Ana nuna damuwa akan karancin kayan gwajin HIV a Taraba
Published: 14th, February 2025 GMT
Kungiyoyin farar hula masu yaki da zazzabin cizon sauro, rigakafi da abinci mai gina jiki (ACOMIN), reshen jihar Taraba, ta koka kan matsalar karancin kayan gwajin cutar kanjamau a jihar.
Shugaban kungiyar na jiha, Alhaji Muhammad Danburam ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar wayar da kan hukumar yaki da cutar kanjamau ta Taraba (TACA), ofishin kula da magunguna masu muhimmanci, da gidauniyar REDAID Nigeria Foundation.
Danburam ya bayyana cewa, wani bincike da aka yi kwanan nan a wasu cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko guda 18 a kananan hukumomin Ardo-kola, Bali, da Takum, ya nuna cewa kayan gwajin cutar kanjamau sun kare a cibiyoyin.
“Rashin kayan gwajin zai kawo cikas ga kokarin yaki da yaduwar cutar kanjamau a jihar,” in ji Danburam.
Ya yi kira ga gwamnatin jihar da masu ruwa da tsaki da su dauki matakin gaggawa don magance karancin.
A jawabinsa, Ko’odinetan Sashen Gudanar da Dabaru (LMCU) na Jiha, Pharm. Pinkai Bade, ya bukaci ‘yan kasar da su jajirce wajen tabbatar da samar da wadannan kayyakin tare da bayyana cewa tsarin samar da kayayyaki na da matukar kalubale sakamakon dakatar da tallafin da Amurka ke ba Najeriya.
Ya kuma yi nuni da cewa, Nijeriya ta himmatu wajen ganin an cike gibin da ke tattare da cutar kanjamau da kuma cimma nasarar rigakafin kamuwa da cutar daga uwa zuwa yara (PMTCT) nan da shekarar 2030.
Hukumar kula da fasaha ta REDAID ta Najeriya, Mista Stanley Nfor, da sakataren hukumar yaki da cutar kanjamau ta Taraba (TACA), Mista Bala Zugyeri, sun bayyana cewa, masu hannu da shuni kadai ba za su iya biyan bukatar kayayyakin gwaji da sauran muhimman kayayyaki ba, inda suka jaddada bukatar tallafin gwamnati.
Karshe/Jamila Abba/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Taraba cutar kanjamau kayan gwajin
এছাড়াও পড়ুন:
Ƙarancin abinci: UNICEF ta tallafawa yara 600,000 a Borno, Yobe
Asusun kula da Ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya bayar da rahoton samun gagarumin ci gaba a ƙoƙarin da take yi na ceto rayukan ƙananan yara.
Da kuma samar da damammakin ci gaba a jihohin Borno da Yobe duk da ƙalubalen da ke tattare da tashe-tashen hankula da talauci, UNICEF ta samu gagarumar nasara a jihohin.
Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya ’Yan sanda sun kashe ’yan fashi da ƙwato makamai a KadunaShugaban ofishin UNICEF na Maiduguri, Joseph Senesie ne ya bayyana hakan a jawabin da ya yi a lokacin wani taron tattaunawa da manema labarai kan ɗa’ar aikin jarida da rahoton kare haƙƙin yara a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe.
A cewarsa, a shekarar 2024 UNICEF ta tallafawa jinyar yara kimanin dubu 600 da ke fama da matsanancin halin rashin abinci mai gina jiki, tare da yi wa yara miliyan 1.2 allurar rigakafin cutar kwalara, tare da kai wa mutane miliyan 1.6 allurar rigakafin cutar kwalara.
Bugu da kari, an tallafa wa sama da yara rabin miliyan masu watanni 0-59 da rajistar haihuwa, kuma yara 500,000 sun samu ilimin boko a jihohin Borno da Yobe.
“Duk da haka, duk da waɗannan yunƙurin, ƙalubalen ya ci gaba ne kawai yadda yara 3 cikin yara 10 a Borno, Yobe, da Adamawa aka yi musu rajistar haihuwarsu. Duk da haka, kusan yara miliyan 2 ba sa zuwa makaranta a Arewa maso Gabas, wanda ke nuna buƙatar halin gaggawa na jin ƙai da ci gaba”.
Lamarin da ya ce ya ƙara dagulewa da matsalar ilimi, inda kashi 72 cikin 100 na ɗaliban da suka kammala firamare a yankin ba su iya karatu da rubutu ba, wadda wannan yana nuna babbar gazawa wajen ba da ilimi a matakin farko, kuma yana nuna buƙatar shiga lamarin cikin gaggawa.
UNICEF ta ci gaba da jajircewa wajen yin aiki tare da gwamnatoci da abokan hulɗa domin magance waɗannan ƙalubale.
Haka nan hukumar ta sadaukar da dala miliyan 270 don bayar da agajin jin ƙai da kawar da fatara a Najeriya, inda ta mayar da hankali kan ilimi da lafiya da kuma kariya ga yara masu rauni.