Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-12@05:02:09 GMT

Jami’ar Ahmadu Bello Ta Yaye Dalibai Fiye Da Dubu 20 a Bana

Published: 27th, January 2025 GMT

Jami’ar Ahmadu Bello Ta Yaye Dalibai Fiye Da Dubu 20 a Bana

Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Farfesa Kabiru Bala ya roki Majalisar Dokoki ta kasa da ta yi gyare-gyaren doka don ware cibiyoyin ilimi daga zama hukumomi masu samarda kudaden shiga.

 

Ya yi wannan roko ne a wajen bikin yaya=e dalibai karo na 44 da aka gudanar a dandalin Mamman Kontagora da ke Samaru a Zariya.

 

Shugaban jami’ar ya ce idan haka ta faru, jami’o’in za su mayar da hankali ne a matsayin manyan cibiyoyin kawo ci gaban kasa.

 

Ya yi nuni da cewa Jami’ar Ahmadu Bello kamar yadda jami’o’in Najeriya da dama ke fuskantar kalubalen kudi don tallafa wa manufofinta na ci gaba da zamanantar da ayyukanta.

 

Farfesa Bala ya yi magana ne game da umarnin kotun masana’antu ta kasa na a rufe asusun ajiyar jami’ar dake a babban bankin Najeriya ajiya wanda ke cike da kudi naira miliyan dubu biyu da miliyan dari biyar da tamanin da biyar.

 

Ya yi nuni rashin jin dadin ganin c ewa wannan asusun jami’ar da abin ya shafa ya kunshi wasu kudade na sassan daban daban kamar tallafin bincike na gida da na waje, kudade na sassan jami’ar da ke da alaka da bincike bincike.

 

Ya bayyana cewa, a sakamakon wannan odar, dukkan ayyukan da suka shafi kashe kudi kamar su tsaftar muhalli, wutar lantarki da sauran kayayyakin masarufi na fuskantar cikas.

 

Tun da farko a nasa jawabin, shugaban jami’ar kuma shugaban majalisar gudanarwar jami’ar, Alhaji Mahmood Yayale Ahmed ya ce tsarin jami’o’in Najeriya na fuskantar kalubale da suka hada da kudade, mulki da gudanarwa.

 

Don haka ya ba da shawarar samun ‘yancin kai na kuɗi don tabbatar da cewa jami’o’i sun kasance matattarar masana da kwararri da tunani da sabbin abubuwa.

 

Shima a nasa jawabin, Uban jami’ar, Obi na Onitsha, Nnaemeka Alfred Achebe, ya dorawa daliban da suka yaye aikin yin amfani da wannan karni na 21 a matsayin shekarun juyin zamani.

 

Bikin karo na 44, an yaye dalibai 21,952 da suka kammala karatun digiri na 2023/2024, daga cikinsu 5,756 sun sami digiri na biyu yayin da 16,196 suka sami digiri na farko.

 

COV/HALIRU HAMZA/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gidauniya ta yi wa masu cutar gwaiwa dubu 12 tiyata kyauta a Katsina

Gidauniyar attajirin ɗan kasuwar nan na Jihar Katsina, Alhaji Dahiru Mangal, ta yi wa masu fama da cutar gwaiwa da taruwar ruwa a wasu sassan jiki fiye da 12,300 tiyata kyauta.

Da yake yi wa wakilin bayani, Malam Husaaini Kabir, mamba a kwamitin amintattu na gidauniyar ne ya tabbatar da hakan a Katsina, a lokacin ƙaddamar da aikin kashi na biyu.

Za a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta Mata zuwa ƙasashe 48 — FIFA Sauya sheƙa bayan cin moriyar jam’iyya butulci ne — Kwankwaso

Kabir ya bayyana cewa gidauniyar tana gudanar da aikin tiyatar da bayar da magani kyauta a duk bayan watanni uku tun lokacin da aka kafa ta a shekarar 2013.

Ya ƙara da cewa, “majinyata masu rauni tsakanin 500 zuwa 600 ne ke cin gajiyar aikin tiyatar gwaiwar da na rage ruwan kyauta a jihar.

“Wannan shiri ba wai yana taimaka wa mutanen garin Katsina ne kawai ba, yana kuma tallafa wa mazauna ƙauyukan jihar da kuma yankunan da ke makwabtaka da su.

“Manufarmu ita ce rage nauyin biyan kuɗin kiwon lafiya ga mutane masu ƙaramin ƙarfi waɗanda ke gwagwarmaya don biyan buƙatun yau da kullun,” in ji shi.

Kabir ya buƙaci sauran ƙungiyoyi da masu hannu da shuni da su tallafawa irin wannan shiri, musamman don taimaka wa ƙoƙarin gwamnati a fannin kiwon lafiya.

Ya jaddada mahimmancin aikin tare don tunkarar ƙalubalen kiwon lafiya a cikin al’ummomin da ba a yi musu hidima ba.

Wasu da suka ci gajiyar shirin sun yaba da shirin tare da ƙarfafa gwiwar gwamnati, ƙungiyoyi masu zaman kansu, da masu hannu da shuni da su yi koyi da hakan.

Sun bayyana cewa sun jure yanayin da suke ciki na tsawon shekaru amma ba za su iya yin tiyatar ba saboda matsalar tattalin arziki.

Aminiya ta ruwaito cewa gidauniyar ta kuma bayar da maganin ido da tiyata kyauta ga marasa lafiyar idon a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta ce tattaunawa ta hudu da Amurka tana da wahala amma tana da amfani  
  • An kama matashi da kawunan mutane a Legas
  • An kama matashi da kawunan mutanen a Legas
  • Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu
  • Gidauniya ta yi wa masu cutar gwaiwa dubu 12 tiyata kyauta a Katsina
  • Jami’ar Colombiya Ta Birnin New York A Amurka Ta Dakatar Da Karatun Daliban Jami’ar Fiye Da 65
  • Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi
  • JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025
  • Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
  • NAJERIYA A YAU: Abin ya sa aka kasa kawo ƙarshen Tamowa a Arewa Maso Gabas