Leadership News Hausa:
2025-10-13@13:33:06 GMT

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Published: 12th, October 2025 GMT

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Matar da ta daina ganin girman mijinta ta riga ta fara ruguza aurenta, da zarar kin yi masa maganganu na cin mutunci, kin yi kamar kin tozarta kanki da kanki ne, saboda girman mace a cikin aurenta yana da alaka da girman mijinta.

2. Rashin adalci tsakanin mijinki da danginsa

Ki sani, mijinki zai iya jure miki a kuskuren da kike masa kai tsaye, amma zai dade yana daukar zafin abin da kika aikata wa iyayensa, ‘yan uwansa ko danginsa, wannan babban kuskure ne da mata da dama suke yi su kuma yi nadama daga baya.

3. Rashin Tausayi da Kulawa

Ki sani, koda kuwa mijinki yana da kudi, yana bukatar jin tausayi daga gare ki. Idan ya dawo gida a gajiye, kuma ba kya nuna damuwarki ko kulawarki, hakan na iya sanyawa ya ji babu darajarsa a idonki. Wannan ma yana daga cikin manyan kurakuran da ake nadama a kai.

4. Yin kishi nai tauri da rashin amana

Kishin mace al’ada ne, amma idan ya wuce kima, yana canza soyayya zuwa guba. Idan baki yarda da mijinki ba, kina tuhumarsa a kan kowanne abu, to ke da kanki za ki gaji, shi ma ya gaji, sai aure ya fara tangal-tangal.

 

Za Mu Ci Gaba Mako Mai Zuwa In Allah Ya Kai Mu

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Uwargida Sarautar Mata Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro? September 12, 2025 Uwargida Sarautar Mata Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa  July 27, 2025 Uwargida Sarautar Mata Ki Bar Auna Yadda Mijinki Yake Miki Da Yadda Wani Yake Wa Matarsa July 20, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

 

A cikin nuna jajircewa da hadin kai tsakanin gwamnati jiha da ta tarayya, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, a ranar Juma’a ya gana da Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, CON, domin yin cikakken bitar aikin titin Abuja–Kaduna–Abuja

 

Taron, wanda aka gudanar a birnin Abuja, ya nuna irin salon jagorancin Gwamna Uba Sani na jajircewarsa wajen tabbatar da kammala wannan muhimmin titi wanda ke da matuƙar tasiri ga tattalin arzikin ƙasa.

 

Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan yadda za a hanzarta kammala ɓangaren Abuja–Jere da Kaduna, wanda ke da muhimmanci ga miliyoyin ‘yan Nijeriya da ke amfani da shi kullum wajen sufuri, kasuwanci da hulɗar zamantakewa.

 

Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa wannan titin ba na yankin Arewa kadai ba ne, ya bayyana shi a matsayin jijiyar ƙasa da ƙasa ne wadda ke haɗa yankuna daban-daban tare da ƙarfafa haɗin kai da bunƙasar tattalin arziki.

 

Ya kara da cewa titin Abuja- Kaduna da Kano na ɗaya daga cikin manyan ayyukan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ƙarƙashin Manufar Sabon Fata na (Renewed Hope Agenda), wadda ke nufin sabunta manyan gine-ginen ƙasa da inganta tattalin arziki.

 

Yace “Wannan titi ba hanya ce kawai ba inda yace wata hanya ce ta tattalin arziki wadda ke haɗa mutane, kasuwanni, da dama a fadin Arewacin Nijeriya da ma bayan haka,”

 

A nasa jawabin, Sanata Umahi ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa yadda yake kaiwa da komowa domin kare muradun al’ummar Kaduna, tare da tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta kuduri aniyar kammala aikin cikin lokaci. Ya bayyana cewa an umarci kamfanonin da ke aikin da su rika aiki sau biyu a rana domin hanzarta cigaba ba tare da rage inganci ba.

 

Ministan ya kara da cewa amfani da fasahar siminti mai ɗorewa wanda zai tabbatar da cewa titin zai dawwama tare da rage kudin gyara nan gaba.

 

Kamfanonin da ke aikin sun yi alkawarin ƙara gaggautawa musamman a yankin Jere dake jihar Kaduna, inda ake sa ido sosai kan ci gaban aiki. Gwamnatin Jihar Kaduna ta kuma tabbatar da ci gaba da haɗin kai da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya domin magance ƙalubalen da ke iya janyo tsaiko.

PR: Shettima Abdullahi

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
  • Sharhi: Lai Qingde Ba Zai Iya Jirkita Gaskiya Ba
  • Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata
  • An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya