Babban kwamandan sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Atisayen soji na “Manzon Allah Mai Girma na 19” ya cimma gagarumar nasara

Babban kwamandan sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Admiral Ali Reza Tangsiri ya sanar da cewa: Atisayen soji mai take “Manzon Allah Mai Girma na 19” ya cimma gagarumar nasara da burin da ake son kai wa bayan samun nasarar gwada sabbin na’urori da gudanar da ayyuka daban-daban, tare da samun nasarar gwajin kai hari kan wuraren abokan gaba.

A wata hira da ya yi da manema labarai a yau Lahadi, Admiral Tangsiri ya bayyana cewa: A rana ta biyu ta atisayen “Manzon Allah Mai Girma na 19” da aka gudanar na gwada karfin soji, wanda ke dauke da sunan shahidi Manjezi, makamai masu linzami daga kasa zuwa teku da kuma daga kasa zuwa masu cin dogon zango, matsakaici da gajere.

Ya kara da cewa: A cikin wannan atisaye a karon farko an harba makami mai linzami na Nawab da ke goyon bayan shamakin jirgin sama da jirgin ruwan shahidi Qassim Suleimani kuma sun samun nasarar cimma wurin da aka harba su.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar

An yi kira ga manoma a jihar Kwara da su yi taka tsan-tsan domin hasashen za a samu ruwan sama da kuma tsawa da ake hasashen nan da kwanaki masu zuwa.

 

A wata sanarwa da kwamishinan noma da raya karkara na jihar, Dr, Afees Abolore ya fitar, ya ce a cewar hukumar kula da yanayi ta Najeriya, NiMet, ana sa ran wasu sassa na jihar za su fuskanci ruwan sama da kuma yiwuwar tsawa.

 

Ya ce za a fuskanci ruwan sama ne da rana da yamma, tsakanin Litinin 28 ga Yuli da Laraba 30 ga Yuli, 2025.

 

Ya yi bayanin cewa duk da cewa ba a sami ruwan sama ba tukuna, yanayin da ke gaba zai iya kawo cikas ga ayyukan noma da ake ci gaba da yi, musamman ga masu sharefilaye, da watsin taki, ko girbin amfanin gona.

 

Ya yi nuni da cewa wuraren da ke da ƙarancin magudanar ruwa ko kuma waɗanda ke kusa da hanyoyin ruwa na iya zama mafi haɗari ga ambaliya.

 

Sanarwar ta shawarci manoman da su daina amfani da takin zamani domin gujewa wankewa da almubazzaranci, da kuma girbi manyan amfanin gona da wuri domin hana lalacewa daga ruwan sama.

 

Yana ƙarfafa manoma da su ɗauki hasashen da gaske kuma su hanzarta yin aiki don rage cikas da kiyaye rayuwarsu.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almujtaba 121
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almutaba (a) 120
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe
  • Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya
  • Babban Jami’in Hamas A Gaza; Makiya ‘Yan Sahayoniyya Suna Rufe Gazawar Sojojinsu Da Kisan Kare Dangi