkiblar hadin gwiwa da goyon bayan juna tsakanin kasashe masu tasowa.

A nasa bangare, Sergei Shoigu ya ce, Sin da Rasha sun kai wani matsayi da ba a taba gani ba, kuma ba su yi hakan don muzgunawa wata kasa ba. Ya ce, haduwar Sin da Rasha ta taka muhimmiyar rawa a duniya, kuma ta nuna misalin dangantaka tsakanin manyan kasashe. Ya ce, Sin da Rasha za su ci gaba da kasancewa masu aminci da juna da tattaunawa bisa daidaito, kuma muhimmin hadin gwiwar dake tsakaninsu, ya dace da muradunsu na bai daya. Bugu da kari, ya ce, Rasha za ta aiwatar da muhimman yarjejeniyoyin da shugabannin kasashen 2 suka cimma tare da karfafa dangantakarta da Sin. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Sin da Rasha

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Wannan mataki ne awanni kaɗan bayan ɓangaren Damagum ya dakatar da Anyanwu da wasu mutane uku, lamarin da ya ƙara ta’azzaea rikicin shugabanci a cikin jam’iyyar PDP.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami November 1, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su November 1, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC