Sai dai kuma, bayan bayyana a taron da gwamnonin tafkin Chadi suka yi a Borno na cewa, tubabbun ‘yan ta’adda sama 5000 ne suka sake haduwa da iyalansu, Jabi ya ce; babu shakka wannan wani cin fuska ne ga fuskokin wadanda aka kashe da kuma jaruman sojojin da suka mutu.

Haka nan, ya kuma sake bayyana hadewar komawar tasu cikin al’umma a matsayin wani babban kuskure wajen aiwatar da manufofin da suka dace.

Ya kara da cewa, “Abin da ya kamata mu yi wa ‘yan ta’adda shi ne, mu tabbata sun girbi abin da suka shuka. Saboda haka, idan har da gaske muke wajen kawar da ta’addanci a fadin wannan kasa, ya kamata mu sanya ido yadda ya kamata. Bana goyon bayan wannan abu da ake kira; sake shigar da ‘yan ta’adda cikin al’umma da siyasa.

“Wannan ba daidai ba ne, kuskure ne. Wadannan mutane, babu wani ci gaba da za su kawo wa kasa ko al’ummar da ke cikinta, in ban da kara dagula al’amura da za su yi”, a cewarsa.

Jabi ya ci gaba da cewa, sakamakon ayyukan ‘yan ta’adda, manoman da ya kamata a ce suna samar wa al’umma abinci; suna can sansanonin ‘yan gudun hijira suna rayuwa cikin mawuyacin hali.

Wani dan asalin Jihar Yobe, wanda ba ya so a bayyana sunansa, saboda fargabar ramuwar gayya; ya nuna rashin jin dadinsa ga gwamnatin tarayya da na jihohi, dangane da shirin sake dawo da wadannan ‘yan ta’adda cikin al’umma.

Ya ce, kyautuwa ya yi gwamnatin tarayya a ce tuni ta kammala fatattakar wadannan ‘yan ta’adda, kafin ta kai ga fara aiwatar da wannan shi.

Shi ma a nasa vangaren, babban daraktan cibiyar kare hakkin al’umma (CISLAC), Auwal Musa Rafsanjani ya ce, mayar da ‘yan ta’addan da suka tuba, ba tare da sake tsugunar da wadanda ta’addacin ya shafa ba, abu ne da zai tava samun karvuwa ba.

Don haka, ya yi kira ga gwamnati da ta gurfanar da duk wadanda suka taka rawa wajen cin zarafin al’umma tare da tabbatar da adalci.

Sanusi Isa, daraktan kungiyar ‘Amnesty International’ ta kasa, shi ma ya yi magana makwatankwaciyar wannan, inda ya yi nuni da cewa, duk wadanda suka aikata laifuka; su fuskanci hukunci na gaskiya.

Sannan ya kara da cewa, dukkanin wadanda abin ya shafa da wadanda suka tsira da iyalansu, sun cancanci a yi musu adalci.

daya daga cikin Shugabannin al’ummar Chibok, Mutah Nkeki, ya bayyana ra’ayinsa a matsayin rashin adalci da gwamnati ta shirya a kan ‘yan asalin Chibok da sauran daukacin wadanda ta’addancin ya shafa.

Ya yi zargin cewa, ‘yan matan makarantar Chibok da Boko Haram suka sace a shekarar 2014, an hana su ganawa da shugabanni da kuma iyayensu, tun bayan da suka tsere daga hannunsu.

Har ila yau, ya kara da cewa, babban abin takaicin shi ne, faruwar lamarin ya jawo mutuwar iyaye dama, inda y ace wadanda ke raye; ba a bas u damar ganin ‘ya’yansu mata da suka kuvuta ko aka kuvutar da su ba.  

Da aka tuntuvi kwamishinan yada labarai da tsaron cikin gida na Jihar Borno, Farfesa Usman Tar; ya musanta dukkanin zarge-zargen.

Ya ce, savanin zargin da ake yi; gwamnati jihar ta bayar da makudan kudade, domin sake tsugunar da al’umma.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Tsaro yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

Ya ce har yanzu matsalar tsaro tana addabar sassan Nijeriya da dama, kuma ana yaudarar shugaban ƙasa game da hakan.

Ya ce, “Idan Shugaba Tinubu yana sauraron labarai masu daɗi kawai daga waɗanda ke son faranta masa rai, to yana rayuwa ne a cikin duhu.”

Abdullahi ya bayyana cewa al’umma da dama a Nijeriya har yanzu na fuskantar hare-haren ‘yan bindiga, kuma mutane na rayuwa cikin tsoro da fargaba.

Ya ce ba daidai ba ne a riƙa nuna kamar abubuwa sun inganta, alhalin jama’a na cikin hali na ƙunci ba.

Jam’iyyar ADC ta kuma soki gwamnatin Tinubu da cewa ba ta ɗauki matakan da suka dace ba wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Sun ce maimakon fadar shugaban ƙasa ta riƙa kare shugaban da labaran da ba su dace ba, kamata ya yi su mayar da hankali kan nemo hanyoyin da za su kawo zaman lafiya da tsaro ga ‘yan kasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
  • Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati