Trump Ya ce An Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Yakin Gaza
Published: 9th, October 2025 GMT
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa Isra’ila da Hamas sun amince da matakin farko na yarjejeniyar tabbatar da zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.
A wani sako da ya wallafa a kafarsa ta sada zumunta ya ce hakan na nufin nan ba da jimawa ba za a saki dukkanin wadanda ake garkuwa da su, sannan Isra’ila za ta janye dakarunta.
Ya ce wannan mataki ne na farko na tabbatar da zaman lafiya mai dorewa. “Za a yi wa kowane bangare adalci,” in ji Trump. Kungiyar Hamas ta tabbatar da cimma yarjejeniyar ta kawo karshen yakin Gaza bayan tattaunawa kan yarjejeniyar Donald Trump.
Hamas ta ce yarjejeniyar ta kunshi janyewar Isra’ila daga yankin da kuma musayar fursunoni da kuma mutanen da aka yi garkuwa da su.
Trump ya ce wannan babbar rana ce ga kasashen Larawaba da na Musulmi da Isra’ila da dukkanin kasashe da kuma Amurka. Sannan ya gode wa kasashen Qatar da Masar da Turkiya da ke shiga tsakani a tattaunawar tsakanin Hamas da wakilan Isra’ila da na Amurka.
Wannan na zuwa a daidai lokacin da shugaba Trump ya ce yana tunanin kai ziyara yankin Gabas Ta Tsakiya a karshen mako domin ganawa da kasar Masar a inda ake tattaunawar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka M D D Ta yi Kira Da A Kawo Karshen Yakin Gaza Da Aka Kwashe Shekaru 2 Ana Yi. October 9, 2025 Iran da Rasha Sun Tattauna Kan Yadda Za su Inganta Yin Aiki Tare A Bangaren Nukiliya. October 9, 2025 Natanyahu Ya Ce Makamai Masu Linzami Masu Keta Nahiyoyi Na Iran Barazana Ce Ga Amurka October 8, 2025 Iran Da Sauran Kasashe Na Bakin Tekun Caspian Sun Rattaba Hannu Kan Yarjeniyar Tsaron Tekun October 8, 2025 HKI Ta Kai Farmaki Kan Jiragen Ruwan ‘Sumud’ Kusa Da Gaza October 8, 2025 Iran Ta Bukaci Karin Taimako Daga MDD Don Kula Da Yan Gudun Hijiran Afganistan October 8, 2025 Burtaniya: An Ci Gaba Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa Duk Tare Da Gargadin Jami’an Tsaro October 8, 2025 Qalibaf: Iran Ba Za Ta Yi Sassauci Kan Tsibiran Kasar Guda Uku Ba October 8, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Gayyaci Jakadun Kasashen Turai Don Gargadarsu October 8, 2025 Iran Ta Bayyana Aniyarta Ta Rashin Daina Samar Da Magunguna Ta Hanyar Fasahar Makamashin Nukiliya October 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Isra ila da
এছাড়াও পড়ুন:
Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza
Adadin Falasdinawan da aka kashe a yakin kisan kare dangi na Isra’ila a Gaza na iya zama mafi girma fiye da yadda aka kiyasta a baya, in ji rahoton jaridar Die Zeit ta Jamus ta mako-mako.
A bisa ga kiyasin masu binciken, tsakanin Falasdinawa 99,997 da 125,915 ne aka kashe a Gaza a cikin shekaru biyu na farko na yakin.
Masana kimiyya a Cibiyar Max Planck sun tattara bayanai daga majiyoyi da yawa kafin su bayyana kididdigar.
Baya ga alkaluman da Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta fitar, sun hada wani bincike mai zaman kansa na gida da rahotannin mace-mace da aka buga a shafukan sada zumunta.
Duk da haka, asibitoci da yawa sun daina aiki yadda ya kamata a lokacin yakin, wanda hakan ya sa hukumomi suka yi amfani da sanarwar mutuwar da iyalai suka bayar.
Misali, wadanda suka mutu a karkashin baraguzan gine-gine galibi ba a rubuta su ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru Mafaka Ta Wucin Gagi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi November 25, 2025 Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin November 25, 2025 An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci