Jami’ar Tarayya Ta Lafiya Ta Rantsar Dalibai Dubu 8
Published: 14th, February 2025 GMT
Jami’ar Tarayya ta Lafia ta yi bikin rantsar dalibai 8,000 da suka sami gurbin karatu a sassan 76 a tsakanin tsangayoyin jami’ar 12.
Da yake jawabi a wajen bikin, Shugaban jami’ar Farfesa Shehu Abdul-Rahman, ya sake jaddada matsayar hukumar a kan duk wani nau’i na rashin da’a da kuma shiga kungiyoyin asiri.
Shugaban jami’ar wanda mataimakin shugaban jami’ar na sashen koyarwa, Farfesa Alemchi Chuku ya wakilta ya ci gaba da cewa basu da hakuri ga duk wani nau’i na rashin da’a kuma za su yi kakkausar suka ga munanan dabi’u.
Ya kuma bukaci sabbin daliban da su mutunta juna da kuma ma’aikatan jami’ar da malamai na jami’ar domin ganin zamansu ya kasance mai amfani.
“Ba mu yarda da ayyukan kungiyoyin da suka saba wa zamantakewa ba, musamman duk wanda aka kama yana gudanar da ayyukan kungiyar asiri za a kore shi daga jami’ar.
COV/Aliyu Muraki/Lafia./Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna
Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari wasu ƙauyuka biyu da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna.
A yayin harin, wata matar aure ta rasu, yayin da wani manomi ya samu rauni.
’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba SaniHarin farko ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na daren ranar Asabar, 21 ga watan Yuni, 2025, a ƙauyen Ungwan Sarkin Hausa da ke Rimau.
Ana zargin maharan sun gudu da shanun da suka sato daga Ƙaramar Hukumar Kauru.
A lokacin harin, sun kashe wata mata mai suna Misis Alheri Danzaria.
Sun kuma sace wasu mutum biyu, amma daga baya suka sake su.
Hari na biyu ya faru ne da safiyar ranar Lahadi da misalin ƙarfe 7 a ƙauyen Kallah.
A nan ne suka harbi wani manomi mai suna Mista Iliya Barde, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa gona.
An garzaya da shi asibiti inda yake samun kulawar likitoci.
Shugaban gundumar Kufana, Mista Stephen Maikori, ya ce hare-haren da ake yawan kai wa sun haddasa tsoro da damuwa a tsakanin mazauna yankin.
Ya buƙaci gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa wajen ƙara tsaro a yankin.
Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya ce zai bincika lamarin sannan ya bayar da amsa, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto bai yi ƙarin haske ba.