Dagacin garin Kirawa a Ƙaramar Hukumar Gwoza, a Jihar Borno, Abdulrahman Abubakar, ya bayyana dalilin da ya sa ya tsere daga Najeriya zuwa Kamaru bayan harin Boko Haram.

A farkon makon nan, mayaƙan Boko Haram sun kai hari garin Kirawa, inda suka kashe mutum biyu sannan suka ƙone fadarsa.

’Yan bindiga sun sace uwa da ’ya’yanta a Kogi Isra’ila ta kai hare-hare a Gaza duk da kiran Trump na tsagaita wuta

A hirar da aka yi da shi, Abubakar ya ce babu wani zaɓi da ya rage masa face ya tsere.

“Babu abin da ya rage sai na tsere zuwa Kamaru. Mazauna garin sun hau manyan motoci sun tsallaka iyaka, wasu kuma sun gudu zuwa Maiduguri.”

Boko Haram ta saki bidiyo da ke nuna yadda mayaƙanta suka ƙone barikin sojoji.

Rahotanni sun nuna cewa sama da mutum 5,000 ne suka tsere zuwa Kamaru saboda hare-hare a Gwoza.

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya kai ziyara yankin da aka kai harin a ranar Juma’a.

Ya tunatar da dakarun Najeriya muhimmancin kare garuruwan da ke kan iyaka irin su Kirawa, Baga, Damasak da Malamfatori.

Zulum, ya ce sojojin Kamaru sun taimaka wajen dawo da jama’a garuruwansu shekarun da suka gabata, amma janyewarsu ya haifar da ƙalubalen tsaro.

“Abin takaici, gargaɗin da na yi bai samu karɓuwa ba. ’Yan ta’adda sun sake kai hari a ranar Laraba, sun kashe mutum biyu, sun kuma ƙone gidaje 50, motocinmu guda takwas da manyan injina. Mun gode wa Allah cewa ba a rasa rayuka masu yawa ba,” in ji gwamnan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Bsarake

এছাড়াও পড়ুন:

Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa Maryam Sanda afuwa, wadda aka yanke wa hukuncin kisa a shekarar 2020 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello, ɗan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Alhaji Haliru Bello.

Maryam,’ mai shekara 37, ta shafe shekaru shida da watanni takwas a gidan yarin Suleja kafin yi mata afuwa.

Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro

Rahotanni sun nuna cewar an yi mata afuwar ne bayan yin nadama da aikata kyakkyawan halaye.

Iyayen Maryam sun roƙi gwamnati da ta sake ta saboda ’ya’yanta biyu da ta ke da alhakin kula da su, tare da alƙawarin sauya halayenta.

Shugaba Tinubu, ya kuma yi wa wasu mutane afuwa da suka haɗa da Manjo Janar Mamman Vatsa, Ken Saro-Wiwa, da kuma Sir Herbert Macaulay.

Gaba ɗaya mutane 175 ne shugaban ya yi musu afuwa, ciki har da masu manyan laifuka, tsoffin fursunoni, da waɗanda suka yi kyakkyawan tuba.

Wannan shi ne karon farko da Shugaba Tinubu ya yi amfani da ikon yafe laifi don tausaya wa waɗanda suka aikata laifuka tun bayan hawansa mulki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno