Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-24@18:28:51 GMT

Jami’ar Tarayya Ta Lafiya Ta Rantsar Dalibai Dubu 8

Published: 14th, February 2025 GMT

Jami’ar Tarayya Ta Lafiya Ta Rantsar Dalibai Dubu 8

 

Jami’ar Tarayya ta Lafia ta yi bikin rantsar dalibai 8,000 da suka sami gurbin karatu a sassan 76 a tsakanin tsangayoyin jami’ar 12.

 

Da yake jawabi a wajen bikin, Shugaban jami’ar Farfesa Shehu Abdul-Rahman, ya sake jaddada matsayar hukumar a kan duk wani nau’i na rashin da’a da kuma shiga kungiyoyin asiri.

 

Shugaban jami’ar wanda mataimakin shugaban jami’ar na sashen koyarwa, Farfesa Alemchi Chuku ya wakilta ya ci gaba da cewa basu da hakuri ga duk wani nau’i na rashin da’a kuma za su yi kakkausar suka ga munanan dabi’u.

 

Ya kuma bukaci sabbin daliban da su mutunta juna da kuma ma’aikatan jami’ar da malamai na jami’ar domin ganin zamansu ya kasance mai amfani.

 

“Ba mu yarda da ayyukan kungiyoyin da suka saba wa zamantakewa ba, musamman duk wanda aka kama yana gudanar da ayyukan kungiyar asiri za a kore shi daga jami’ar.

 

COV/Aliyu Muraki/Lafia./Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lafiya nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Mika Gaisuwar “Bikin Girbi Na Manoman Kasar Sin” Na Takwas

Yayin da “bikin girbi na manoman kasar Sin” na takwas ke karatowa, babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin wato JKS, shugaban kasar, kuma shugaban kwamitin kolin soja Xi Jinping, a madadin kwamitin kolin JKS, ya mika gaisuwar bikin, da fatan alheri ga manoma da ma’aikatan dake gudanar da ayyukan da suka shafi harkokin noma, da kauyuka da kuma manoma a fadin kasar.

Xi Jinping ya yi nuni da cewa, a bana, mun shawo kan illar bala’o’i kamar fari, da ambaliyar ruwa, da samun daidaiton noman hatsin rani, da karuwar noman shinkafa mai nuna da wuri, ana kuma sa ran samun karin girbin hatsi.

Xi Jinping, ya jaddada cewa, zamanantarwa irin ta kasar Sin ba za a iya raba ta da zamanantar da aikin gona da kauyuka. Don haka dole ne kwamitocin JKS, da gwamnatoci na sassan kasar su aiwatar da shawarwari da tsare-tsare na kwamitin kolin JKS, da tsayawa tsayin daka wajen raya aikin gona da kauyuka, da kyautata manufofi don karfafawa, da amfana, da wadatar da manoma, da karfafa goyon bayan kayayyakin aikin gona na kimiyya da fasaha, da mayar da hankali kan inganta cikakken karfin samar da amfanin gona, da aiwatar da matakai da dama don inganta ayyukan yi, da kara samun kudin shiga na manoma, da kuma sa kaimi ga farfadowar kauyuka a dukkan fannoni. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Tsaron Amruka Sun Kai Hari Ofishi Da Gidan John  Bolton
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda
  • An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya
  • Xi Jinping Ya Mika Gaisuwar “Bikin Girbi Na Manoman Kasar Sin” Na Takwas
  • Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya
  • Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina
  • An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike
  • Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri
  • Shettima ya tafi New York don halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya