Masar Za Ta Karbi Bakuncin Taron Gaggawa Na Larabawa Kan Batun Falasdinu
Published: 10th, February 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen Masar ta sanar cewa, kasar za ta karbi bakuncin taron gaggawa na kasashen Larabawa a ranar 27 ga watan Fabrairun nan, domin tunkarar al’amura na baya-bayan nan da suka shafi batun Falasdinu da zirin Gaza.
Sanarwar ta ce, an yanke shawarar gudanar da taron ne bayan muhimman shawarwarin da Masar ta yi da kasashen Larabawa, ciki har da Falasdinu da ta bukaci gudanar da taron, tare da hadin gwiwar Bahrain.
A wani labarin kuma, kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ta yi kakkausar suka kan munanan kalamai da kuma rashin da’a da firaministan Isra’ila ya yi na yin kira da a kafa kasar Falasdinu a kasar Saudiyya.
A ranar Alhamis, ne Netanyahu ya ba da shawara yayin wata hira da tashar 14 ta Isra’ila cewa “Saudiyya za ta iya kafa kasar Falasdinu a Saudiyya, suna da kasa mai girma.”
Kungiyar ta OIC ta dauki wannan a matsayin tsokana ga Saudiyya, kuma cin zarafi ne ga ’yancin kai, tsaron kasa da kuma yankinta, da kuma keta dokokin kasa da kasa da kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya.
A yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa a birnin Washington da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ne a ranar Talata, shugaban Amurka Donald Trump ya ce Amurka na shirin “karbe ikon zirin Gaza,” da tura Falasdinawa zuwa kasashe makwabta, da kuma sake raya yankunan gabar tekun, kalaman na Trump da Netanyahu sun haifar da cece-kuce a yankin da ma duniya baki daya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya zanta da takwaransa na kasar Rasha, Vladimir Putin, ta wayar tarho a yau Jumma’a 8 ga wata.
A tattaunawarsu, Putin ya bayyana ra’ayin kasar Rasha dangane da rikicin Ukraine a halin yanzu, da yadda Rasha ta tuntubi Amurka kwanan nan, inda ya ce, Rasha ta yaba sosai da muhimmiyar rawar da kasar Sin take takawa a fannin shawo kan rikici ta hanyar siyasa.
A nasa bangaren kuma, Xi ya jaddada matsayin kasar Sin, tare da bayyana cewa babu wata dabara mai sauki da ke iya magance matsaloli masu sarkakiya. Ba tare da la’akari da duk wani sauyi da za a fuskanta ba, kasar Sin za ta tsaya ga neman sulhu da gudanar da shawarwari. Kazalika, Sin na fatan ganin Rasha da Amurka su rika tuntubar juna, da nufin kyautata dangantakarsu, da taimaka wa warware rikicin Ukraine ta hanyar siyasa.
Har wa yau, shugabannin biyu sun yaba da yadda kasashensu suka amince da juna ta fuskar siyasa da inganta hadin-gwiwa bisa manyan tsare-tsare, inda suka yarda da kara ciyar da dangantakarsu gaba. Sun ce za su kara hadin-gwiwa da juna wajen gudanar da taron kolin kungiyar hadin-kai ta Shanghai wato SCO a birnin Tianjin yadda ya kamata, da sa kaimin inganta ci gaban kungiyar. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp