Taron dai na zuwa ne sa’o’i kadan bayan da majalisar dattawan kasar a ranar Laraba ta gayyaci shugabannin hukumar leken asiri don gudanar da bincike kan zargin da dan majalisar dokokin Amurka, Perry Scott ya yi na cewa, hukumar bayar da tallafi ta kasa da kasa ta Amurka, USAID na tallafa wa kungiyoyin ta’addanci ciki har da Boko Haram.

 

Da yake jawabi a zaman taron na ranar Laraba, Akpabio ya ce Nijeriya ba za ta bar Hukumar USAID ta ci gaba da aiki a Nijeriya ba idan aka same ta da laifin daukar nauyin ta’addanci.

 

Ya ci gaba da cewa, yana da muhimmanci Nijeriya ta tabbatar da gaskiyar wannan zargi.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci

Ƙasar Amurka ta amince ta sayar wa Najeriya makaman da kuɗinsu ya kai Dala miliyan 346, kwatankwacin Naira biliyan 530 don yaƙi da ta’addanci.

Makaman da za a siyar sun haɗa da bama-bamai da na’urorin kakkabo jiragen sama da jirage marasa matuka da sauran su.

NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai

A cewar Kamfanin Sarrafa Makamai na Amurka (DSCA), za a sayar wa Najeriya makaman ne domin tallafa wa shirinta na yaki da ’yan ta’adda da masu safarar miyagun ƙwayoyi.

Kamfanin ya sanar da cinikin ne a cikin wata sanarwa ranar Laraba.

A cewar sanarwar, Najeriya ta buƙaci sayen bama-bamai guda 1,002, na’urar kakkabo jirage guda 1,002, sai manyan bindigu guda guda 5,000 da sauran makamai.

Kazalika, Amurkar ta amince ta sayar wa Najeriya helikwaftocin kai hari guda 12 da sauran muggan makaman da darajarsu ta kai Dala miliyan 997 a 2022.

Kamfanin ya ce kamfanonin da aka amince wa su yi kwangilar dillancin makaman su ne Lockheed Martin da RTX.N da kuma BAE.

“Wannan cinikin zai taimaka wa bunƙasa hulɗar kasa da kasa da kuma manufofin Amurka a kan harkar tsaro da inganta alaƙa da Najeriya a matsayin babbar ƙawa a yanki Afirka yamma da hamadar Sahara,” in ji sanarwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu
  • Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci
  • Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukumar Rano Na Tsawon Watanni Uku
  • Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa
  • Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki
  • Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su
  • Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja
  • DAGA LARABA: Yadda sinadaran dandanon abinci ke yin illa ga lafiya
  • Tinubu Ya Sake Nada Dankaka A Matsayin Shugaban Hukumar Kula Da Da’ar Ma’aikata Ta Kasa