Leadership News Hausa:
2025-10-13@13:33:05 GMT

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

Published: 11th, October 2025 GMT

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

A cewarta, shirin ya taimaka wajen noman shinkafa da ta kai kimanin tan 99,452, wacce kuma kudinta ya kai kimanin Naira biliyan 13.527 tare kuma da noman rogo da ya kai kimanin tan 87,237, wanda kudinsa ya kai Naira biliyan 3.925, musamman domin a kara samar da wadataccen abinci da kuma kara bunkasa fannin tattalin arzikin jihar.

 

Sai dai, ta bayyana cewa; har yanzu a jihar ba a samar da wani cikakken tsari a hukumance ba, a kan tsarin na shirin na CAF wanda hakan ke haifar wa da shirin koma baya a jihar.

 

Ta yi kira ga sauran masu ruwa da tsaki a fannin bunkasa aikin noma, domin samun riba a jihar da su bayar da hadin kai wajen shiga cikin tsarin na CAF, musamman a bangaren noman shinkafa da rogo da sauran amfanin gona.

 

Kazalika, ta bukaci mahukunta a jihar da su samar da tsari a hukumance, musamman na dogon zango domin ci gaba da samar da wadataccen abinci a fadin jihar baki-daya.

 

Shi ma a nasa bangaren, jami’in shirin na jihar; Dakta Emmanuel Igbaukum ya bayyana cewa, masu ruwa da tsaki a jihar, sun nuna sha’awarsu ta shiga cikin shirin tare kuma da sanya shi a cikin tsarin jihar na samar da abinci mai gina jiki.

 

Ya kara da cewa, shirin zai kuma taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin aikin noma na jihar baki-daya.

 

A nata jawabin, Babbar Sakatariya a ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci, Pharm. Elijah ta bayar da tabbacin cewa; gwamnatin jihar za ta bayar da kason kudi a kan lokaci tare kuma da yin rangwame wajen sayen kayan aikin noma cikin rahusa.

 

Ta bayyana cewa, gudunmawar shirin na IFAD ya taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin tattalin arziki da kuma fannin aikin noma na jihar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Noma Da Kiwo Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara October 11, 2025 Noma Da Kiwo Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina October 3, 2025 Noma Da Kiwo Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo October 3, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

Bugu da kari, an rufe shafukan hakar ma’adanai haramtacce 98 a fadin kasar.

 

“An kiyasta cewa Nijeriya na asarar kusan Dala biliyan 9 a kowace shekara sakamakon haramtacciyar hakar ma’adanai. Wannan sata ta albarkatunmu da ya kamata ta bunkasa kasarmu ta wuce kima, kuma lokaci ya yi da za a kawo karshensa,” in ji Abdulraheem.

 

A cewar sa, kwamitin na da alhakin hana asarar kudaden shiga, tabbatar da gaskiya da adalci a harkokin hakar ma’adanai, da tabbatar da cewa dukiyoyin ma’adanin kasar suna ba da cikakken gudunmawa ga ci gaban tattalin arziki.

 

“Yayin da muke ci gaba, daya daga cikin manyan manufofin wannan kwamitin shi ne hana asarar kudaden shiga da haramtacciyar hakar ma’adanai da ayyukanta ke haifarwa, wanda ba wai kawai ke satar kudaden asusun kasa ba, har ma yana hana bunkasar ayyukan hakar ma’adanai na halal wadanda za su iya ba da gudunmawa mai yawa ga cikakken kudin shiga na cikin gida na kasa (IGR).

 

“Ta hanyar tsauraran kulawa da tsare-tsare, za mu karfafa hanyoyin bibiyar kudaden shiga kuma mu tabbatar cewa duk fa’idojin da ke tattare da bangaren hakar ma’adanai na Nijeriya sun shiga asusun gwamnati kai tsaye, ba tare da a sata ta hanyar haramtacciyar hakar ma’adanai ba.

 

“Haka kuma, batun laifuka da lalacewar muhalli da ke da alaka da haramtacciyar hakar ma’adanai yana da muhimmanci. Wadannan ayyuka ba kawai suna kara rashin tsaro ba ne, har ma suna haifar da gurbatar hanyoyin ruwa, lalata dazuzzukanmu, da tilasta kwashe al’ummomi masu rauni daga gidajensu. Wannan lamari ne na gaggawa na kasa wanda ya zama dole a tunkare shi kai tsaye,” in ji shi kari.

Yana mai jaddada cewa majalisar kasa za ta yi duk mai yiwuwa ba tare da wasa ba, ya ce kwamitin yana tsaye kafada da kafada kan ikonsa na kundin tsarin mulki da ‘yan Nijeriya suka ba shi.

Yayin da yake tabbatar da shirin majalisar wajen daukar mataki mai karfi kan duk wanda aka same shi da hannu a haramtacciyar hakar ma’adanai, Shugaban Kwamitin ya yi kira ga ‘yan kasa da su bayyana masu laifi a cikin al’ummominsu don amfanin kasa baki daya.

“Mun kuduri aniyar cika wajibcinmu na sa ido kamar yadda kundin tsarin mulkin Tarayyar Nijeriya ya tanadar, wajen fallasa cin hanci da rashawa a kowace hanya, dakile miyagun ayyuka, da tabbatar da cewa albarkatunmu ana amfani da su ne domin amfanin duk ‘yan Nijeriya.

“Ta hanyar wannan tsauraran sa ido ne za mu kawar da cutar haramtacciyar hakar ma’adanai daga kasarmu, mu kare muhalli, da kuma tabbatar da jin dadin ‘yan kasa. Ta amfani da ikon da aka ba mu, za mu gudanar da bincike, tattara hujjoji, da bayar da shawarwarin da za su dawo da hankali da gaskiya a bangaren hakar ma’adanai na Nijeriya,” in ji shi kari.

Game da Kamfanin Karafa na Ajaokuta (Ajaokuta Steel Company), ya tabbatar cewa gwamnatin Tinubu ta nuna jagoranci da kuma shirin farfado da wannan dukiyar kasa.

“Tsawon shekaru da dama, Kamfanin Karafa na Ajaokuta ya kasance alamar bai cika burinsa ba. Ko ma dai yaya, ina alfahari da cewa yanzu yana kan hanyar cika ainihin burinsa. Gwamnatin yanzu ta nuna kwazo na siyasa da ba a taba gani ba wajen farfado da wannan muhimmin dukiyar kasa.”

“Wannan yana bayyana ne a cikin nadin wani kwararren dan kasa domin jagorantar farfado da kamfanin, mataki da ke ba mu fata ga makomar masana’antar karfe ta Nijeriya.

Tare da shirye-shiryen Ajaokuta na samun nasara, muna kallon hakan ba kawai a matsayin sauyin tattalin arziki ba, har ma a matsayin ginshiki ga masana’antu, samar da ayyukan yi, da dogon lokacin bunkasar tattalin arziki,” in ji shi.

Wakilin (NSCDC), Kwamandan Ma’aikatan Tsaron Hakar Ma’adanai, Attah Onoja, ya tabbatar wa kwamitin da cikakken hadin kai daga jami’ai.

Onoja ya bayyana cewa tun bayan kaddamar da aikin Mining Marshals a watan Maris 2024, NSCDC ta kama masu hakar ma’adanai haramtacce sama da 500, inda kimanin 270 daga cikinsu ke fuskantar shari’a a halin yanzu.

“Ina so in bayyana cikin gaggawa cewa sama da masu hakar ma’adanai 500 an kama su a lokacin wannan aikin. Kuma daga cikin wannan adadi, kimanin 270 suna fuskantar shari’a a yanzu kamar yadda muke magana a yau.

“Jami’an NSCDC, a matsayin hukuma, tana tabbatar wa wannan Kwamitin girmamawa da cikakken hadin kai da goyon baya a duk inda ya zama dole domin tabbatar da cewa an cimma wannan muhimmin burin tattalin arziki,” in ji shi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano October 10, 2025 Labarai Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN October 10, 2025 Labarai ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  
  • An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 
  • Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara