Tirela ta murƙushe mutane a Gadar Hotoro a Kano
Published: 14th, February 2025 GMT
Ana fargabar mutane da dama sun rasu bayan wata tirela ta murƙushe su a Gasar Muhammadu Buhari da ke yankin Hotoro a a Jihar Kano.
Tirelar ta kife ne bayan da ta kwace a ƙarƙashin gadar, a hanyarta ta zuwa Kudancin Najeriya daga Yankin Arewa maso Gabas.
Wani ganau ya bayyana cewa kimanin mutane 20 da kaya ne ke cikin motar a lokacin da ta kife, inda wasu daga cikinsu suka rasu suka jikkata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hatsari
এছাড়াও পড়ুন:
Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
Wata kotu da ke birnin Madrid ta yi watsi da ƙarar da Hukumar ƙwallon ƙafa ta Nahiyyar Turai UEFA, LaLiga da Hukumar Kwallon Kafa ta Sipaniya suka shigar kan ƙin amincewa da gasar Super League.
Wannan yana nufin yanzu Real Madrid da sauran ƙungiyyoyin za su iya neman diyyar kudi Euro Milyan 4.
Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar Christopher MusaReal Madrid ta ce, wannan hukuncin ya tabbatar da cewa UEFA ta karya dokokin gasa, kuma ƙungiyyoyi sun rasa maƙuden kuɗaɗe tun daga lokacin da aka dakatar da gasar.
Gasar wacce aka shirya farawa a shekarar 2021 tare da manyan ƙungiyoyin Turai, an yi hasashen zata samar da kusan Yuro miliyan 200 ga ƙungiyoyin da suka shiga.
A nata martanin hukumar UEFA ta dage cewa wannan sabon hukuncin ba ya nufin an dawo ko an amince da a buga gasar Super League ba ne.