Hajjin 2025: Ana shirya wa shugaban NAHCON maƙarƙashiya – Musa Iliyasu
Published: 12th, February 2025 GMT
Jigo a jam’iyyar APC a Jihar Kano, Musa Iliyasu Kwankwaso, ya tabbatar da cewa Shugabancin Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan a Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ba zai gaza ba duk da ƙoƙarin yaɗa jita-jita da wasu ke yi.
Kwankwaso, ya musanta wani rahoto da ke cewa mahajjata na iya rasa zuwa aikin Hajjin 2025, inda ya bayyan cewar wannan ƙarya ce da aka shirya don yaudarar jama’a da kuma ɓata sunan shugaban NAHCON.
Ya buƙaci jama’a, musamman maniyyatan da za su yi aikin Hajjin 2025, da su yi watsi da wannan rahoto, inda ya Farfesa Pakistan yana da ƙwarewa wajen shirya aikin Hajji.
“Muna sane da jita-jitar da ake yaɗawa cewa dubban maniyyata na iya rasa zuwa aikin Hajjjin 2025.
“Wannan ƙarya ce da ake ƙoƙarin amfani da ita don kawo cikas ga Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan,” in ji Kwankwaso.
Ya zargi ’yan adawa da ɗaukar nauyin wannan jita-jita saboda tsoron nasarar da Farfesa Pakistan zai kawo tare da sauyi a tsarin aiki. Hajji.
“Muna da masaniya cewa wasu mutane na yaɗa labarai marasa tushe don ɓata masa suna.
“Manufarsu ita ce kawo cikas ga mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, amma ba za su yi nasara ba,” a cewarsa.
Kwankwaso, ya kuma bayyana cewa NAHCON ba ta soke kowace kwangila ba, inda ya alaƙanta hakan da ƙasae Saudiyya.
Ya bayyana cewa Farfesa Pakistan yana ƙasar Saudiya don warware matsalar lokacin da aka yaɗa rahoton na ƙarya.
Ya kuma tabbatar wa maniyyata cewa za a gudanar da Hajjjin 2025 cikin nasara.
“Ina kira ga duk maniyyata da su kwantar da hankalinsu. Farfesa Pakistan ya samu wannan muƙami ne saboda cancantarsa.
“Kuma yana da ƙwarewar da za ta sa a samu nasara. Babu wani maniyyaci da aka yi wa rijista da ba zai samu damar tafiya aikin Hajji ba,” in ji shi.
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, shi ma ya bayyana cewa babu buƙatar mutane su shiga damuwa game da lamarin.
Ya kuma ya musanta zargin cewa kwangilar da aka bai wa wasu domin gudanar da aikin Hajjin bana na iya samu matsala.
Kwankwaso ya ƙarƙare da cewa waɗanda ke yaɗa jita-jitar suna ƙoƙarin hana gwamnati samun nasara ne, kuma a cewarsa burinsu ba zai cika ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan Maƙarƙashiya maniyyata Musa Iliyasu Kwankwanso Farfesa Pakistan
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
Dabbobi sama da miliyan guda ne ake sa ran za a yi wa rigakafi a fadin karamar hukumar Babura da ke jihar Jigawa.
Shugaban karamar hukumar Babura, Alhaji Hamisu Muhammad Garu, ne ya bayyana hakan yayin kaddamar da aikin rigakafin dabbobi na bana.
A cewarsa, fiye da tumaki da awaki miliyan daya da shanu dubu ashirin ake sa ran za a yi wa rigakafi a fadin karamar hukumar.
Ya jaddada cewa karamar hukumar na da cikakken shiri da kudurin tallafawa sauyin noma na Gwamna Umar Namadi, domin inganta rayuwa da tattalin arzikin al’ummar jihar.
Shugaban ya jaddada muhimmancin masu kiwon dabbobi su bada hadin kai yayin aikin rigakafin domin tabbatar da lafiyar dabbobinsu.
Alhaji Hamisu Garu ya kuma nuna jin dadinsa game da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya a yankin, yana mai kira gare su da su ci gaba da gudanar da rayuwa cikin fahimta da hadin kai.
Haka zalika, yayin taron, Shugaban Sashen Noma da Albarkatun Kasa, Malam Lawan Sabo Kaugama, ya bayyana cewa an ware cibiyoyi guda goma sha biyu domin gudanar da aikin rigakafin wanda ake sa ran zai dauki kwanaki hudu.
Ya yaba da kokarin gwamnatin jiha da ta karamar hukuma wajen samar da allurar rrigakafn da kuma duk wasu kayan aiki da ake bukata.
Usman Muhammad Zaria