Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-27@23:26:46 GMT

Jami’ar Ahmadu Bello Ta Yaye Dalibai Fiye Da Dubu 20 a Bana

Published: 27th, January 2025 GMT

Jami’ar Ahmadu Bello Ta Yaye Dalibai Fiye Da Dubu 20 a Bana

Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Farfesa Kabiru Bala ya roki Majalisar Dokoki ta kasa da ta yi gyare-gyaren doka don ware cibiyoyin ilimi daga zama hukumomi masu samarda kudaden shiga.

 

Ya yi wannan roko ne a wajen bikin yaya=e dalibai karo na 44 da aka gudanar a dandalin Mamman Kontagora da ke Samaru a Zariya.

 

Shugaban jami’ar ya ce idan haka ta faru, jami’o’in za su mayar da hankali ne a matsayin manyan cibiyoyin kawo ci gaban kasa.

 

Ya yi nuni da cewa Jami’ar Ahmadu Bello kamar yadda jami’o’in Najeriya da dama ke fuskantar kalubalen kudi don tallafa wa manufofinta na ci gaba da zamanantar da ayyukanta.

 

Farfesa Bala ya yi magana ne game da umarnin kotun masana’antu ta kasa na a rufe asusun ajiyar jami’ar dake a babban bankin Najeriya ajiya wanda ke cike da kudi naira miliyan dubu biyu da miliyan dari biyar da tamanin da biyar.

 

Ya yi nuni rashin jin dadin ganin c ewa wannan asusun jami’ar da abin ya shafa ya kunshi wasu kudade na sassan daban daban kamar tallafin bincike na gida da na waje, kudade na sassan jami’ar da ke da alaka da bincike bincike.

 

Ya bayyana cewa, a sakamakon wannan odar, dukkan ayyukan da suka shafi kashe kudi kamar su tsaftar muhalli, wutar lantarki da sauran kayayyakin masarufi na fuskantar cikas.

 

Tun da farko a nasa jawabin, shugaban jami’ar kuma shugaban majalisar gudanarwar jami’ar, Alhaji Mahmood Yayale Ahmed ya ce tsarin jami’o’in Najeriya na fuskantar kalubale da suka hada da kudade, mulki da gudanarwa.

 

Don haka ya ba da shawarar samun ‘yancin kai na kuɗi don tabbatar da cewa jami’o’i sun kasance matattarar masana da kwararri da tunani da sabbin abubuwa.

 

Shima a nasa jawabin, Uban jami’ar, Obi na Onitsha, Nnaemeka Alfred Achebe, ya dorawa daliban da suka yaye aikin yin amfani da wannan karni na 21 a matsayin shekarun juyin zamani.

 

Bikin karo na 44, an yaye dalibai 21,952 da suka kammala karatun digiri na 2023/2024, daga cikinsu 5,756 sun sami digiri na biyu yayin da 16,196 suka sami digiri na farko.

 

COV/HALIRU HAMZA/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Cutar amosanin jini wacce aka fi sani da cutar sikila na cigaba da barazana ga rayukan masu dauke da ita.

Wannan cuta na saka masu ita da ‘yan uwan su cikin halin ha’ula’i, a wasu lokutan ma tana haifar da rasa rayukan wasu dake dauke da ita.
Rahotannin Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) sun nuna cewa, kusan yara 300,000 ne ake haifa da cutar Sikila a duk shekara a fadin duniya, inda yankin Kudu da Sahara a Afirka ke dauke da kashi 75% na wannan yawan.
A Najeriya kadai, ana kiyasta cewa fiye da yara 150,000 ake haifa da cutar Sikila a kowace shekara — hakan ya sa Najeriya ke da mafi yawan masu fama da cutar Sikila a duniya.

NAJERIYA A YAU: Halin Da Shirin Samar Da Tsaro A Makarantun Najeriya Ke Ciki DAGA LARABA: Hanyoyin Da Suka Kamata A Bi Wajen Ceto Daliban Kebbi Da Aka Sace

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan cutar amosanin jini don gano yadda masu fama da ita ke ji a rayuwar su.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • ’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
  • NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza
  • NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta