Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya
Published: 4th, October 2025 GMT
Me Hakan Ke Nufi Ga Tawagar Nijeriya?
Ga Yadda Tsayuwar Rukunin C Yake
A ranar 9 ga watan Satumba ne tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta tashi da kunnen doki a wasan da ta buga da tawagar ta Afirka ta Kudu a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya. Bayan wasan ne kasar Afirka ta Kudu ta kara zama a saman teburi da maki 17 cikin wasa takwas da ta buga a Rukunin C.
Tawagar Jamhuriyar Benin ke biye mata da maki 14, sai kuma Nijeriya da ke mataki na 3 da maki 11.
Sai dai kuma Nijeriya ta kasance tana da maki daya ne da na Rwanda da ke mataki na 4, sai kuma kasar Lesotho da ke da maki 6 a mataki na 5, sai kuma Zimbabwe ta karshe da maki 4.
Kasashe tara ko 10 ne za su wakilci nahiyar Afirka a gasar cin kofin duniya na 2026, wadda kasashe 48 za su fafata kuma kasashen Amurka da Medico da Canada za su karbi bakunci.
Canjin Da aka samu Bayan Hukunci
A ka’idar wasannin neman gurbin, duk tawagar da ta kare a mataki na daya daga kowane rukuni guda tara na nahiyar Afirka ce za ta samu gurbi kai-tsaye. Daga baya sai a zabo hudu mafiya kokari da suka kare a mataki na 2, inda za a fitar da daya daga cikinsu sannan ta kara da wata tawagar daga nahiyar.
Yanzu da aka rage wa Afirka ta Kudu maki uku, zai zama tana da maki 14 kenan, dai-dai da tawagar kasar Benin, ita kuma kasar Lesotho ta samu karin maki uku zuwa maki tara maimakon shida a baya kafin a kara mata maki uku.
Yanzu wasa biyu ne suka rage wa kowace tawaga, inda Nijeriya take bukatar samun nasara a wasannin guda biyu. Idan ta samu nasara a wasannin da za ta buga da Lesotho da Benin, zai zama Nijeriya da maki 17 ke nan jimilla.
Sai dai kuma hakan zai ta’allaka ne da wasannin sauran kungiyoyin, domin idan Afirka ta Kudu ko Benin daya daga ciki ta ci wasa daya, ta yi canjaras a wasa daya, za ta koma maki 18. Amma idan ta yi rashin nasara a wasa daya, ta ci daya za ta tsaya da maki 17 ne, daidai ke nan da idan Nijeriya ta samu nasara a wasanninta biyu na gaba.
Ita Benin yanzu damarta ta karu, kuma akwai wasa tsakanin Nijeriya da Benin, wasan da za a iya kira da raba gardama domin shi ne wasan Nijeriya na karshe a rukunin na C.
Ke nan Nijeriya ta fi bukatar samun nasara a wasanninta biyu na gaba, sannan Afirka ta Kudu da Benin su rasa wasanninsu biyu na gaba, inda za ta kara da maki 17, su kuma suna 14. Haka kuma idan Nijeriya da Afirka ta Kudu suka karkare da maki daya, Super Eagles na bukatar kwallaye fiye da Afirka ta Kudu haka ita ma Benin. Yanzu haka Afirka ta Kudu na da yawan kwallaye +8, yayin da Nijeriya ke da +2.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
Ministar wadda ta je kamfanin domin daukar sabuwar motarta ta alfarma kirar Nord Demir SUB da kamfanin ya hada nataimakin Shugaban jami’ar na sashen kula da ilimi da gudanar da bincike Farfesa Bola Oboh da kuma Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi ne, suka karbi bakuncinta.
A jawabin da ta gabatar a lokacin ziyarar ministar ta bayyana cewa,Duba da yarjejeniyar hada-hadar kasuwanci wajen fitar da kaya zuwa ketare kamfanin zai iya yin amfani da wannan samar waken fitar da motocinsa zuwa ketare.
Ta kara da cewa, Nijeriya na da gurare biyu ne da ake hada motoci da suka hada da, na wannan jami’ar da kuma na EPs, inda ta yi nuni da cewa, karfin da kamfanin ya ke da shi, zai iya cike gibin bukatar da ake da ita, ta ‘yan kasar na bukatar motocin.
Ya ci gaba da cewa, za mu ci gaba da kara karfafa kwarin guwair ‘yan kasar domin da kuma sauran kamfanoni masu zaman kansu domin su rinka sayen kayan da kamfanonin kasar, suka sarrafa da kuma hada su.
Ta ce, wannan babban abin alhari ne, ganin cewa, a wannan jami’ar ce, aka hada wannan mortar.
Shi kuwa a na sa jawabin Farfesa Oboh ya bayyana cewa, muna Myrna da wannan shirin na Gwamnatin Tarayya wanda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ke jagorantar bai wa ‘yan kasar kwarin guwair sayen kayan da aka sarrafa a cikin kasar
A cewarsa, jami’ar ta UNILAG, ba wai kawai na yin alfahari da samun wannan wajen hada motocin ba ne, kadai amma ta na alharin da cewa, an samar da wajen a jami’ar.
Shi ma, Shugaban kamfanin Mista Oluwatobi Ajayi, a yayin da ya ke nuna jin dadinsa kan gudunmwar da ministar ke bai wa kamfanin ya a bayyana cewa, na yi matukar farin ciki ganin cewa, ministar ta kasance daya daga cikin abokan cinikayyar mu
Kazalika, Shugaban ya kuma gode wa mahukunta jami’ar ta UNILAG kan yin hadaka da kamfanin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA