Aminiya:
2025-10-13@20:16:34 GMT

Tinubu ya yi sauye-sauye a Jami’ar Abuja

Published: 6th, February 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya sauke Aisha Maikudi daga muƙaminta na Shugabar Jami’ar Abuja, wadda yanzu ake kira da Jami’ar Yakubu Gowon.

Sanarwar sauke Maikudi ta fito ne jim kaɗan bayan ta jagoranci bikin maraba da sabbin ɗalibai a jami’ar.

Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a Bayelsa HOTUNA: Yadda gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Kano

Tun farko, naɗinta ya jawo ce-ce-ku-ce, inda wasu malaman jami’ar suka ce ba ta cancanta ta riƙe wannan matsayi bisa doka.

Tinubu ya naɗa Farfesa Lar Patricia Manko a matsayin Muƙaddashiyar Shugabar Jami’ar na tsawon watanni shida.

Sai dai ba za ta iya neman kujerar dindindin ba idan aka buɗe damar neman muƙamin.

 

Cikakken bayani na tafe…

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami ar Abuja Jami ar Yakubu Gowon Kora

এছাড়াও পড়ুন:

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Ta ce, “Dole ne akwai kalubale da dama, wanda daga cikinmu muke fuskanta a yayin shigowa wannan masana’anta, amma dai ni babu wani abu da zan iya tunawa, illa wani wanda na iske a masana’antar ya karbi zunzurutun kudi har Naira 50,000 a mabanbantan lokuta da sunan zai yi min rijista a masana’antar, kuma bai yi ba, daga karshe ma na gano cewa; kudin rijistar duka-duka Naira 5,000 ne.

 

A wata hira da Khadija ta yi da gidan Rediyon Hikima, ta bayyana cewa, matukar ta samu abin da ya kawo ta masana’antar (Kudi), to nan da shekara daya ma; za ta iya shiga daga ciki, ma’ana za ta samu miji ta yi aurenta na Sunna.

 

Khadija, wadda ta ce; ita haifaffiyar birnin Maiduguri ce ta Jihar Borno, wadda zama ya dawo da ita birnin Kanon Dabo, ta kuma bukaci masu kallon su da su dinga nuna musu soyayya kamar yadda suke nuna wa sauran jaruman duniya, musamman wadanda ke cikin masana’antar Bollywood ta Kasar Indiya.

 

“Akwai bukatar dukkaninmu, mu hada karfi da karfe don ganin mun taimaki junanmu, ba mu koma gefe muna zagin junanmu ba, abin da ya sa na fadi haka kuwa shi ne, akwai lokacin da wani ya zo neman aurena, amma wasu suka zagaya baya suka hure masa kunne a kan cewa; kada ya sake ya aure ni, saboda ni jarumar fim ce. Ta kara da cewa; mu ma Hausawa ne kamar mafi yawan masu kallonmu, sannan kuma bai kamata ku yi la’akari da duk wani abu da kuka gani a cikin fim, wajen yanke hukuncin cewa, halin dan fim kenan ko a zahiri ba.

 

Daga karshe, Khdadija ta ce; “Dukkanninmu ‘yan fim, muna kokari wajen ganin mun killace kanmu( Sirrinta al’amuranmu), domin kauce wa zargi, duk wani wanda ka ga yana fallasa halayensa na zahiri a shafukansa na sada zumunta, to ba dan fim ba ne, kawai yana zuwa neman taimako wajen masu shirya fina-finai ne su saka shi ya fito sau biyu ko sau uku a fim, domin su samu na cefane, amma ba lallai ne ya zama cikakaken dan fim ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Nishadi Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri? October 11, 2025 Nishadi Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano October 6, 2025 Nishadi An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana October 4, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3
  • ASUU ta tsunduma yajin aikin mako 2
  • Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace
  • Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • ASUU za ta fara yajin aikin mako 2 daga ranar Litinin
  • Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja
  • Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
  • Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida