Leadership News Hausa:
2025-09-24@11:14:07 GMT

David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa – Amorim

Published: 22nd, February 2025 GMT

David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa – Amorim

Kocin Manchester United Ruben Amorim ya bayyan cewar Kocin ƙungiyar ƙwallon kafa ta Everton David Moyes ba mutum ne wanda za a raina iyawarshi a harkar kwallon ƙafa ba, David Moyes ya na yin aiki mai kyau na farfado da Everton fiye da yadda na ke yi cikin ƙanƙanin lokaci a Old Trafford inji Amorim.

Amorim zai fafata da Kocin Everton Moyes a ranar Asabar yayin da yake kokarin fitar da United daga koma bayan da ta ke fuskanta, tsohon kocin na Sporting Lisbon ya lashe wasanni huɗu ya yi rashin nasara a wasanni takwas a wasannin gasar Firimiya 12 da ya jagoranci Manche’ster United tun bayan zuwanshi a watan Nuwamba.

Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu

Moyes, wanda United ta sallama a shekarar 2014 bayan ƙasa da shekara guda yana jan ragamar horar da ‘yan wasan, tuni ya samu adadin nasarorin da Amorim ya samu tun bayan zuwanshi Old Trafford duk da cewa wasanni shida kacal ya jagoranta tun bayan komawarsa Everton a watan Janairu.

Everton, a matsayi na 14, tana sama da United wadda ta ke matsayi na 15 a teburin Firimiya gabanin haduwar kungiyoyin na karshe a Goodison Park,Everton wadda akewa lakabi da Toffees za su koma wani sabon filin wasa a kakar wasa mai zuwa.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gavi Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Yi Masa Tiyata

 

Gavi dai ba zai dawo ba sai a farkon shekarar 2026, shekarar da ake ganin kasar Sifaniya za ta kasance cikin kasashen da suka fi damar lashe gasar cin kofin duniya da za a buga a kasashen Amurka, Mexico da kuma Canada.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun ci ribar Naira biliyan 601 a watanni shidan farkon 2025 – Bankin GT
  • Gavi Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Yi Masa Tiyata
  • Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
  • An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya
  • Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
  • Bayan Mutuwar Wani Matashi, An Kafa Dokar Ta Baci A Yauri
  • Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC
  • Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri
  • Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI
  • 2027: ‘Ku Yi Zaɓe Bisa Ga Ra’ayin Kanku, Ba Lura Da Ƙabila Ko Yanki Ba’, – Atiku Ga ‘Yan Nijeriya