Ana nuna damuwa akan karancin kayan gwajin HIV a Taraba
Published: 14th, February 2025 GMT
Kungiyoyin farar hula masu yaki da zazzabin cizon sauro, rigakafi da abinci mai gina jiki (ACOMIN), reshen jihar Taraba, ta koka kan matsalar karancin kayan gwajin cutar kanjamau a jihar.
Shugaban kungiyar na jiha, Alhaji Muhammad Danburam ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar wayar da kan hukumar yaki da cutar kanjamau ta Taraba (TACA), ofishin kula da magunguna masu muhimmanci, da gidauniyar REDAID Nigeria Foundation.
Danburam ya bayyana cewa, wani bincike da aka yi kwanan nan a wasu cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko guda 18 a kananan hukumomin Ardo-kola, Bali, da Takum, ya nuna cewa kayan gwajin cutar kanjamau sun kare a cibiyoyin.
“Rashin kayan gwajin zai kawo cikas ga kokarin yaki da yaduwar cutar kanjamau a jihar,” in ji Danburam.
Ya yi kira ga gwamnatin jihar da masu ruwa da tsaki da su dauki matakin gaggawa don magance karancin.
A jawabinsa, Ko’odinetan Sashen Gudanar da Dabaru (LMCU) na Jiha, Pharm. Pinkai Bade, ya bukaci ‘yan kasar da su jajirce wajen tabbatar da samar da wadannan kayyakin tare da bayyana cewa tsarin samar da kayayyaki na da matukar kalubale sakamakon dakatar da tallafin da Amurka ke ba Najeriya.
Ya kuma yi nuni da cewa, Nijeriya ta himmatu wajen ganin an cike gibin da ke tattare da cutar kanjamau da kuma cimma nasarar rigakafin kamuwa da cutar daga uwa zuwa yara (PMTCT) nan da shekarar 2030.
Hukumar kula da fasaha ta REDAID ta Najeriya, Mista Stanley Nfor, da sakataren hukumar yaki da cutar kanjamau ta Taraba (TACA), Mista Bala Zugyeri, sun bayyana cewa, masu hannu da shuni kadai ba za su iya biyan bukatar kayayyakin gwaji da sauran muhimman kayayyaki ba, inda suka jaddada bukatar tallafin gwamnati.
Karshe/Jamila Abba/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Taraba cutar kanjamau kayan gwajin
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta bayyana sabbin nasarorin da ta samu wajen yaƙi da laifuka a jihar, ta hanyar holen mutum 34 da ta kama da aikata laifuka daban-daban.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Rabi’u Muhammad, ya ce wannan ci gaba ya samu ne saboda sabbin dabarun aiki da kuma bayanan sirri da aka samu daga al’umma da hukumomin tsaro.
Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000A Anguwar Barnawa da wasu wurare a Kaduna, rundunar Operation Fushin Kada ta kama mutane 13 da ake zargi da aikata fashi da makami da satar wayoyi a otel-otel da gidaje.
An ruwaito sun taɓa kashe ɗan sanda a shekarar 2024, kuma suna samun bayanai daga dilolin miyagun ƙwayoyi a wuraren shaƙatawa. A
An ƙwato bindiga ƙirar gida, gatari da adduna 13, mota, kwamfuta huɗu, wayoyi 13 da talabijin huɗu.
Haka kuma, a Nunbu Bashayi da ke Sanga, an kama mutane bakwai da ake zargi da garkuwa da mutane tare da neman kuɗin fansa.
Dukkanimsu sun amsa laifinsu kuma ana neman ragowar waɗanda suke tsere.
A wani samame daban, ’yan sanda sun kama wasu mutane huɗu da ake zargi da aikata fashi, fyaɗe da damfara.
Sun saba kai hari gidajen mutane, ɗaukar kuɗaɗen mutane, aikata fyaɗe sannan su riƙa ɗaukar bidiyo tsoratar da mutane.
A Zariya kuwa, an kama wasu mutane tara da suka haɗa da maza da mata waɗanda ake zargi da yi wa direban Adaidaita sahu fashi ta hanyar zuba masa magani a abin sha.
Rundunar ta kuma kama wani likitan bogi mai suna Adamu Abubakar Muhammed wanda ya yi wa mutane tiyata ba tare da shaidar karatun likitanci ba.
Ya yi amfani da takardun bogi wajen yin aiki na tsawon wata guda kafin a gano shi.
Kwamishinan, ya ce duk waɗanda aka kama suna hannun rundunar, kuma za a gurfanar da su kotu bayan kammala bincike.
Ya gode wa jami’an tsaro da al’umma kan haɗin kai, inda ya yi da a ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin inganta tsaro a jihar da ƙasa baki ɗaya.