Asabar ne zaɓen ƙananan hukumomin Jihar Katsina
Published: 14th, February 2025 GMT
Kamar yadda doka ta tanada cewar duk wata ƙaramar hukumar a tabbatar da cewa zaɓaɓɓun shugabanni ne ke jagorancin ta.
Wannan ya sa Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Umar Dikko Raɗɗa ta shirya aiwatar da zaɓen ƙananan hukumomi 34 da ke faɗin jahar wanda hakan zai ƙara ba su damar cin gashin kan su kamar yadda dokar ƙasa ta tanadar.
Kamar yadda shugaban Hukumar zaɓen mai zaman kanta ta Jihar Alhaji Lawal Alhassan Faskari ya shaidawa manema labarai a lokacin da ake rarraba kayan zaɓen zuwa ƙananan hukumomin jihar ya ce, tuni hukumar zaɓen ta kammala duk wasu shirye-shirye don ganin anyi zaɓen bisa doka.
Hakan ya sa aka ba kowace jam’iya damar fito da wanda zai yi mata takarar kujerar ƙaramar hukumar ko ta Kansila. Sai dai abin da mafi yawan jama’a suka yi tsammani cewar babbar jam’iyar adawa ta PDP ba za ta shiga zaɓen ba bisa dalilanta na cewa, ba sahihin zaɓe ne za a yi ba.
Duk da hakan bai hana wasu jam’iyun shiga cikin wannan zaɓe ba. Jam’iyar Accord da Booth da AAC da ADC sun shiga cikin wannan zaɓe.
Dangane da wuraren da ake fama da matsalar tsaro kuwa, an shirya gudanar da yin zaɓukan su a wasu wurare da aka tanada a yankunansu kamar yadda aka yi a zaɓukan da suka gabata.
Duk da haka kuma hukumomin tsaro a jihar sun ja hankali tare da gargaɗi ga masu ƙoƙarin kawo wata fitina da gargaɗin su ko su fuskanci fushin hukuma.
Kazalika, an hana zirga zirgar ababen hawa in baya ga na musamman da kuma masu gudanar da aiyukan zaɓen.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
Rahotanni na cewa ’yan bindiga sun sace wasu mutum takwas a garin Biresawa da ke Karamar Hukumar Tsanyawa ta Jihar Kano a daren jiya na Litinin.
Wata majiyar da ta tabbatar da lamarin ta shaida wa Aminiya cewa maharan sun shiga garin tsakanin 11 na dare zuwa 12 na tsakar dare, inda suka yi awon gaba da maza biyu da mata shida.
’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun TuraiWani ɗan uwa ga waɗanda aka sace, Kabiru Usman, ya ce maharan sun zo ne a ƙafa ɗauke da makamai, suka kuma yi garkuwa da matarsa Umma, ɗiyarsa mai shekara 17, da matar ɗan’uwansa da wasu mata biyu daga Tsundu mai makwabtaka.
Ya ce al’ummar garin sun yi ƙoƙarin daƙile harin amma suka kasa saboda ƙarancin makamai, duk da cewa sun sanar da ’yan sanda da sojoji tun kafin faruwar harin bayan samun bayanan cewa ’yan bindigar na dosar yankin.
Ya roƙi gwamnati ta ɗauki mataki wajen ceto mutanen da aka sace da kuma kare rayukan mazauna yankin.
Aminiya ta yi ƙoƙarin ji ta bakin Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa, sai da har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba.