Asabar ne zaɓen ƙananan hukumomin Jihar Katsina
Published: 14th, February 2025 GMT
Kamar yadda doka ta tanada cewar duk wata ƙaramar hukumar a tabbatar da cewa zaɓaɓɓun shugabanni ne ke jagorancin ta.
Wannan ya sa Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Umar Dikko Raɗɗa ta shirya aiwatar da zaɓen ƙananan hukumomi 34 da ke faɗin jahar wanda hakan zai ƙara ba su damar cin gashin kan su kamar yadda dokar ƙasa ta tanadar.
Kamar yadda shugaban Hukumar zaɓen mai zaman kanta ta Jihar Alhaji Lawal Alhassan Faskari ya shaidawa manema labarai a lokacin da ake rarraba kayan zaɓen zuwa ƙananan hukumomin jihar ya ce, tuni hukumar zaɓen ta kammala duk wasu shirye-shirye don ganin anyi zaɓen bisa doka.
Hakan ya sa aka ba kowace jam’iya damar fito da wanda zai yi mata takarar kujerar ƙaramar hukumar ko ta Kansila. Sai dai abin da mafi yawan jama’a suka yi tsammani cewar babbar jam’iyar adawa ta PDP ba za ta shiga zaɓen ba bisa dalilanta na cewa, ba sahihin zaɓe ne za a yi ba.
Duk da hakan bai hana wasu jam’iyun shiga cikin wannan zaɓe ba. Jam’iyar Accord da Booth da AAC da ADC sun shiga cikin wannan zaɓe.
Dangane da wuraren da ake fama da matsalar tsaro kuwa, an shirya gudanar da yin zaɓukan su a wasu wurare da aka tanada a yankunansu kamar yadda aka yi a zaɓukan da suka gabata.
Duk da haka kuma hukumomin tsaro a jihar sun ja hankali tare da gargaɗi ga masu ƙoƙarin kawo wata fitina da gargaɗin su ko su fuskanci fushin hukuma.
Kazalika, an hana zirga zirgar ababen hawa in baya ga na musamman da kuma masu gudanar da aiyukan zaɓen.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
Haka kuma wasu hukumomin gwamnati sun taimaka, ciki har da Hukumar ‘Yan Gudun Hijira ta Ƙasa, Hukumar Shige da Fice, Hukumar Tsaro ta DSS, Hukumar Lafiya ta Tashar Jirgin Sama da Rundunar ‘Yansanda.
Mutane biyu daga cikin waɗanda aka dawo da su na fama da matsananciyar rashin lafiya, kuma an garzaya da su asibitin New Ikeja don a duba lafiyarsu.
Bayan an yi musu rijista da ɗaukar bayanan yatsunsu, an mayar da su cibiyar mazauna ‘yan gudun hijira da ke Igando, a Jihar Legas, inda za su samu taimako don ci gaba da rayuwa.
NEMA ta ce wannan wani ɓangare ne na ƙoƙarinta na tallafa wa ‘yan Nijeriya da ke cikin mawuyacin hali a ƙasashen waje da kuma taimaka musu su farfaɗo da rayuwarsu cikin aminci a gida.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp