Aminiya:
2025-08-17@10:25:29 GMT

Hajjin 2025: Ana shirya wa shugaban NAHCON maƙarƙashiya – Musa Iliyasu

Published: 12th, February 2025 GMT

Jigo a jam’iyyar APC a Jihar Kano, Musa Iliyasu Kwankwaso, ya tabbatar da cewa Shugabancin Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan a Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ba zai gaza ba duk da ƙoƙarin yaɗa jita-jita da wasu ke yi.

Kwankwaso, ya musanta wani rahoto da ke cewa mahajjata na iya rasa zuwa aikin Hajjin 2025, inda ya bayyan cewar wannan ƙarya ce da aka shirya don yaudarar jama’a da kuma ɓata sunan shugaban NAHCON.

An yi wa kashi 25 na matan Nijeriya kaciya Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya

Ya buƙaci jama’a, musamman maniyyatan da za su yi aikin Hajjin 2025, da su yi watsi da wannan rahoto, inda ya Farfesa Pakistan yana da ƙwarewa wajen shirya aikin Hajji.

“Muna sane da jita-jitar da ake yaɗawa cewa dubban maniyyata na iya rasa zuwa aikin Hajjjin 2025.

“Wannan ƙarya ce da ake ƙoƙarin amfani da ita don kawo cikas ga Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan,” in ji Kwankwaso.

Ya zargi ’yan adawa da ɗaukar nauyin wannan jita-jita saboda tsoron nasarar da Farfesa Pakistan zai kawo tare da sauyi a tsarin aiki. Hajji.

“Muna da masaniya cewa wasu mutane na yaɗa labarai marasa tushe don ɓata masa suna.

“Manufarsu ita ce kawo cikas ga mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, amma ba za su yi nasara ba,” a cewarsa.

Kwankwaso, ya kuma bayyana cewa NAHCON ba ta soke kowace kwangila ba, inda ya alaƙanta hakan da ƙasae Saudiyya.

Ya bayyana cewa Farfesa Pakistan yana ƙasar Saudiya don warware matsalar lokacin da aka yaɗa rahoton na ƙarya.

Ya kuma tabbatar wa maniyyata cewa za a gudanar da Hajjjin 2025 cikin nasara.

“Ina kira ga duk maniyyata da su kwantar da hankalinsu. Farfesa Pakistan ya samu wannan muƙami ne saboda cancantarsa.

“Kuma yana da ƙwarewar da za ta sa a samu nasara. Babu wani maniyyaci da aka yi wa rijista da ba zai samu damar tafiya aikin Hajji ba,” in ji shi.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, shi ma ya bayyana cewa babu buƙatar mutane su shiga damuwa game da lamarin.

Ya kuma ya musanta zargin cewa kwangilar da aka bai wa wasu domin gudanar da aikin Hajjin bana na iya samu matsala.

Kwankwaso ya ƙarƙare da cewa waɗanda ke yaɗa jita-jitar suna ƙoƙarin hana gwamnati samun nasara ne, kuma a cewarsa burinsu ba zai cika ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan Maƙarƙashiya maniyyata Musa Iliyasu Kwankwanso Farfesa Pakistan

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse

Al’ummar garin Talasse da ke Ƙaramar Hukumar Balanga a Jihar Gombe, sun ce sun gaji da rayuwa cikin duhu har na tsawon shekaru 19.

Sun kuma bayyana takaicinsu bayan tsayawar aikin wutar lantarki da ya tsaya.

Ba a ba mu dala 100,000 da gwamnati ta mana alƙawari ba — Super Falcons NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe

Aikin, wanda ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Billiri da Balanga, Ali Isa JC, ya fara tun farkon wannan shekara, ya sanya al’ummar yankin farin ciki bayan an kafa turakun wuta da na’urorin taransifoma.

Sai dai cikin watanni biyu da suka gabata, aikin ya tsaya ba tare da wani bayani ba.

“Yan siyasa su kan zo da alƙawura a lokacin zaɓe, sannan su ɓace bayan sun yi nasara,” in ji Yakubu Ayuba, mazaunin Talasse.

Ya ce rashin wuta ya jawo durƙushewar kasuwanci da tattalin arziƙi a yankin, kuma hakan zai yi tasiri a zaɓen 2027.

Wani mai sana’ar ɗinki, Musa Adamu Galadima, ya ce: “Janerata ya fi ƙarfinmu. Na kori yaran da ke koyon sana’a saboda ba zan iya ɗaukar nauyinsu ba.”

Shi ma Sulaiman Idris, mai sayar da lemun kwalba, ya ce yana kashe kusan Naira 10,000 a rana wajen siyan ƙanƙara.

“Lokacin da aka kawo kayan aiki mun yi farin ciki, amma yanzu komai ya tsaya,” in ji shi.

Da aka tuntuɓi ɗan majalisar don jin ta bakinsa, Ali Isa JC, ya ce matsalar ta samo asali ne daga jinkirin sakin kuɗaɗen aikin daga Gwamnatin Tarayya, amma suna ƙoƙarin ganin aikin ya ci gaba.

A halin yanzu, gwamnatin Jihar Gombe ta fara aikin samar da wuta ta hanyar samar da ƙaramar madatsar ruwa da hasken rana a Dam ɗin Balanga, wanda zai iya samar da 620KW.

Duk da haka, jama’ar Talasse sun ce rashin wutar zai sa su ƙauracewa kaɗa ƙuri’a a zaɓen 2027.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Iran na Shirin fara wata muhimmiyar ziyara a Armenia da Belarus
  • An kama manyan shugabannin ’yan ta’addan ƙungiyar Ansaru — Ribadu
  • Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
  • Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
  • ASCSN Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Nada Muhammad Dagaceri Shugaban Ma’aikata
  • Gwamna Namadi Ya Nada Kwamishina Na Farko A Ma’aikatar Cigaban Kiwon Dabbobi
  • Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC
  • Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 
  • Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara
  • Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse