Leadership News Hausa:
2025-08-08@14:37:40 GMT

David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa – Amorim

Published: 22nd, February 2025 GMT

David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa – Amorim

Kocin Manchester United Ruben Amorim ya bayyan cewar Kocin ƙungiyar ƙwallon kafa ta Everton David Moyes ba mutum ne wanda za a raina iyawarshi a harkar kwallon ƙafa ba, David Moyes ya na yin aiki mai kyau na farfado da Everton fiye da yadda na ke yi cikin ƙanƙanin lokaci a Old Trafford inji Amorim.

Amorim zai fafata da Kocin Everton Moyes a ranar Asabar yayin da yake kokarin fitar da United daga koma bayan da ta ke fuskanta, tsohon kocin na Sporting Lisbon ya lashe wasanni huɗu ya yi rashin nasara a wasanni takwas a wasannin gasar Firimiya 12 da ya jagoranci Manche’ster United tun bayan zuwanshi a watan Nuwamba.

Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu

Moyes, wanda United ta sallama a shekarar 2014 bayan ƙasa da shekara guda yana jan ragamar horar da ‘yan wasan, tuni ya samu adadin nasarorin da Amorim ya samu tun bayan zuwanshi Old Trafford duk da cewa wasanni shida kacal ya jagoranta tun bayan komawarsa Everton a watan Janairu.

Everton, a matsayi na 14, tana sama da United wadda ta ke matsayi na 15 a teburin Firimiya gabanin haduwar kungiyoyin na karshe a Goodison Park,Everton wadda akewa lakabi da Toffees za su koma wani sabon filin wasa a kakar wasa mai zuwa.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta hana jagoran adawa Maurice Kamto takarar shugaban ƙasa a Kamaru

Kotun tsarin mulkin Kamaru ta haramta wa jagoran adawar ƙasar, Maurice Kamto tsayawa takarar shugaban ƙasa, a babban zaɓe mai zuwa na watan Oktoba, kan abin da ta bayyana rashin cika ka’idojin tsayawa takara.

Lauyansa, Hippolyte Meli Tiakouang ne ya tabbatar wa manema labarai hukuncin kotun wanda ba za a iya ƙalubalanta ba, bayan kammala zamanta na wannan Talata.

A cewarsa, kotun ta yi watsi da ƙarar da suka shigar kan matakin hukumar zaɓen ƙasar na cire shi daga cikin jerin ’yan takarar da za su fafata a zaɓen ranar 12 ga watan Oktoban bana.

Mulkin Tinubu ya fi na Buhari muni — Maina Waziri ’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu

Mista Kamto mai shekaru 71, ya yi ƙaurin suna wajen sukar gwamnatin shugaba Paul Biya, kuma shi ne ya yi na biyu a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2018, bayan tsayawa takara a jam’iyyar MRC.

A wannan karo kuma ya nemi tsayawa takarar a jam’iyyar MANIDEM, inda ya bayyana muradin tsayawar watanni biyar da suka gabata.

Hukumar zaɓen ƙasar ta yanke hukuncin cire Kamto saboda “’yan takara masu yawa,” bayan wani ɗan takara daga wani tsagin jam’iyyar ya miƙa buƙatar makamanciyar wannan, wanda ya sa ake nuna damuwa kan halascin shugabancin jam’iyyar.

Bayan gabatar da hukuncin, Kamto wanda da alama bai ji daɗin hakan ba, ya fice daga harabar kotun ba tare da magana da ’yan jarida ba.

Hukuncin da aka yanke a ranar Talata ya ƙara tayar da fargabar hargitsi.

An jibge jami’an tsaro a kusa da cibiyar taro da ke babban birnin ƙasar, Yaoundé, inda Kwamitin Kundin Tsarin Mulki ya bayyana hukuncin, da kuma manyan titunan birnin.

A ranar da ta gabata, ’yan sanda sun harba hayaƙi mai sa hawaye tare da kama mutane da dama da suka fito zanga-zangar goyon bayan Kamto.

Lauyoyinsa waɗanda ba su yi ƙarin bayani kan mataki da za su ɗauka ba, sun ce Kamto ne zai bayyana matakin da zai ɗauka.

Masu suka na ganin cewa akwai wata maƙarƙashiya ne na kawar da ɗan siyasar daga zaɓen.

Duk da raɗe-raɗin rashin lafiya, yanzu haka shugaba Paul Biya mai shekaru 92, wanda ya shafe tsawon shekaru 43 yana mulkin Kamaru, zai sake neman wa’adi na takwas a kan karagar mulki ba tare da wata ƙwaƙƙwarar adawa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027
  • Mahaifin Ɗan Bello ya rasu
  • Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
  • Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki
  • IRGC: Bayan yakin Kwanaki 12 Yanayi Ya Sauya Zuwa Ga Amfani Ga Iran
  • Iran tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Tsakanun Kasashen Yankin
  • Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino da Kaka – Shettima
  • Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi
  • Kotu ta hana jagoran adawa Maurice Kamto takarar shugaban ƙasa a Kamaru