Aminiya:
2025-11-27@22:57:46 GMT

Hajjin 2025: Ana shirya wa shugaban NAHCON maƙarƙashiya – Musa Iliyasu

Published: 12th, February 2025 GMT

Jigo a jam’iyyar APC a Jihar Kano, Musa Iliyasu Kwankwaso, ya tabbatar da cewa Shugabancin Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan a Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ba zai gaza ba duk da ƙoƙarin yaɗa jita-jita da wasu ke yi.

Kwankwaso, ya musanta wani rahoto da ke cewa mahajjata na iya rasa zuwa aikin Hajjin 2025, inda ya bayyan cewar wannan ƙarya ce da aka shirya don yaudarar jama’a da kuma ɓata sunan shugaban NAHCON.

An yi wa kashi 25 na matan Nijeriya kaciya Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya

Ya buƙaci jama’a, musamman maniyyatan da za su yi aikin Hajjin 2025, da su yi watsi da wannan rahoto, inda ya Farfesa Pakistan yana da ƙwarewa wajen shirya aikin Hajji.

“Muna sane da jita-jitar da ake yaɗawa cewa dubban maniyyata na iya rasa zuwa aikin Hajjjin 2025.

“Wannan ƙarya ce da ake ƙoƙarin amfani da ita don kawo cikas ga Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan,” in ji Kwankwaso.

Ya zargi ’yan adawa da ɗaukar nauyin wannan jita-jita saboda tsoron nasarar da Farfesa Pakistan zai kawo tare da sauyi a tsarin aiki. Hajji.

“Muna da masaniya cewa wasu mutane na yaɗa labarai marasa tushe don ɓata masa suna.

“Manufarsu ita ce kawo cikas ga mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, amma ba za su yi nasara ba,” a cewarsa.

Kwankwaso, ya kuma bayyana cewa NAHCON ba ta soke kowace kwangila ba, inda ya alaƙanta hakan da ƙasae Saudiyya.

Ya bayyana cewa Farfesa Pakistan yana ƙasar Saudiya don warware matsalar lokacin da aka yaɗa rahoton na ƙarya.

Ya kuma tabbatar wa maniyyata cewa za a gudanar da Hajjjin 2025 cikin nasara.

“Ina kira ga duk maniyyata da su kwantar da hankalinsu. Farfesa Pakistan ya samu wannan muƙami ne saboda cancantarsa.

“Kuma yana da ƙwarewar da za ta sa a samu nasara. Babu wani maniyyaci da aka yi wa rijista da ba zai samu damar tafiya aikin Hajji ba,” in ji shi.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, shi ma ya bayyana cewa babu buƙatar mutane su shiga damuwa game da lamarin.

Ya kuma ya musanta zargin cewa kwangilar da aka bai wa wasu domin gudanar da aikin Hajjin bana na iya samu matsala.

Kwankwaso ya ƙarƙare da cewa waɗanda ke yaɗa jita-jitar suna ƙoƙarin hana gwamnati samun nasara ne, kuma a cewarsa burinsu ba zai cika ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan Maƙarƙashiya maniyyata Musa Iliyasu Kwankwanso Farfesa Pakistan

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro da ta addabi dukkan sassa a Nijeriya.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin wannan Larabar mai ɗauke da sa hannunsa, Tinubu ya bayyana cewa dole ne a ɗauki matakan gaggawa da suka dace domin fuskantar barazanar tsaro da ke ƙaruwa ƙasar nan.

Shugaban ya bayar da umarnin ɗaukar ƙarin jami’an tsaro da suka haɗa da jami’an ’yan sanda 20,000, lamarin da zai ƙara adadin jami’an da za a ɗauka zuwa 50,000, bayan umarnin da ya bayar a ranar Lahadi na ɗaukar jami’an tsaro 30,000.

Real Madrid za ta yi karon-batta da Olympiacos a Gasar Zakarun Turai Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu

Haka kuma, Tinubu ya bai wa rundunar sojin ƙasa da sauran hukumomin tsaro umarnin ɗaukar ƙarin jami’ai.

Sanarwar ta ce za a yi amfani da sansanonin masu yi wa ƙasa hidima NYSC a matsayin wuraren horas da sabbin ’yan sandan.

Kazalika, shugaban ya bai wa hukumar ’yan sandan farin kaya ta DSS umarnin ɗaukar ƙarin jami’ai a rundunar kare dazuka wato Dakarun Gandun Daji ta Forest Guard.

Shugaba Tinubu ya kuma umarci DSS ta aika dakarun Forest Guard “domin zaƙulo ’yan ta’adda da ’yan fashi daga dazuka.”

“Babu wani sauran gidan ɓuya ga miyagu,” in ji shi kamar yadda wata sanarwa daga fadar shugaban ta bayyana.

Sanarwar ta ƙara da cewar, za a sake horar da jami’an ’yan sanda da aka janye daga gadin fitattun mutane kafin mayar da su aikin ɗan sandan gada-gadan.

Shugaban ya yi amfani da damar wajen jinjinawa hukumomin tsaro wajen kuɓutar da mutane 34 da aka sace a Mujami’ar Kwara da ɗalibai 24 da aka sace a makarantar jihar Kebbi, yayin da ya ce suna ɗaukar matakan da suka dace wajen kuɓutar da ɗaliban makarantar mabiya ɗarikar Katolika da ke Jihar Neja.

Tinubu ya jinjinawa rundunar sojin ƙasar a kan gudumawar da jami’anta ke bayarwa da kuma gabatar da ta’aziyar rasuwar Janar Musa Uba da ƴanta’adda suka yiwa kisan gilla, yayin da ya buƙace su da su ƙara ƙaimi wajen tabbatar da tsaro a yankunan da ake fama da tashin hankali.

Shugaban ya buƙaci majalisar ƙasa da ta sake fasalin dokokin tsaro domin bai wa jihohi damar samar da ’yan sanda na kashin kan su, yayin da ya ce gwamnatin tarayya za ta taimaka musu.

Tinubu ya kuma buƙaci Masallatai da Majami’u da su dinga neman taimakon jami’an tsaro a duk lokacin da za su gudanar da taron ibadun su, musamman a yankunan da ake fama da matsalar tsaro.

Shugaban ya kuma jajanta wa gwamnatoci da kuma mutanen jihohin Kebbi da Borno da Zamfara da Neja da Yobe da kuma Kwara saboda kisan gillar da ƴan ta’adda suka yiwa mutanen su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa
  • Mali: An Dakatar Da  Aikin Kafafen Watsa Labarun Faransa Biyu A Cikin Kasar Mali