Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-16@07:55:34 GMT

Muna Jaje Ga Masautar Zazzau – Manjo Janar Bello

Published: 3rd, February 2025 GMT

Kwamandan makarantar horas da sojoji dake Zaria, Manjo Janar Ahmadu Bello Mohammed ya yi alkawarin inganta dangantakar da ke tsakanin makarantar da majalisar masarautar Zazzau.

Ya bayyana haka ne lokacin da ya kai wa mai martaba Sarkin zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli ziyarar ban girma a fadar sa dake Zaria.

Manjo Janar Ahmadu Bello, wanda ya bayyana ziyarar a matsayin wani sabon babi a dangantakar daje tsakanin makarantar horas da kuratan da masarautar ta zazzau ya yi alkawarin bunkasa dangantakar dake tsakanin su,ya kuma bayyana cewa ya kai ziyarar ce domin neman albarka da hadin kan majalisar masarautar ta zazzau.

Kwamandan ya kuma mika ta’aziyar makarantar horas da kuratan sojojin ga masarautar ta zazzau bisa rasuwar daya daga cikin yan majalisar masarautar, Alhaji Rilwanu Yahaya Fate,Sarkin Yaki zazzau da ya rasu kwanan nan.

Da ya ke maida jawabi, mai martaba Sarkin zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya gode wa Kwamandan bisa ziyarar, ya kuma yi alkawarin baiwa makarantar ta Dapo duk goyon baya da hadin kai da suke bukata domin sauke nauyin dake kan su.

Mai martaban ya kara da cewa za a gudanar da tsare-tsaren da suka kamata domin daidaita batutuwan dake masarautar ta zazzau da masarautar horas da kuratan sojojin.

Haliru Hamza

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ta aziya masarautar ta zazzau

এছাড়াও পড়ুন:

Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

Ita jigida irin ta da ba haka kawai ake sakata ba, domin shahararru kuma jarumai ne a wacan lokacin suke yin ta don haka ne take da tasiri da kuma tsada ga masu saye.

Sai dai a baya akwai jigida ta ‘yan mata akwai ta matan aure da kuma na tsofaffi, kuma a wannan lokacin babu matsala ko wani gani-gani da ake yi wa macen da aka ganta sanye da jigida saboda abu ne da aka dauka na al’ada maimakon ado ko kiran maza da wasu ke ganin matan yanzu suke yi da jigida ba.

Yanzu dai sanya jigida ga mata ya bunkasa ya fadada har cikin kashen Turai. Matan turawa kamar yadda bincike ya tabbatar kashi 60 cikin 100 suna sawa.

Sai dai a wannan zamanin da muke ciki sanya jigida ga mata ya zama abin ado ne ba domin dalilai irin na camfi da muka ambata a baya da mutanen baya suke yi ba, duk da yake ana samun kadan daga cikin matan kauyawa masu saka jigida da manufa ta camfi.

Shima dai kamar irin na da ne, wannan zamanin ana yin jigida ne da wasu duwatsu masu kyalli da kuma robobi masu sheki wadanda nauyinsu bai kai irin na zamanin baya ba.

Babban alfanun da jigida yake yi wa mata kamar yadda bincike ya tabbatar a wannan lokacin shi ne, yana kara wa mace fadin kugunta ga irin matan nan da suke da karancisa.

Maza da dama da aka zanta da su sun nuna sha’awarsu ta ganin matansu na aure suna saka jigida domin yana karamusu kyau musamman idan mace tana sanye da kayan da za su bayyanasu.

Har ilayau cikin alfanun da jigida ke da shi shi ne ta kan motsa sha’awan maza a yayin da suka ji sautinsa ko suka hango shatinsa.

Sai dai duk da wadannan tasiri, mahimanci da alfanun da jigida ke da su ba duka mata bane suke sanyawa ba, haka ma maza da dama ba su son ganin mace da jigida. Wasu mutane sun riga sun kudura cewa duk mace ko budurwar da aka ga tana sa jigida ko aka ji sautinsa a tare da ita suna daukan irin wadannan matan mazinata ne.

Sannan kuma yanzu ana jigida ta mganin mata. Masu maganin mata sun samo yadda ake jigida da garin magani a maimakon duwatsun da ake yi da shi, sai a yi da maganin a ciccura ta kamar dutse sai a huda tsakiyar asa zare duk haka za’a jera su. Mata su daurashi a kugunsu yana maganin mata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
  • IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila
  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi