Aminiya:
2025-06-15@23:03:37 GMT

Netanyahu ya gurfana a kotu kan karbar cin hanci

Published: 10th, February 2025 GMT

Fira Ministan Isra’ila, Banjamin Netanyahu, ya gurfana a kotu kan zargin aikata zamba da karbar cin hanci da rashawa.

An gurfanar da Mista Netanyahu ne daomin ya amsa tambayoyi a shari’ar da aka jima ana zargin sa da aikata manyan laifuka uku na cin hanci da cin amana.

Masu gabatar da kara na zargin sa da aikata laifukan da suka hada da karbar cin hanci da zamba da kuma cin amana.

Laifukan sun hada da sa da daga kafar harajin Dala miliyan 500 ga kamfanin sadarwa na Bezeq Telecom domin kamfanin ya tallata shi da matarsa Sara a wani shafin yada labarai. Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe ’Yan sanda na neman ’yan bola-jari ruwa a jallo a Abuja

A kan haka yake fuskantar zargin bayar da cin hanci da kuma cin amanar dukiyar al’umma da aka ba shi.

Ana kuma zargin shi da matarsa da karbar toshiyar baki ta Dalar Amurka 21,000 daga wani furodusa a masana’anatar fina-finan Amurka ta Hollywood, dan kasar Isra’ila mai suna Arnon Milchan, da wani attajirin kasar Australiya, James Packer.

Yana kuma fuskantar zargin kulla yarjejeniyar da mamallakin kamfanin jaridar Yedioh Ahronoth, Arnon Mozes, domin tallata shi, inda shi kuma zai yi dokar da za ta hana bunkasar wata jarida da ke gogayya da Yedioh Ahronoth.

A kan wannan kuma ana zargin Netanyahu da laifin zamba da kuma cin amana.

Tun shekarar 2020 Netanyahu yake fuskantar wadannan zarge-zarge, amma ya musanta aikata ba daidai ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Netanyahu

এছাড়াও পড়ুন:

Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga

An shiga zaman ɗari-ɗari a garin Makurdi na Jihar Benuwe, bayan ’yan sanda sun harba barkonon tsohuwa domin tarwatsa wasu masu zanga-zanga a shataletalen Wurukum.

Masu zanga-zangar sun fara taruwa da misalin ƙarfe 9:30 na safe domin nuna fushinsu kan kisan mutane sama da 100 a garin Yelewata da ke Ƙaramar Hukumar Guma, a ranar Asabar.

Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina

Tun kafin fara zanga-zangar, jami’an tsaro daga hukumomi daban-daban sun mamaye manyan hanyoyi a birnin Makurdi.

Da safiyar ranar Lahadi da misalin ƙarfe 7 na safe jami’an tsaro, ciki har da motar yaƙi ta ‘yan sanda sun yi wa wajen tsinke.

An kuma hango sojoji a gadar kusa da wajen, yayin da jami’an NDLEA, NSCDC da sauran hukumomi suka kasance ɗauke da manyan makamai.

Rahotanni sun nuna cewa wannan matakin tsaro an ɗauke shi ne don hana zanga-zangar, amma da mutane suka fara taruwa, ‘yan sanda sun harba barkonon tsohuwa da misalin ƙarfe 11 na safe domin tarwatsa su.

Duk da haka, masu zanga-zangar ba su karaya ba, yayin da wani shahararren mai fafutuka a kafafen sada zumunta, VeryDarkMan, ya jagoranci zanga-zangar.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Ifeanyi Enemari, ya isa wajen zanga-zangar sannan ya roƙi matasan da ke zanga-zangar da su zauna lafiya.

Ya ce jami’an tsaro na bakin ƙoƙarinsu don kawo ƙarshen kashe-kashen da ke faruwa a jihar.

Ya bayyana cewa Sufeto Janar na ’Yan Sanda ya tura rundunoni na musamman zuwa jihar domin taimakawa wajen tsaro, kuma wasu daga cikinsu sun isa jihar, sauran kuma na hanya.

Kwamishinan ya ce gwamnati ta bai wa jami’an tsaro goyon baya sosai kuma an riga an kama wasu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)