Aminiya:
2025-06-23@00:49:24 GMT

Asabar ne zaɓen ƙananan hukumomin Jihar Katsina 

Published: 14th, February 2025 GMT

Kamar yadda doka ta tanada cewar duk wata ƙaramar hukumar a tabbatar da cewa zaɓaɓɓun shugabanni ne ke jagorancin ta.

Wannan ya sa Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Umar Dikko Raɗɗa ta shirya aiwatar da zaɓen ƙananan hukumomi 34 da ke faɗin jahar wanda hakan zai ƙara ba su damar cin gashin kan su kamar yadda dokar ƙasa ta tanadar.

Mutum 23 sun mutu da raunata wasu a haɗarin mota a gadar Kano Shugaban Ƙungiyar Afenifere, Adebanjo ya rasu

Kamar yadda shugaban Hukumar zaɓen mai zaman kanta ta Jihar Alhaji Lawal Alhassan Faskari ya shaidawa manema labarai a lokacin da ake rarraba kayan zaɓen zuwa ƙananan hukumomin jihar ya ce, tuni hukumar zaɓen ta kammala duk wasu shirye-shirye don ganin anyi zaɓen bisa doka.

Hakan ya sa aka ba kowace jam’iya damar fito da wanda zai yi mata takarar kujerar ƙaramar hukumar ko ta Kansila. Sai dai abin da mafi yawan jama’a suka yi tsammani cewar babbar jam’iyar adawa ta PDP ba za ta shiga zaɓen ba bisa dalilanta na cewa, ba sahihin zaɓe ne za a yi ba.

Duk da hakan bai hana wasu jam’iyun shiga cikin wannan zaɓe ba. Jam’iyar Accord da Booth da AAC da ADC sun shiga cikin wannan zaɓe.

Dangane da wuraren da ake fama da matsalar tsaro kuwa, an shirya gudanar da yin zaɓukan su a wasu wurare da aka tanada a yankunansu kamar yadda aka yi a zaɓukan da suka gabata.

Duk da haka kuma hukumomin tsaro a jihar sun ja hankali tare da gargaɗi ga masu ƙoƙarin kawo wata fitina da gargaɗin su ko su fuskanci fushin hukuma.

Kazalika, an hana zirga zirgar ababen hawa in baya ga na musamman da kuma masu gudanar da aiyukan zaɓen.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka

Hukumar da ke kula da kafar yaɗa labarai ta Muryar Amurka (VOA) ta sallami ƙarin ’yan jarida da sauran ma’aikata 639 a ranar Juma’a.

Hukumar Kula da Harkokin Watsa Labarai ta Duniya ta Amurka (USAGM) ta bayyana cewa kawo yanzu an sallami ma’aikata 1,400 a wani bangare na shirin Shugaban Amurka Donald Trump na rage ma’aikata a hukumar zuwa mafi ƙarancin adadi kamar yadda doka ta tanada.

Hakan na nufin an kori mutum takwas a cikin kowane ma’aikata 10 da ke VOA a wata uku da suka gabata, a sakamakon wannan matakin Hukumar USAGM ta ɗauka.

Babbar Mashawarciya ga Hukumar, Kari Lake, ta bayyana cewa, “An aika wa ma’aikata 639 a VOA da USAGM da takardun kora a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin da ya kamata a yi tun da daɗewa don kawar da dimbin ma’aikata cima-zaune da kuma rashin riƙon amana a hukumar,” in ji sanarwar da ta fitar.

Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila 2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya

Lake ta kuma tabbatar da cewa hukumar ta kasance “cike da jami’an da ba sa aiki komai, nuna son kai, da ɓarnatar da dukiya.”

Ta bayyana cewa wannan mataki na nufin USAGM yanzu tana aiki kusa da mafi ƙarancin ma’aikata 81 da doka ta tanada.

Ma’aikata 250 kuma za su ci gaba da zama a Ofishin Watsa Labarai na Cuba (OCB), wanda ke watsa labarai zuwa ƙasar Cuba mai mulkin kwaminisanci.

An lura cewa babu ko ɗaya daga cikin ma’aikata 33 na OCB da aka kora.

Wannan mataki mai yiwuwa alama ce ta kusan kawo ƙarshen wannan shahararren gidan rediyo VOA wanda miliyoyin mutane ke saurara tsawon shekara 50 a faɗin duniya.

VOA, wadda aka kafa a 1942 don yaƙar farfagandar Nazi, tana watsa shirye-shirye a kusan harsuna 50 kuma ta mutane miliyan 360 ke sauraron shirye-shiryenta a mako, a faɗin duniya.

A watan Mayu aka kori ma’aikatan kwangila kusan 600 na VOA.

Wasu ’yan jam’iyyar Republican a baya sun zargi tashar da sauran kafofin yaɗa labarai masu samun tallafin gwamnati da nuna son kai ga masu ra’ayin mazan jiya, suna masu kira da a rufe tashar a matsayin wani ɓangare na rage kashe kuɗin gwamnati.

Wata tashar USAGM, Radio Free Asia, wadda tuni aka rage ma’aikatanta sosai, ta sanar a cikin wani sakon imel ga ma’aikata a ranar Juma’a cewa tana aiwatar da karin hutun tilas a sassa daban-daban.

Ana ci gaba da shari’o’i daban-daban kan lamarin korar ma’aikatan na USAGM.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato
  • An yi ma’aikatan ƙananan hukumomin Gombe ƙarin albashin N5,000
  • Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
  • An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka
  • Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila
  • Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
  • Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina