Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-31@16:51:39 GMT

Muna Jaje Ga Masautar Zazzau – Manjo Janar Bello

Published: 3rd, February 2025 GMT

Kwamandan makarantar horas da sojoji dake Zaria, Manjo Janar Ahmadu Bello Mohammed ya yi alkawarin inganta dangantakar da ke tsakanin makarantar da majalisar masarautar Zazzau.

Ya bayyana haka ne lokacin da ya kai wa mai martaba Sarkin zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli ziyarar ban girma a fadar sa dake Zaria.

Manjo Janar Ahmadu Bello, wanda ya bayyana ziyarar a matsayin wani sabon babi a dangantakar daje tsakanin makarantar horas da kuratan da masarautar ta zazzau ya yi alkawarin bunkasa dangantakar dake tsakanin su,ya kuma bayyana cewa ya kai ziyarar ce domin neman albarka da hadin kan majalisar masarautar ta zazzau.

Kwamandan ya kuma mika ta’aziyar makarantar horas da kuratan sojojin ga masarautar ta zazzau bisa rasuwar daya daga cikin yan majalisar masarautar, Alhaji Rilwanu Yahaya Fate,Sarkin Yaki zazzau da ya rasu kwanan nan.

Da ya ke maida jawabi, mai martaba Sarkin zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya gode wa Kwamandan bisa ziyarar, ya kuma yi alkawarin baiwa makarantar ta Dapo duk goyon baya da hadin kai da suke bukata domin sauke nauyin dake kan su.

Mai martaban ya kara da cewa za a gudanar da tsare-tsaren da suka kamata domin daidaita batutuwan dake masarautar ta zazzau da masarautar horas da kuratan sojojin.

Haliru Hamza

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ta aziya masarautar ta zazzau

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

Amma yanzu, babu matsalar gaba ɗaya a ƙananan hukumomi 11, yayin da aka samu sauƙi a wasu tara.

Ya ce har yanzu ana fama da hare-hare a ƙananan hukumomi huɗu: Faskari, Ƙankara, Safana da Matazu.

Kwamishinan ya jaddada cewa jami’an tsaro suna iyakar ƙoƙarinsu, kuma gwamna yana ci gaba da tattaunawa da manyan jami’an tsaro domin kawo ƙarshen matsalar.

Ya buƙaci al’umma da su daina suka, su kuma tallafa wa jami’an tsaro da addu’a da fahimta, ganin irin sadaukarwar da suke yi domin kare rayukan jama’a.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  • Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati